Sashe 5
Nawaff Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read
WAI WACECE YASMEEN????.
FATIMA shine cikakken sunanata, malam Yakubu shine mahaifinta, su 'yan asalin kasar Nijar ne, awani gari kwangwalan, kwangwalan yana nan kusada jihar katsina, dan za'a iya cewa a boda suke.
Kharima itace mahaifiyarsu wato umma, malam yakubu makiyayi ne a garin kwangwalan mutumne mai tsananin hak'uri, 'yan uwansa basa sonsa, kasancewarsu 'yan ubane, shi kad'ai mahaifiyarsa ta hafa a gidansu.
Yaransa biyu Fatima sunan mamansa aka saka mata, shiyyasa suke kiranta da yasmeen, saikuma ABUBAKAR shima dai sunan baban umma ne, shiyyasa suke kiransa da yaseer.
Yasmeen da yaseer k'yawawane, dan sunada kala irinta asalin buzaye.
Yasmeen tun tana yarinya takeda farin jini, kowa sonta yake, dan haka dangin babanta suka tsaneta laifin babanta ya shafeta.
Lokacin da yasmeen takai shekara 12 sai dangi suka matsa akan ayi mata aure, zuwa sannan yasmeen tanada wanda takeso wani sule, tana sonsa sosai shima haka, dan haka lokacin da'akace za'ayimata aure saitayi murna.
Amma saidai kash, dangin mahaifinta sunce sun za'ba mata miji, d'an wan babanta wato Tanimu, yasmeen sam bata son Tanimu dan d'an iskane kowa yasani kuma, amma babu yanda zatayi.
Aka saka biki wata hud'u, amma amarya bata so, dahaka biki yarage saura sati d'aya.
Ana saura kwana hud'u d'aurin aure Tanimu yazo gun yasmeen, abin yabata mamaki dan bai ta'ba zuwa wajentaba tunda aka saka musu rana.
Da'kyar umma ta lalla'bata ta fita, ko sallama bata yimasaba bare gaisuwa, yasaki baki yana zuba mata surutan banza, wai idan sunyi aure randa aka kaita zaiyi kaza zaiyi kaza.
Yasmeen taji yana d'akko mata zancen daya fi karfin tunaninta, dan haka takama hanyar gida zata tafi, da sauri Tanimu ya dam'ko yasmeen, ya matse abango.
Yasmeen tafara ihu dan ganin abubuwan daya ke mata, kafin mutane su kawo mata d'auki ya turmushe ta ak'asa, lokacin da mutane suka zo yana saman yasmeen amma baiyi mata komai ba, sai rigarta daya yaga, nanfa mutane suka shiga jibgarsa dan dama haushinsa akeji.
Kafin safiya labari ya baje garin kwangwalan wai Tanimu yayima yasmeen fad'e a daren jiya.
Duk gari ya d'auka cewa an lalata yasmeen, dan hakama fita ta gagareta, dan babu wanda zai yarda da ba haka bane, aranar kuma dangin mahaifinta sukace sun warware maganar auren, wai yasmeen 'yar iskace tana neman maza.
Abu kullum k'ara gaba yake, harta kai umma da baba basuda ikon fita sai ayita zind'ensu, harda yaseer dabai san komai ba, idan yafita sai ayita tsan gwamarsa, itako yasmeen ma aibatada ikon fita ko k'ofar gida.
Ahaka aka kulla wata 7 amma komai bai canja ba, kuma babu mai zuwa wajen yasmeen, sule ma iyayensa sun hanashi.
Bak'in ciki da damuwa suka ishi baba, dama akwai wani Alhaji dayake zuwa sayen dabbobi a wajensa, shi d'an Najeria ne a jihar kano.
Baba baiyi k'asa aguywa ba wajan sanarma Alhaji halin dasuke ciki,, Alhaji buba ya tausaya musu sosai, dan haka ya ce, "su baba su shirya yatafi dasu Najeria.
Babu musu suka yarda, batareda kowa yasaniba suka baro kwangwalan, koda Alhaji buba yakawo su gidansa sai hajiya jummai ta nuna musu tsangwama, ta ce, "saidai baba yarink'a musu gadi dama mai gadinsu yagudu saboda wahala.
Baba bai musaba yakar'bi tayinta, baba yana gadi umma tana taya hajiyar wasu 'yan ayyukan gida.
Alhaji buba yanada wani yaro mara jin magana, sunansa Fasal, shikad'ai ya haifa dan haka ake nuna masa gata na tsiya, tunda faisal ya 'kayalla idanu yaga Yasmeen ya kafa mata k'ahon zuk'a.
Yasmeen bata manta da abinda yafaruba a garinsu dan haka take baya2 da faisal, duk abinda yake faruwa hajiya jummai tana kula, tasan kuma halin d'anta yanzu saiya 'bata yarinyar mutane, dan haka ta tsawatar masa.
Alhaji buba yasaka su yasmeen makaranta , ahankali k'yawun yasmeen yafara fitowa, zawa sannan faisal yakai 'kololuwar sha'awar yasmeen, awata ranar lahadine, yad'auki hanyar cimma burinsa, yasaka yasmeen ta gyara masa d'aki, daga haka ya rutseta a d'aki, ihu takwala wanda yasa hajiya jummai isowa da gudu d'akin faisal, saita tarar yana shirin aikata ta'asa, ta daka masa tsawa sanna ta 'ban'bare yasmeen dak'yar.
Babu wani mataki da 'aka d'auka, dan ko fad'a basuyima faisal ba, dan haka hankalin umma da baba yatashi, suka fara tsanar zaman gidan, dan indai aka cigaba da tafiya haka wataran faisal saiya lalata musu yarinya.
Da alhaji buba yaga hankalinsu yatashi saiya ce, "yana nemawa faisal auren yasmeen idan yadawo daga karatu america za'ayi biki, inko har basu aminceba to zasu barmasa gida, indan suka amince to zai siya musu gidan dazasu zauna ya nemawa baba aikinyi yabar gadi, zaikuma d'auki nauyin karatun yasmeen da faisal harzuwa inda suke buk'ata.
Da farko basu aminceba dan sunsan faisal bashida tarbiya, amma dasukaga babu sarki sai ALLAH saisuka amince.
Aka saka rana da komai, faisal yatafi america karo karatu, badan yasoba, dan yaso saiya mallaki yasmeen kafin yatafi, bawani so yake mataba sha'awarta kawai yakeyi, daya sami biyan buk'ata zai watsar da banxa😔.
Bayan komai ya kankama alhaji buba yacika al'kawarin duk daya d'auka yasiyama baba gida madaidaici, yakuma d'auki nauyin karatun su yasmeen, yanzu haka yasmeen tana karatu a (FCE KANO ) yaseer yana shekararsa ta k'arshe a secondary, idan yasmeen zata makaranta ko anguwa kaita akeyi, dan an d'akko mata direba na musamman wato balarabe, duk motar dayaso yake d'aukowa a gidan su faisal yakai yasmeen makaran ta daduk inda take buk'ata.
Sutura kuwa mai tsadar gsk su alhaji suke sayama yasmeen, haka kayan kwalliya, hajiya jummai tana k'ok'ari wajen sayama yasmeen, waya mai tsada yasmeen take ri'kewa, wata sa'in agidan take weekend, sunayin waya da faisal, saidai hirar tasa duk takan kasance batsa, abun yana damun yasmeen amma babu yanda zatayi.
Yanzu haka saura wata 5 faisal ya kammala karatunsa, yana dawowa kuma za'asha biki, saidai yasmeen da iyayenta duk basa son wannan aure, kullum addu'arsu ALLAH yakawo sanadin da auren zai rushe, wannan shine tarihin yasmeen....................✍🏻
©2016
💞Bilyn Abdul💞
💞Mrs Abdus'salam💞
💞LUV U OLL MY FAN's💞
[1/12, 8:53 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF🎾
☆☆☆☆☆☆☆
NA BILKISA IBRAHIM💞
Page👉🏻10
......Yau takama d'aurin aure amma yasmeen batada niyyar zuwa, umma tayi mata maga ta ce, "bazata jeba sai anjima.
Shima dai Nawaff ya halarci taron d'aurin auren daganan yakama gabansa, dan shi mutumne dabaya son yawan hayaniya, gashi da mutane sun ganshi bazasu bari ya huta ba.
3:30pm
Yasmeen kwance a falo tana kallon film, umma tafito daga d'akin abba, ta zauna kusada yasmeen.
Yasmeen ta d'ago tana kallonta, umma ta ce, "mamana yau bazaki wajen bikin asma'u d'in ba??, yasmeen ta ce, "gsky umma bazan jeba bana jin dad'i, amma idan naga zuwa anjima naji sauk'i sai naje.
To shikenan ALLAH ya sauwak'e.
Amin yasmeen tafad'a tana kallon tv, lfyr yasmeen k'alau, batason zuwa wajenne su had'u da Nawaff, tana tsoron karya aikata mugun nufinsa akanta, jadabaya ga rago 🐏kuwa aiba tsoron fad'a bane, inji masu iya magana.
Badan ALLAH Nawaff yay shirin zuwa wajen walimar ba, yajene kawai domin yasmeen, amma saidai kash ita batajeba, tunda yaje yake baza idanu, amma komai kama da ita bai ganiba.
Duk abinda yake mus'ad yana kallonsa, dukda yasan Nawaff bazai aikata abinda yafad'a akan yasmeen ba, amma yayi matuk'ar farin ciki da bata zo wajenba.
Bayan antashi daga walimar su Nawaff sukai saurin guduwa, saboda mutane, amota mas'ud ya ce, "bro's waimi kake nema d'azu kaketa lek'e2.
Nawaff yad'an ja hancinsa tareda kwantawa sosai ajikin kujera yana kallon titi, daga bisani yadawo da kallonsa wajen mas'ud dake tuk'i, ya ce, mara kunyar yarinyar nan nake nema, amma ban gantaba, inaga tsoro yahanata zuwa.
Mas'ud yay murmushi, hankalinsa na bisa titi, ya ce, "aii masu iya magana suna cewa hanyar lafiya abita da shekara, nikaina naji dad'i dabata zoba.
Nawaff ya harari mas'ud, kai malam mikake nufine?? wai ko dai son k'abar nan kakeyi??.
Mas'ud yay dariya yana fad'in A'a alhaji maida wuk'ar niba sonta nakeyiba, kada kishi yasa ka b'arar dani.
Banza Nawaff yay masa, dan yasan halin Mas'ud sarai yanzu saiyayita jan wannan maganar har momcy taji.
Dahaka suka k'arasa gida, kai tsaye b'an garen momcy suka nufa, afalo suka iskesu itada papa da Abdallah.
Nawaff yazauna kusada k'afar papa yana kwasar gaisuwa, shima mas'ud ya gaisheshi, suka gaida momcy, Abdallah ya gaishesu.
Papa ya ce, " 'yan samari daga ina haka??.
Nawaff yad'an sosa sumarsa ya ce, "papa daga wajen bikin Safwan muke.
Papa ya ce, "masha ALLAH, ALLAH yasanya alkairi, kuma aii yakamata kufito da matan auren ko??, da sauri Nawaff yad'ago yana fad'in papa aurefa kace??.
Papa ya ce, "o, ashe kajini modeebbo!!.
Nawaff ya ce, "papa 27year's fa.
Momcy ta ce, "toshi wannan dakukaje bikin ba abokinku bane, amma gashi yayi, kudai nakula daga kai har Mas'ud bakwa sonyin aure, ko sokuke saikun tsufa??.
Barsu ummul'khairi, aimun yanke magana da Alhaji, nanda k'arshen shekara idan har basu kawo matan aureba, tomu zamu nema musu.
Nawaff ya ce, "papa saikace mata.
Papa yakama kunnensa, yana fad'in toku zauna kukagani, sadaka zamu badaku.
Abdallah ya tunysure da dariya.
Nawaff ya harareshi yana mazurai, kai wa kakema dariya??, mas'ud ya ce, "bro's barshi zaizo ya samemune.
Momcy tayi dariya A'a karku huce akan d'ana, tunda bashi ya ce, "ayi sadaka dakuba.
Papa ya ce, "barshi ai shima hardashi.
Abdallah ya zaro idanu, papa nikuma asuwa wai kare da gudun layya, 'yan 27year's basuyiba, bare ni d'an 20years papa kwanan fa nashiga jami'a.
Nawaff ya daka masa tsawa, kai dallah kaima mutane shiru, kabi ka ishi mutane da shegen surutu.
Abdallah ya zunb'uro baki gaba yana gunguni, amma Nawaff bayajinsa, Dan yasan idan yajisa, hummm.
Saida sukaci abinci sanan suka tafi b'an garen Nawaff.
Mas'ud ya ce, "kai malam kahuta wlhy karigaya ka kama matarka ahannu, babu rabon ayi sadaka dakai.
Nawaff ya ce, "agidan ubanwa nasamu matar, ALLAH mas'ud kaifa d'an iskane.
Mas'ud ya tun tsure da dariya, kazauna kallon ruwa wlhy kwad'o yamaka k'afa, kanaji kana gani za'ayi sadaka dakai.
Nawaff yaja tsaki tareda kwanciya saman kujera, ya lumshe idanu.
Duk surutun da mas'ud yakeyi yana jinsa amma yay kunnen uwar shegu dashi................✍🏻
💞Bilyn Abdul💞
💞Mrs Abdus'salam💞
💞LUV U OLL MY FAN's 💞
[1/12, 8:54 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF🎾
☆☆☆☆☆☆☆
NA BILKISA IBRAHIM💞
Page👉🏻11
FATIMA shine cikakken sunanata, malam Yakubu shine mahaifinta, su 'yan asalin kasar Nijar ne, awani gari kwangwalan, kwangwalan yana nan kusada jihar katsina, dan za'a iya cewa a boda suke.
Kharima itace mahaifiyarsu wato umma, malam yakubu makiyayi ne a garin kwangwalan mutumne mai tsananin hak'uri, 'yan uwansa basa sonsa, kasancewarsu 'yan ubane, shi kad'ai mahaifiyarsa ta hafa a gidansu.
Yaransa biyu Fatima sunan mamansa aka saka mata, shiyyasa suke kiranta da yasmeen, saikuma ABUBAKAR shima dai sunan baban umma ne, shiyyasa suke kiransa da yaseer.
Yasmeen da yaseer k'yawawane, dan sunada kala irinta asalin buzaye.
Yasmeen tun tana yarinya takeda farin jini, kowa sonta yake, dan haka dangin babanta suka tsaneta laifin babanta ya shafeta.
Lokacin da yasmeen takai shekara 12 sai dangi suka matsa akan ayi mata aure, zuwa sannan yasmeen tanada wanda takeso wani sule, tana sonsa sosai shima haka, dan haka lokacin da'akace za'ayimata aure saitayi murna.
Amma saidai kash, dangin mahaifinta sunce sun za'ba mata miji, d'an wan babanta wato Tanimu, yasmeen sam bata son Tanimu dan d'an iskane kowa yasani kuma, amma babu yanda zatayi.
Aka saka biki wata hud'u, amma amarya bata so, dahaka biki yarage saura sati d'aya.
Ana saura kwana hud'u d'aurin aure Tanimu yazo gun yasmeen, abin yabata mamaki dan bai ta'ba zuwa wajentaba tunda aka saka musu rana.
Da'kyar umma ta lalla'bata ta fita, ko sallama bata yimasaba bare gaisuwa, yasaki baki yana zuba mata surutan banza, wai idan sunyi aure randa aka kaita zaiyi kaza zaiyi kaza.
Yasmeen taji yana d'akko mata zancen daya fi karfin tunaninta, dan haka takama hanyar gida zata tafi, da sauri Tanimu ya dam'ko yasmeen, ya matse abango.
Yasmeen tafara ihu dan ganin abubuwan daya ke mata, kafin mutane su kawo mata d'auki ya turmushe ta ak'asa, lokacin da mutane suka zo yana saman yasmeen amma baiyi mata komai ba, sai rigarta daya yaga, nanfa mutane suka shiga jibgarsa dan dama haushinsa akeji.
Kafin safiya labari ya baje garin kwangwalan wai Tanimu yayima yasmeen fad'e a daren jiya.
Duk gari ya d'auka cewa an lalata yasmeen, dan hakama fita ta gagareta, dan babu wanda zai yarda da ba haka bane, aranar kuma dangin mahaifinta sukace sun warware maganar auren, wai yasmeen 'yar iskace tana neman maza.
Abu kullum k'ara gaba yake, harta kai umma da baba basuda ikon fita sai ayita zind'ensu, harda yaseer dabai san komai ba, idan yafita sai ayita tsan gwamarsa, itako yasmeen ma aibatada ikon fita ko k'ofar gida.
Ahaka aka kulla wata 7 amma komai bai canja ba, kuma babu mai zuwa wajen yasmeen, sule ma iyayensa sun hanashi.
Bak'in ciki da damuwa suka ishi baba, dama akwai wani Alhaji dayake zuwa sayen dabbobi a wajensa, shi d'an Najeria ne a jihar kano.
Baba baiyi k'asa aguywa ba wajan sanarma Alhaji halin dasuke ciki,, Alhaji buba ya tausaya musu sosai, dan haka ya ce, "su baba su shirya yatafi dasu Najeria.
Babu musu suka yarda, batareda kowa yasaniba suka baro kwangwalan, koda Alhaji buba yakawo su gidansa sai hajiya jummai ta nuna musu tsangwama, ta ce, "saidai baba yarink'a musu gadi dama mai gadinsu yagudu saboda wahala.
Baba bai musaba yakar'bi tayinta, baba yana gadi umma tana taya hajiyar wasu 'yan ayyukan gida.
Alhaji buba yanada wani yaro mara jin magana, sunansa Fasal, shikad'ai ya haifa dan haka ake nuna masa gata na tsiya, tunda faisal ya 'kayalla idanu yaga Yasmeen ya kafa mata k'ahon zuk'a.
Yasmeen bata manta da abinda yafaruba a garinsu dan haka take baya2 da faisal, duk abinda yake faruwa hajiya jummai tana kula, tasan kuma halin d'anta yanzu saiya 'bata yarinyar mutane, dan haka ta tsawatar masa.
Alhaji buba yasaka su yasmeen makaranta , ahankali k'yawun yasmeen yafara fitowa, zawa sannan faisal yakai 'kololuwar sha'awar yasmeen, awata ranar lahadine, yad'auki hanyar cimma burinsa, yasaka yasmeen ta gyara masa d'aki, daga haka ya rutseta a d'aki, ihu takwala wanda yasa hajiya jummai isowa da gudu d'akin faisal, saita tarar yana shirin aikata ta'asa, ta daka masa tsawa sanna ta 'ban'bare yasmeen dak'yar.
Babu wani mataki da 'aka d'auka, dan ko fad'a basuyima faisal ba, dan haka hankalin umma da baba yatashi, suka fara tsanar zaman gidan, dan indai aka cigaba da tafiya haka wataran faisal saiya lalata musu yarinya.
Da alhaji buba yaga hankalinsu yatashi saiya ce, "yana nemawa faisal auren yasmeen idan yadawo daga karatu america za'ayi biki, inko har basu aminceba to zasu barmasa gida, indan suka amince to zai siya musu gidan dazasu zauna ya nemawa baba aikinyi yabar gadi, zaikuma d'auki nauyin karatun yasmeen da faisal harzuwa inda suke buk'ata.
Da farko basu aminceba dan sunsan faisal bashida tarbiya, amma dasukaga babu sarki sai ALLAH saisuka amince.
Aka saka rana da komai, faisal yatafi america karo karatu, badan yasoba, dan yaso saiya mallaki yasmeen kafin yatafi, bawani so yake mataba sha'awarta kawai yakeyi, daya sami biyan buk'ata zai watsar da banxa😔.
Bayan komai ya kankama alhaji buba yacika al'kawarin duk daya d'auka yasiyama baba gida madaidaici, yakuma d'auki nauyin karatun su yasmeen, yanzu haka yasmeen tana karatu a (FCE KANO ) yaseer yana shekararsa ta k'arshe a secondary, idan yasmeen zata makaranta ko anguwa kaita akeyi, dan an d'akko mata direba na musamman wato balarabe, duk motar dayaso yake d'aukowa a gidan su faisal yakai yasmeen makaran ta daduk inda take buk'ata.
Sutura kuwa mai tsadar gsk su alhaji suke sayama yasmeen, haka kayan kwalliya, hajiya jummai tana k'ok'ari wajen sayama yasmeen, waya mai tsada yasmeen take ri'kewa, wata sa'in agidan take weekend, sunayin waya da faisal, saidai hirar tasa duk takan kasance batsa, abun yana damun yasmeen amma babu yanda zatayi.
Yanzu haka saura wata 5 faisal ya kammala karatunsa, yana dawowa kuma za'asha biki, saidai yasmeen da iyayenta duk basa son wannan aure, kullum addu'arsu ALLAH yakawo sanadin da auren zai rushe, wannan shine tarihin yasmeen....................✍🏻
©2016
💞Bilyn Abdul💞
💞Mrs Abdus'salam💞
💞LUV U OLL MY FAN's💞
[1/12, 8:53 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF🎾
☆☆☆☆☆☆☆
NA BILKISA IBRAHIM💞
Page👉🏻10
......Yau takama d'aurin aure amma yasmeen batada niyyar zuwa, umma tayi mata maga ta ce, "bazata jeba sai anjima.
Shima dai Nawaff ya halarci taron d'aurin auren daganan yakama gabansa, dan shi mutumne dabaya son yawan hayaniya, gashi da mutane sun ganshi bazasu bari ya huta ba.
3:30pm
Yasmeen kwance a falo tana kallon film, umma tafito daga d'akin abba, ta zauna kusada yasmeen.
Yasmeen ta d'ago tana kallonta, umma ta ce, "mamana yau bazaki wajen bikin asma'u d'in ba??, yasmeen ta ce, "gsky umma bazan jeba bana jin dad'i, amma idan naga zuwa anjima naji sauk'i sai naje.
To shikenan ALLAH ya sauwak'e.
Amin yasmeen tafad'a tana kallon tv, lfyr yasmeen k'alau, batason zuwa wajenne su had'u da Nawaff, tana tsoron karya aikata mugun nufinsa akanta, jadabaya ga rago 🐏kuwa aiba tsoron fad'a bane, inji masu iya magana.
Badan ALLAH Nawaff yay shirin zuwa wajen walimar ba, yajene kawai domin yasmeen, amma saidai kash ita batajeba, tunda yaje yake baza idanu, amma komai kama da ita bai ganiba.
Duk abinda yake mus'ad yana kallonsa, dukda yasan Nawaff bazai aikata abinda yafad'a akan yasmeen ba, amma yayi matuk'ar farin ciki da bata zo wajenba.
Bayan antashi daga walimar su Nawaff sukai saurin guduwa, saboda mutane, amota mas'ud ya ce, "bro's waimi kake nema d'azu kaketa lek'e2.
Nawaff yad'an ja hancinsa tareda kwantawa sosai ajikin kujera yana kallon titi, daga bisani yadawo da kallonsa wajen mas'ud dake tuk'i, ya ce, mara kunyar yarinyar nan nake nema, amma ban gantaba, inaga tsoro yahanata zuwa.
Mas'ud yay murmushi, hankalinsa na bisa titi, ya ce, "aii masu iya magana suna cewa hanyar lafiya abita da shekara, nikaina naji dad'i dabata zoba.
Nawaff ya harari mas'ud, kai malam mikake nufine?? wai ko dai son k'abar nan kakeyi??.
Mas'ud yay dariya yana fad'in A'a alhaji maida wuk'ar niba sonta nakeyiba, kada kishi yasa ka b'arar dani.
Banza Nawaff yay masa, dan yasan halin Mas'ud sarai yanzu saiyayita jan wannan maganar har momcy taji.
Dahaka suka k'arasa gida, kai tsaye b'an garen momcy suka nufa, afalo suka iskesu itada papa da Abdallah.
Nawaff yazauna kusada k'afar papa yana kwasar gaisuwa, shima mas'ud ya gaisheshi, suka gaida momcy, Abdallah ya gaishesu.
Papa ya ce, " 'yan samari daga ina haka??.
Nawaff yad'an sosa sumarsa ya ce, "papa daga wajen bikin Safwan muke.
Papa ya ce, "masha ALLAH, ALLAH yasanya alkairi, kuma aii yakamata kufito da matan auren ko??, da sauri Nawaff yad'ago yana fad'in papa aurefa kace??.
Papa ya ce, "o, ashe kajini modeebbo!!.
Nawaff ya ce, "papa 27year's fa.
Momcy ta ce, "toshi wannan dakukaje bikin ba abokinku bane, amma gashi yayi, kudai nakula daga kai har Mas'ud bakwa sonyin aure, ko sokuke saikun tsufa??.
Barsu ummul'khairi, aimun yanke magana da Alhaji, nanda k'arshen shekara idan har basu kawo matan aureba, tomu zamu nema musu.
Nawaff ya ce, "papa saikace mata.
Papa yakama kunnensa, yana fad'in toku zauna kukagani, sadaka zamu badaku.
Abdallah ya tunysure da dariya.
Nawaff ya harareshi yana mazurai, kai wa kakema dariya??, mas'ud ya ce, "bro's barshi zaizo ya samemune.
Momcy tayi dariya A'a karku huce akan d'ana, tunda bashi ya ce, "ayi sadaka dakuba.
Papa ya ce, "barshi ai shima hardashi.
Abdallah ya zaro idanu, papa nikuma asuwa wai kare da gudun layya, 'yan 27year's basuyiba, bare ni d'an 20years papa kwanan fa nashiga jami'a.
Nawaff ya daka masa tsawa, kai dallah kaima mutane shiru, kabi ka ishi mutane da shegen surutu.
Abdallah ya zunb'uro baki gaba yana gunguni, amma Nawaff bayajinsa, Dan yasan idan yajisa, hummm.
Saida sukaci abinci sanan suka tafi b'an garen Nawaff.
Mas'ud ya ce, "kai malam kahuta wlhy karigaya ka kama matarka ahannu, babu rabon ayi sadaka dakai.
Nawaff ya ce, "agidan ubanwa nasamu matar, ALLAH mas'ud kaifa d'an iskane.
Mas'ud ya tun tsure da dariya, kazauna kallon ruwa wlhy kwad'o yamaka k'afa, kanaji kana gani za'ayi sadaka dakai.
Nawaff yaja tsaki tareda kwanciya saman kujera, ya lumshe idanu.
Duk surutun da mas'ud yakeyi yana jinsa amma yay kunnen uwar shegu dashi................✍🏻
💞Bilyn Abdul💞
💞Mrs Abdus'salam💞
💞LUV U OLL MY FAN's 💞
[1/12, 8:54 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF🎾
☆☆☆☆☆☆☆
NA BILKISA IBRAHIM💞
Page👉🏻11