Sashe 54
Mijin Marigayiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kafin tace wani abu ya shige bandaki. Ta zubura baki ta ja tsaki don ba haka ta so ba, so take ayi masifa ta sami damara da za a ce Habib ya bar gidan. In ya so sai ta san yanda zata yi da Afaf, tana gamawa da wadannan biyun ta san gidan ya zama nata, musamman da yake Shukra ita matsoraciya ce duk yanda ma aka juya ta haka takeyi.
Jimawa kadan ya fito ya sake kaya sannan ya wuce ya zauna a dining table ya fara cin abinci. Yana cikin cin abincin ya dauki waya ya kirawo Habib, ba tare da bata lokaci ba ya hawo ya same shi.
‘Abba gani.’ Ya fada yana tsaye daga gefe.
Ya ajiye cokalin da yake hannunsa sannan yace ‘Habib me yasa Antinka ta saka ka wanki ka ki yi?’
Yace ‘Abba ba kin yi nayi ba, wankin ne da yawa kuma nace gobe zan samo musu yaro ya wanke a biya shi.’
‘Kala dayan ne da yawa? Kayan ma da ba nawa bane.’ Ta fada tana wasu muzurai.
Yace ‘Ni dai kayan da aka bani zasu kai kamar kala biyar ko fiye, ban sani ba ko ba su aka nuna miki ba.’
Abbansu yace ‘Ka ga Malam, bana son wani karin bayani. An ce kaya kala daya ne kuma gobe ake so ayi amfani da su. Kace a baka kayan ka wanke yanzu in ba so kake ranka ya baci ba, kuma daga yau bana son a saka ka aiki ka dinga kin yi. Ba zan dauki taurin kai da rashin kunya ba.’
Ya bude baki zai yi magana sai kuma ya fasa, ya juya ya fice.
Ya dubi Najan yace ‘Kije kice mata ta bashi kayan ya wanke.’
Ta tashi ta fice.
Yana zaune a tsakar gida wajen Baba maigadi Shukra taje ta kirawoshi. Yana shigowa ya ci karo da wankin a zube a bakin kofa; tabbas wankin sun fi kala biyar. Yana shiga cikin parlor din kafin yayi magana Naja da take tsaye tace ‘Gasu nan kaje ka wanke, kuma wallahi idan basu fita ba sakewa zaka yi har sai sun fita.’
Ta juya ta haye sama ta barsu a nan shi da kannensa.
Ya juya ya dawo ya tsaya a kan wankin yana kare musu kallo yana tunani; tabbas ba zai yi wankin nan ba, ko da kuwa kala dayan ta bayar kamar yanda tace. Kuma yanda yaga a gaban Abban tace kala daya ne kuma ta dauko kaya da yawa haka ta bashi ya san ta shirya wata makarkashiyar.
PAGE 226
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya san ba lallai Abbanshi ya saurareshi ba saboda tana gabansa tana tsara masa zance, kuma ya san idan har yayi wannan wankin to ta sami damar da zata mayar da shi dan aikin gida kuma ba zai yi ba. Haka ya kewaye ya fice ya bar wankin a nan inda ta ajiye su.
………
Suna sama ita da maigidan suna ta hirarsu cikin kwanciyar hankali, sai waje karfe tara sannan Anti Wiyya ta fito daga dakin baki ta ga wankin. Tayi matukar mamaki musamman da ta tambayi Afaf ta tabbatar mata Habib din ya fice bai dauki wankin ba. Nan ta koma daki ta kirawo Naja a waya wadda ta sauko, ta nuna mata wankin sannan tayi mata bayanin cewa a nan ya fice ya barsu.
Yaran suna kallo ta tsuguna ta tsince kayan ta bar kala daya da hijab guda daya sannan Anti Wiyyan ta koma daki ita kuma ta haye sama.
Jimawa kadan Mustapha ya sako yana tambayar Afaf ina kaninta.
‘Abba ban ganshi ba, ficewa kawai yayi ba tare da yace komai ba.’ Ta bashi amsa.
A fusace ya murda kofar dakin Habib din ya shiga yana kiransa, sai dai ga mamakinsa Habib din baya cikin dakin. Ya fice wajen Baba Maigadi inda ya tabbatar masa bai san inda Habib yake ba, ya kara da cewa ‘Bana jin ma fita yayi, don tun da aka ce ya zo kana kiransa ban sake ganin gilmawarsa ba. Sai dai ko da ina sallah ne ya fice ban sani ba.’
Ya koma cikin gidan ba tare da yace komai ba.
Yana shiga parlor din ya dubi kayan yace ‘Nasreen zo ki kwashi kayan nan ki mayar mata, yayan naki zai zo ya same ni.’
Ya haye saman inda ya tara da Naja a zaune a parlor ita da Rukayya, ya sami waje ya zauna sannan ya dauki wayarsa ya dannawa Habib kira. Ba karamin mamaki yayi ba da yaji wayar Habib din a kashe, sai dai yayi tunanin kashe wayar Habib din yayi don ya san bashi da gaskiya. Don haka sai kawai ya sauko ya sanar da Baba Maigadi cewa idan Habib ya shigo gidan yayi masa waya.
……..
Tun yana sa ran shigowar Habib har abun ya fara bashi tsoro; yaran duk sun tafi sun kwanta har sha biyun dare ta yi amma Habib bai shigo gidan ba, gashi sai kiran wayarsa ake yi a kashe. Yana son ya kirawo Hajia ko Habib din yaje can amma kuma baya son ya daga musu hankali.
PAGE 227
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid
A karo na babu iyaka motsin shigarsa dakin ne ya farakar da ita daga bacci, ta gyarawa Baby Maryam kwanciyarta sannan ta dubeshi tace ‘Wai bai dawo ba.’
A jigace yace ‘Eh, wallahi har abun ya fara bani tsoro. To ina Habib zai tafi? Ina ma ya sani a garin nan shi da ba wani yawo yake ba?’
Tace ‘Ya zaka ce ina ya sani yaron da yake level 1, kuma yake tafiya makaranta da kansa. Ai yanzu ba kamar da bane, tsaf ya san ko ina.’
‘To ina zai tafi a wannan daren? Gashi Baba Maigadi ma yace ko fitarsa bai gani ba kuma gidan nan babu inda bamu duba ba baya nan.’
Tace ‘To ka dai yi hakur ka zo ka kwanta tunda ka ga yanzu dayan dare ta kusa, zuwa wayewar gari sai a nemoshi a bashi hakuri a gaya masa ya barwankin.’
‘Mtseww! Wai kin san me kike fada kuwa? Na zo na kwanta saboda ke kin kwanta ko?’ ya sake jan tsaki sannan ya fice daga dakin ya rufe mata kofar da karfi, rufe kofar da sai da ya farkar mata da Baby daga barci.
Ta juya a fusace tana gunguni ta dauki yarinyarta ta saka mata nono.
Yanda yaga rana haka yaga dare, yana zaune a parlor shi kadai. Sai dai idan bacci ya daukeshi yayi firgigit ya farka, ya sake buga lambar Habib amma a kashe. Yana fara jin kiran sallar asuba ya kirawo Alhaji ya sanar da shi ba a ga Habib ba.
A shirye ya fice masallaci, bayan an idar da sallar asuba ya sanar da su bacewar habib. Yana dawowa gidan ya dauki mukullin motarsa ya fice ya nufi gidan Hajia.
Suma a tsaye ya samesu cikin tashin hankali, nan suka zauna suna jira gari ya kara wayewa suje police station su sanar.
Suna zaune a parlor din Alhaji cikin tashin hankali Hajia ta dubi Mustapha tace ‘Kuma ka tuntubi kakanninsa, can gidan su Ma’u da ma ita Khadeejan ko wajensu ya tafi?’
Ya gyara zama yana cewa ‘Khadeeja dai na tambayeta itama bata ganshi ba, amma gidan mama ma ni na manta da su. Bari na kirawosu na ji.’
Kafin ya gama laluben lambar suka jiyo bugun kofa, gaba dayansu suka nufi kofar saboda Alhaji ya bada sanarwa a masallaci yayi zaton ko an sami wani labari ne.
PAGE 228
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ga mamakinsu Kawu Auwal ne wato kanin Ma’u tare da Habib din. Suna hada ido Mustapha ya kai masa duka yana cewa ‘Shine zaka fice ba tare da ka gayawa mutane ba saboda raini ko?’
Alhaji yace ‘Ka barshi mana ya zauna yayi bayani.’
Suka karasa cikin gidan suka zauna a parlor din Alhaji.
Bayan sun gaggaisa Kawu Auwalu yace ‘Wallahi nima da asuba Mama ta kirawoni tace na zo na dawo da shi, itama ta yi zaton an san yana gidan shi yasa ma bata nemi kowa ba. Sai dazu bayan sallar asuba Antinsa Khadeeja ta kirawota tana cigiyarsa. Shine ta kirawoni tace na kawo shi nan nayi bayani.’
Alhaji yayi masa godiya sannan ya dubu Habib yace ‘Mutumina ya haka kuma? Me suka yi maka a gidan da zaka bi dare ka gudu? Kuma madadin ka zo ka gaya min sai ka tafi ka dagawa Mama hankali.’
A nan ne ya sami dama ya gayawa Alhaji abinda ya faru, sannan ya sanar da shi irin zaman da ake yi a gidan.
Hajia tace ‘Dama Aminan Jidda ta fada, tace wancan zuwan da suka yi gidan basu ma ga Najan ba. Kamar yaran suna kasa su da mai aiki suna rayuwarsu ita kuma tana sama ita da nata yaran, kuma yanda ya fada haka Aminana ta fada tace shi kanshi Mustaphan yaran basa ganinshi sai dai idan ya sauko.’
Shima Auwalu ya tabbatar musu da cewa duk wadannan maganganu yaran sun dade da yiwa Mama bayani, sai dai da yake ta dauka ba huruminta bane shi yasa ma bata ce komai ba. Amma dai gaskiya da akwai matsala, tunda ai da ba a taba samun matsala irin wannan ba.’
‘Hakane, in sha Allahu za a duba kuma a dauki mataki.’ Alhaji ya fada.
Suka karasa tattaunawa Auwalu yayi musu sallama ya tafi.
Shima Mustapha ya mike ya sa Habib a gaba don su tafi, sai dai shi habib din ya nuna ba zai koma don ya fi so ya zauna a nan wajen Hajia. Alhaji ne ya saka shi a gaba da nasiha yana nuna masa gara ya zauna saboda kannensa, kada ya tafi ya barsu su kuma bai san me zai faru da su ba.
Sai wajen karfe tara sannan Hajia ta shirya suka kama hanya tare da Habib din da Mustapha suka koma gidan.
PAGE 229
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Jimawa kadan ya fito ya sake kaya sannan ya wuce ya zauna a dining table ya fara cin abinci. Yana cikin cin abincin ya dauki waya ya kirawo Habib, ba tare da bata lokaci ba ya hawo ya same shi.
‘Abba gani.’ Ya fada yana tsaye daga gefe.
Ya ajiye cokalin da yake hannunsa sannan yace ‘Habib me yasa Antinka ta saka ka wanki ka ki yi?’
Yace ‘Abba ba kin yi nayi ba, wankin ne da yawa kuma nace gobe zan samo musu yaro ya wanke a biya shi.’
‘Kala dayan ne da yawa? Kayan ma da ba nawa bane.’ Ta fada tana wasu muzurai.
Yace ‘Ni dai kayan da aka bani zasu kai kamar kala biyar ko fiye, ban sani ba ko ba su aka nuna miki ba.’
Abbansu yace ‘Ka ga Malam, bana son wani karin bayani. An ce kaya kala daya ne kuma gobe ake so ayi amfani da su. Kace a baka kayan ka wanke yanzu in ba so kake ranka ya baci ba, kuma daga yau bana son a saka ka aiki ka dinga kin yi. Ba zan dauki taurin kai da rashin kunya ba.’
Ya bude baki zai yi magana sai kuma ya fasa, ya juya ya fice.
Ya dubi Najan yace ‘Kije kice mata ta bashi kayan ya wanke.’
Ta tashi ta fice.
Yana zaune a tsakar gida wajen Baba maigadi Shukra taje ta kirawoshi. Yana shigowa ya ci karo da wankin a zube a bakin kofa; tabbas wankin sun fi kala biyar. Yana shiga cikin parlor din kafin yayi magana Naja da take tsaye tace ‘Gasu nan kaje ka wanke, kuma wallahi idan basu fita ba sakewa zaka yi har sai sun fita.’
Ta juya ta haye sama ta barsu a nan shi da kannensa.
Ya juya ya dawo ya tsaya a kan wankin yana kare musu kallo yana tunani; tabbas ba zai yi wankin nan ba, ko da kuwa kala dayan ta bayar kamar yanda tace. Kuma yanda yaga a gaban Abban tace kala daya ne kuma ta dauko kaya da yawa haka ta bashi ya san ta shirya wata makarkashiyar.
PAGE 226
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya san ba lallai Abbanshi ya saurareshi ba saboda tana gabansa tana tsara masa zance, kuma ya san idan har yayi wannan wankin to ta sami damar da zata mayar da shi dan aikin gida kuma ba zai yi ba. Haka ya kewaye ya fice ya bar wankin a nan inda ta ajiye su.
………
Suna sama ita da maigidan suna ta hirarsu cikin kwanciyar hankali, sai waje karfe tara sannan Anti Wiyya ta fito daga dakin baki ta ga wankin. Tayi matukar mamaki musamman da ta tambayi Afaf ta tabbatar mata Habib din ya fice bai dauki wankin ba. Nan ta koma daki ta kirawo Naja a waya wadda ta sauko, ta nuna mata wankin sannan tayi mata bayanin cewa a nan ya fice ya barsu.
Yaran suna kallo ta tsuguna ta tsince kayan ta bar kala daya da hijab guda daya sannan Anti Wiyyan ta koma daki ita kuma ta haye sama.
Jimawa kadan Mustapha ya sako yana tambayar Afaf ina kaninta.
‘Abba ban ganshi ba, ficewa kawai yayi ba tare da yace komai ba.’ Ta bashi amsa.
A fusace ya murda kofar dakin Habib din ya shiga yana kiransa, sai dai ga mamakinsa Habib din baya cikin dakin. Ya fice wajen Baba Maigadi inda ya tabbatar masa bai san inda Habib yake ba, ya kara da cewa ‘Bana jin ma fita yayi, don tun da aka ce ya zo kana kiransa ban sake ganin gilmawarsa ba. Sai dai ko da ina sallah ne ya fice ban sani ba.’
Ya koma cikin gidan ba tare da yace komai ba.
Yana shiga parlor din ya dubi kayan yace ‘Nasreen zo ki kwashi kayan nan ki mayar mata, yayan naki zai zo ya same ni.’
Ya haye saman inda ya tara da Naja a zaune a parlor ita da Rukayya, ya sami waje ya zauna sannan ya dauki wayarsa ya dannawa Habib kira. Ba karamin mamaki yayi ba da yaji wayar Habib din a kashe, sai dai yayi tunanin kashe wayar Habib din yayi don ya san bashi da gaskiya. Don haka sai kawai ya sauko ya sanar da Baba Maigadi cewa idan Habib ya shigo gidan yayi masa waya.
……..
Tun yana sa ran shigowar Habib har abun ya fara bashi tsoro; yaran duk sun tafi sun kwanta har sha biyun dare ta yi amma Habib bai shigo gidan ba, gashi sai kiran wayarsa ake yi a kashe. Yana son ya kirawo Hajia ko Habib din yaje can amma kuma baya son ya daga musu hankali.
PAGE 227
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid
A karo na babu iyaka motsin shigarsa dakin ne ya farakar da ita daga bacci, ta gyarawa Baby Maryam kwanciyarta sannan ta dubeshi tace ‘Wai bai dawo ba.’
A jigace yace ‘Eh, wallahi har abun ya fara bani tsoro. To ina Habib zai tafi? Ina ma ya sani a garin nan shi da ba wani yawo yake ba?’
Tace ‘Ya zaka ce ina ya sani yaron da yake level 1, kuma yake tafiya makaranta da kansa. Ai yanzu ba kamar da bane, tsaf ya san ko ina.’
‘To ina zai tafi a wannan daren? Gashi Baba Maigadi ma yace ko fitarsa bai gani ba kuma gidan nan babu inda bamu duba ba baya nan.’
Tace ‘To ka dai yi hakur ka zo ka kwanta tunda ka ga yanzu dayan dare ta kusa, zuwa wayewar gari sai a nemoshi a bashi hakuri a gaya masa ya barwankin.’
‘Mtseww! Wai kin san me kike fada kuwa? Na zo na kwanta saboda ke kin kwanta ko?’ ya sake jan tsaki sannan ya fice daga dakin ya rufe mata kofar da karfi, rufe kofar da sai da ya farkar mata da Baby daga barci.
Ta juya a fusace tana gunguni ta dauki yarinyarta ta saka mata nono.
Yanda yaga rana haka yaga dare, yana zaune a parlor shi kadai. Sai dai idan bacci ya daukeshi yayi firgigit ya farka, ya sake buga lambar Habib amma a kashe. Yana fara jin kiran sallar asuba ya kirawo Alhaji ya sanar da shi ba a ga Habib ba.
A shirye ya fice masallaci, bayan an idar da sallar asuba ya sanar da su bacewar habib. Yana dawowa gidan ya dauki mukullin motarsa ya fice ya nufi gidan Hajia.
Suma a tsaye ya samesu cikin tashin hankali, nan suka zauna suna jira gari ya kara wayewa suje police station su sanar.
Suna zaune a parlor din Alhaji cikin tashin hankali Hajia ta dubi Mustapha tace ‘Kuma ka tuntubi kakanninsa, can gidan su Ma’u da ma ita Khadeejan ko wajensu ya tafi?’
Ya gyara zama yana cewa ‘Khadeeja dai na tambayeta itama bata ganshi ba, amma gidan mama ma ni na manta da su. Bari na kirawosu na ji.’
Kafin ya gama laluben lambar suka jiyo bugun kofa, gaba dayansu suka nufi kofar saboda Alhaji ya bada sanarwa a masallaci yayi zaton ko an sami wani labari ne.
PAGE 228
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ga mamakinsu Kawu Auwal ne wato kanin Ma’u tare da Habib din. Suna hada ido Mustapha ya kai masa duka yana cewa ‘Shine zaka fice ba tare da ka gayawa mutane ba saboda raini ko?’
Alhaji yace ‘Ka barshi mana ya zauna yayi bayani.’
Suka karasa cikin gidan suka zauna a parlor din Alhaji.
Bayan sun gaggaisa Kawu Auwalu yace ‘Wallahi nima da asuba Mama ta kirawoni tace na zo na dawo da shi, itama ta yi zaton an san yana gidan shi yasa ma bata nemi kowa ba. Sai dazu bayan sallar asuba Antinsa Khadeeja ta kirawota tana cigiyarsa. Shine ta kirawoni tace na kawo shi nan nayi bayani.’
Alhaji yayi masa godiya sannan ya dubu Habib yace ‘Mutumina ya haka kuma? Me suka yi maka a gidan da zaka bi dare ka gudu? Kuma madadin ka zo ka gaya min sai ka tafi ka dagawa Mama hankali.’
A nan ne ya sami dama ya gayawa Alhaji abinda ya faru, sannan ya sanar da shi irin zaman da ake yi a gidan.
Hajia tace ‘Dama Aminan Jidda ta fada, tace wancan zuwan da suka yi gidan basu ma ga Najan ba. Kamar yaran suna kasa su da mai aiki suna rayuwarsu ita kuma tana sama ita da nata yaran, kuma yanda ya fada haka Aminana ta fada tace shi kanshi Mustaphan yaran basa ganinshi sai dai idan ya sauko.’
Shima Auwalu ya tabbatar musu da cewa duk wadannan maganganu yaran sun dade da yiwa Mama bayani, sai dai da yake ta dauka ba huruminta bane shi yasa ma bata ce komai ba. Amma dai gaskiya da akwai matsala, tunda ai da ba a taba samun matsala irin wannan ba.’
‘Hakane, in sha Allahu za a duba kuma a dauki mataki.’ Alhaji ya fada.
Suka karasa tattaunawa Auwalu yayi musu sallama ya tafi.
Shima Mustapha ya mike ya sa Habib a gaba don su tafi, sai dai shi habib din ya nuna ba zai koma don ya fi so ya zauna a nan wajen Hajia. Alhaji ne ya saka shi a gaba da nasiha yana nuna masa gara ya zauna saboda kannensa, kada ya tafi ya barsu su kuma bai san me zai faru da su ba.
Sai wajen karfe tara sannan Hajia ta shirya suka kama hanya tare da Habib din da Mustapha suka koma gidan.
PAGE 229
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)