Sashe 17
Mijin Marigayiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai a lokacin ma sannan ya tuna ashe tana zuwa jami’a; amma dai shi har yanzu bai gane dalilin da yasa ba zata koma yau din ba har sai nan da sati biyu. Ya dai fahimci so take kawai tace aikin gida da na yara ya mata yawa, kuma shi bai ga wani wahala a ciki ba tunda Ma’u ma ko sau daya bata taba daukan mai aiki ba haka take komai da kanta.
PAGE 69
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Kawai dai ya fahimci Mommyn Khadeeja tana da son zuciya da iko shine take son ta juya shi kamar yanda take juya Baffansu, kuma gaskiya shi ba zai dau wannan ba.
Haka dai ya gama kwana-kwanarsa ya tashi ya kwashi yaransa suka wuce gidan Hajia cike da takaicin Mommy Khadeeja wadda duk ita ya dorawa laifi, gani yake kamar itace take juya Khadeeja da Baffan gaba daya.
Tuni Mommy ta bada umarni a samo mata ‘yar aiki.
………
Ransa a bace ya shiga gidan Hajia.
Yana shiga ya tarar da Yaya Jidda a gidan ita da yaranta, suna zaune a parlor din Hajia suna hira. A gaggauce yaran suka gaisa da Hajia da Yaya Jidda suka shige wajen Baffa da gudu inda yake zaune yana jiran Kaman dan autan gidan ya dawo daga shan mai ya kai shi unguwa. A nan Mustapha ya zauna wajen Hajia da yaya Jidda, bayan sun gaggaisaya dubi Yaya Jidda yace ‘Ke Yaya sai kace jira kike a bude gari ki taho, har ma kin rigani zuwa.’
Tayi dariya tace ‘Ni dama babu ni a lockdown in dai gidan nan ne kullum sai na zo, Alhaji ma ya gaji ya barni.’
Hajia ta dubeshi tace ‘Ya jikin Khadeejan?’
Ya dan karkata kai yace ‘Da sauki.’
‘Jiya ma munyi waya da Mommyn tata ai, ta dawo gidan ko sai kun fita daga nan zaku daukota?’
‘Mtseww!’ Ya ja gajeran tsaki sannan ya cigaba ‘Daga can muke, wai Mommyn tace bata gama hutawa ba kuma sai an mata wanka da gyara za a dawo da ita zuwa bayan sallah.’
Hajia ta gyara zama ta kama haba ‘Ikon Allah, to kai kuma sai kace me?’
‘To Hajia ya zan yi da su; shima baban nata bayan tuni muka gama magana da shi yace nazo na dauketa ina zuwa kuma ya canza zance; yace wai na barta. Itama kuma Khadeejan kamar haka ta zaba, kin ga kenan babu yanda zan yi da ita. Da ace ma ta bani hadin kai ne da zata iya canzawa Mommyn ra’ayi don kula kamar wannan shirin duka nata ne.’
Kafin Hajia tace wani abu Yaya Jidda tace ‘Ai kuwa lallai shiri, barin ne sai an yi wani wanka da gyara? Lallai matan nan, nifa dama shi yasa yaran ‘yan bokon nan basa wani burgeni, ciki fal iyayin tsiya.’
PAGE 70
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Hajia tace ‘To me suke nufi? Wannan duk ranar da ta haihu ai sai ta shekara sun gyara sannan zasu baka ita. To yanzu ya suke so kayi da wadannan ‘yayan, ko kuwa don ba ita ta haifesu ba? Tunda ia da nata ne hadawa zasuyi da su ko kuma ita da kanta ma ba zata yarda ta tafi ta barsu ba. Wannan ai ba tsari bane ba ma, sai dai da yake dama an bar gidan a hannun mace ai dole a ga son zuciya irin wannan.’
Ya gayara zama yace ‘Hmmm! Su suka sani kuma.’
‘To yanzu ya zaka yi da yaran? Ko kuwa haka zaku hakura kuyi zamanku tunda dama babu fita? Ko kuma nan zaka bar mini su sai muyi zamanmu, ka ga na sha allura a wajen Dr. Nasreen.’
Ya dubi Yaya Jidda sannan yace ‘Da tunani nake na barsu wajen Yaya Jidda sai na koma na dauko musu kayansu, in ya so sai a barsu iyayen Khadeejan muga lokacin da zasu dawo da ita.’
Har hajia ta bude baki zata yi magan Yaya Jidda ta tari numfashinta ‘Eh to kuma ka ga da sai muyi zaman mu, sai dai ka san gidan namu karami ne wajen kwanan zai iya yi musu kadan gaba daya da nawa yaran. Ko nan din ma ka barsu wajen Hajiyan ai duk muna tare tunda kullum ni nake zuwa na tsaya a kan hidimar gidan.’
Suka yi shiru na dan lokaci kowa da abinda yake tunani, jiamwa kadan hajia tace ‘To hakan ma ai yayi, ka bar min su a nan tunda ga baito nan tana nan zata iya duk wata hidimarsu. Tunda ka ga ai ba ma tsari ace kana zaune a gida daga kai sai yaranka yaran ma mata.’
‘Ba damuwa, zan je na dauko kayansu kafin biyar din ta yi.’
Ya tashi ya fice wajen Alhaji.
Yaya Jidda tabi bayansa da kallo; ya bata tausayi amma gaskiya ba zata karbi su Afaf ba, gara dai a nan din. Can gidanta idama ga nata yaran wadanda iadna ta ga dama nan take turosu wajen Hajia suci abinci suyi koamia sannan kuma a kara mata wasu? Gaskiya ba zata iya ba.
…..
Sai da la’asar ta kusa sannan ya fita yaje gidan ya hado musu kayansu ya kawo sannan ya koma ya barsu a nan.
PAGE 71
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Karo na babu iyaka kenana da ta dauki wayarta ta budo whatsapp ta duba; har yanzu bai amsa messages dinta ba kuma bai biyo whatsapp call din da ta yi masa ba. To me yake faruwa ne? Allah dai yasa lafiya Mustapha yake da shi da yaran. Da farko da taga tayi magana ta whatsapp bai kulata ba kuma ta kirawoshi ta whatsapp din bai daga ba sai ta zata ko fushi yayi, amma dai zuwa yau kwana uku abun ya fara bata tsoro kada taje ko wani abu ne ya sameshi.
Ta riga ta san babuu credit a wyar don haka ko balance ma bata duba ba; shi din ba mutum ne mai son saka mata credita ba, idan ma tayi magana sai yace wa zata kirawo ko kuma me zata yi da data din. Idan aka yi albashi dai idan ta yi magana yana saka mata naira dari biyar, shine zata samu ta raba ta sa data sauran ta dan yi waya. Don haka yanzun ma babu na wayar sai dai data din da ta yi mata saura. Tayi tsaki sannan ta sauka daga kan gadon Nabila inda take kwance ta wuce dakin Mommy.
A parlor ta sami Mommy tana zaune tana kallon tafsiri a tashar Sunnah TV, ta zauna a kusa da ita bayan tayi sallama ta amsa. Sai da suka dan yi jim kadan ta kula dai Mommy babu abinda zata ce mata sannan tace ‘Mommy don Allah ki dan saka min 1k a waya mana.’
Ta kalleta tana dariya tace ‘1k kuma? Ina Mustaphan ko kuma yau ba nashi kike so ba tunda kina gidana nawa kike so?’
Itama dariyar tayi ta kara langabe kai ‘A’a Mommy, don Allah dai ki taimaka, wallahi ya saka min kararwa nayi kuma dai kin san bani da kudi.’
‘Ke kenan kullum baki da kudi?’
‘Mommy bari dai na fara aiki.’
‘Uhm, shi Mustaphan ko dan na kashewa baya yaga miki balle gaki ‘yar makaranta?’
Ta dan marairaice ‘To ai kin ga yanzu anyi hutu Mommy, duk ‘yan sauran canjin ma na kashe.’
‘Shi yasa kike maula kuma? To dauko min wayata a daki na saka miki a cikin wanda mijina ya bani.’
Ta mike tana dariya tace ‘Mommy.’
PAGE 72
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Baffanta ba wai millionaire bane amma dai ta san yana da kyauta; duk da Mommy tana sayar da ‘yan kunnaye da sarkoki amma duk wata sai ya tura mata kudin kashewa account dinta sai dai ko ya tura babu yawa amma fa sai ya tura. Kuma idan dai ta bukaci wani abu bayan wannan to yana iya bakin kokarinsa wajen ganin yayi mata sai dai ko idan babu hali.
Tayi zaton haka zata je ta samu a wajen Mustapha, musamman da yake yana yawan yi mata kyaututtuka da saka credit a waya laokacin da yana neman aurenta. Sai dai bayan ta shiga gidan sai ta tarar ba haka bane; don wani lokacin a kan ya saka mata kati a waya ya gwammace ya bata aron wayarsa tayi waya. Ko da ta koma makaranta ma tayi zaton zai dan dinga bata kudin makaranta da kudin kashewa sai dai tun a ranar farko da gane ba zai jure ba. Domin da farko bayan ta gama shiryawa tayi zaton zai kaita ne, amma sai dai suna fitowa da aka zo inda zai dauke hanya ya wuce office dinsu sai yace ta sauka a nan ta hau motar haya. Da tayi maganar kudin mota kuma sai yace mata wai ya zata tana da kudi; ta dai samu ya bata naira dubu kamar ba da son ranshi ba. Tun daga ranar ma sai ya zama ta daina damuwa tayi saui ta shirya ta bishi, yawanci sai ta jira idan ya fita sai ta kama hanya a motar haya. Kudin motar ma tana shirin ta tambayi Baffa ya dinga bata aka shiga lockdown; kuma har yanzu tana da niyyar kafin ta koma gida ta sanar da Baffanta kawai ya dinga tura mata kudin mota. Tana ta wannan tunanin taje ta dauko wayar ta kawowa Momy; ba tare da bata lokaci ba ta tura mara katin naira dubu kamar yanda ta bukata.
Nan da nan ta koma daki ta sake hayewa kan gadon Nabila sannan ta danna masa kira.
Sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ya dauka, cike da isa yana magana da kyar ya amsa sallamarta, haka ma gaisuwarta kamar ba zai amsa ba. Wannan ya sa jikinta yayi sanyi kuzarin da ta fara wayar da shi duk ya gushe.
Cikin sanyi murya tace ‘Babe, ya na jika haka? Ko baka da lafiya ne?’
PAGE 69
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Kawai dai ya fahimci Mommyn Khadeeja tana da son zuciya da iko shine take son ta juya shi kamar yanda take juya Baffansu, kuma gaskiya shi ba zai dau wannan ba.
Haka dai ya gama kwana-kwanarsa ya tashi ya kwashi yaransa suka wuce gidan Hajia cike da takaicin Mommy Khadeeja wadda duk ita ya dorawa laifi, gani yake kamar itace take juya Khadeeja da Baffan gaba daya.
Tuni Mommy ta bada umarni a samo mata ‘yar aiki.
………
Ransa a bace ya shiga gidan Hajia.
Yana shiga ya tarar da Yaya Jidda a gidan ita da yaranta, suna zaune a parlor din Hajia suna hira. A gaggauce yaran suka gaisa da Hajia da Yaya Jidda suka shige wajen Baffa da gudu inda yake zaune yana jiran Kaman dan autan gidan ya dawo daga shan mai ya kai shi unguwa. A nan Mustapha ya zauna wajen Hajia da yaya Jidda, bayan sun gaggaisaya dubi Yaya Jidda yace ‘Ke Yaya sai kace jira kike a bude gari ki taho, har ma kin rigani zuwa.’
Tayi dariya tace ‘Ni dama babu ni a lockdown in dai gidan nan ne kullum sai na zo, Alhaji ma ya gaji ya barni.’
Hajia ta dubeshi tace ‘Ya jikin Khadeejan?’
Ya dan karkata kai yace ‘Da sauki.’
‘Jiya ma munyi waya da Mommyn tata ai, ta dawo gidan ko sai kun fita daga nan zaku daukota?’
‘Mtseww!’ Ya ja gajeran tsaki sannan ya cigaba ‘Daga can muke, wai Mommyn tace bata gama hutawa ba kuma sai an mata wanka da gyara za a dawo da ita zuwa bayan sallah.’
Hajia ta gyara zama ta kama haba ‘Ikon Allah, to kai kuma sai kace me?’
‘To Hajia ya zan yi da su; shima baban nata bayan tuni muka gama magana da shi yace nazo na dauketa ina zuwa kuma ya canza zance; yace wai na barta. Itama kuma Khadeejan kamar haka ta zaba, kin ga kenan babu yanda zan yi da ita. Da ace ma ta bani hadin kai ne da zata iya canzawa Mommyn ra’ayi don kula kamar wannan shirin duka nata ne.’
Kafin Hajia tace wani abu Yaya Jidda tace ‘Ai kuwa lallai shiri, barin ne sai an yi wani wanka da gyara? Lallai matan nan, nifa dama shi yasa yaran ‘yan bokon nan basa wani burgeni, ciki fal iyayin tsiya.’
PAGE 70
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Hajia tace ‘To me suke nufi? Wannan duk ranar da ta haihu ai sai ta shekara sun gyara sannan zasu baka ita. To yanzu ya suke so kayi da wadannan ‘yayan, ko kuwa don ba ita ta haifesu ba? Tunda ia da nata ne hadawa zasuyi da su ko kuma ita da kanta ma ba zata yarda ta tafi ta barsu ba. Wannan ai ba tsari bane ba ma, sai dai da yake dama an bar gidan a hannun mace ai dole a ga son zuciya irin wannan.’
Ya gayara zama yace ‘Hmmm! Su suka sani kuma.’
‘To yanzu ya zaka yi da yaran? Ko kuwa haka zaku hakura kuyi zamanku tunda dama babu fita? Ko kuma nan zaka bar mini su sai muyi zamanmu, ka ga na sha allura a wajen Dr. Nasreen.’
Ya dubi Yaya Jidda sannan yace ‘Da tunani nake na barsu wajen Yaya Jidda sai na koma na dauko musu kayansu, in ya so sai a barsu iyayen Khadeejan muga lokacin da zasu dawo da ita.’
Har hajia ta bude baki zata yi magan Yaya Jidda ta tari numfashinta ‘Eh to kuma ka ga da sai muyi zaman mu, sai dai ka san gidan namu karami ne wajen kwanan zai iya yi musu kadan gaba daya da nawa yaran. Ko nan din ma ka barsu wajen Hajiyan ai duk muna tare tunda kullum ni nake zuwa na tsaya a kan hidimar gidan.’
Suka yi shiru na dan lokaci kowa da abinda yake tunani, jiamwa kadan hajia tace ‘To hakan ma ai yayi, ka bar min su a nan tunda ga baito nan tana nan zata iya duk wata hidimarsu. Tunda ka ga ai ba ma tsari ace kana zaune a gida daga kai sai yaranka yaran ma mata.’
‘Ba damuwa, zan je na dauko kayansu kafin biyar din ta yi.’
Ya tashi ya fice wajen Alhaji.
Yaya Jidda tabi bayansa da kallo; ya bata tausayi amma gaskiya ba zata karbi su Afaf ba, gara dai a nan din. Can gidanta idama ga nata yaran wadanda iadna ta ga dama nan take turosu wajen Hajia suci abinci suyi koamia sannan kuma a kara mata wasu? Gaskiya ba zata iya ba.
…..
Sai da la’asar ta kusa sannan ya fita yaje gidan ya hado musu kayansu ya kawo sannan ya koma ya barsu a nan.
PAGE 71
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Karo na babu iyaka kenana da ta dauki wayarta ta budo whatsapp ta duba; har yanzu bai amsa messages dinta ba kuma bai biyo whatsapp call din da ta yi masa ba. To me yake faruwa ne? Allah dai yasa lafiya Mustapha yake da shi da yaran. Da farko da taga tayi magana ta whatsapp bai kulata ba kuma ta kirawoshi ta whatsapp din bai daga ba sai ta zata ko fushi yayi, amma dai zuwa yau kwana uku abun ya fara bata tsoro kada taje ko wani abu ne ya sameshi.
Ta riga ta san babuu credit a wyar don haka ko balance ma bata duba ba; shi din ba mutum ne mai son saka mata credita ba, idan ma tayi magana sai yace wa zata kirawo ko kuma me zata yi da data din. Idan aka yi albashi dai idan ta yi magana yana saka mata naira dari biyar, shine zata samu ta raba ta sa data sauran ta dan yi waya. Don haka yanzun ma babu na wayar sai dai data din da ta yi mata saura. Tayi tsaki sannan ta sauka daga kan gadon Nabila inda take kwance ta wuce dakin Mommy.
A parlor ta sami Mommy tana zaune tana kallon tafsiri a tashar Sunnah TV, ta zauna a kusa da ita bayan tayi sallama ta amsa. Sai da suka dan yi jim kadan ta kula dai Mommy babu abinda zata ce mata sannan tace ‘Mommy don Allah ki dan saka min 1k a waya mana.’
Ta kalleta tana dariya tace ‘1k kuma? Ina Mustaphan ko kuma yau ba nashi kike so ba tunda kina gidana nawa kike so?’
Itama dariyar tayi ta kara langabe kai ‘A’a Mommy, don Allah dai ki taimaka, wallahi ya saka min kararwa nayi kuma dai kin san bani da kudi.’
‘Ke kenan kullum baki da kudi?’
‘Mommy bari dai na fara aiki.’
‘Uhm, shi Mustaphan ko dan na kashewa baya yaga miki balle gaki ‘yar makaranta?’
Ta dan marairaice ‘To ai kin ga yanzu anyi hutu Mommy, duk ‘yan sauran canjin ma na kashe.’
‘Shi yasa kike maula kuma? To dauko min wayata a daki na saka miki a cikin wanda mijina ya bani.’
Ta mike tana dariya tace ‘Mommy.’
PAGE 72
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Baffanta ba wai millionaire bane amma dai ta san yana da kyauta; duk da Mommy tana sayar da ‘yan kunnaye da sarkoki amma duk wata sai ya tura mata kudin kashewa account dinta sai dai ko ya tura babu yawa amma fa sai ya tura. Kuma idan dai ta bukaci wani abu bayan wannan to yana iya bakin kokarinsa wajen ganin yayi mata sai dai ko idan babu hali.
Tayi zaton haka zata je ta samu a wajen Mustapha, musamman da yake yana yawan yi mata kyaututtuka da saka credit a waya laokacin da yana neman aurenta. Sai dai bayan ta shiga gidan sai ta tarar ba haka bane; don wani lokacin a kan ya saka mata kati a waya ya gwammace ya bata aron wayarsa tayi waya. Ko da ta koma makaranta ma tayi zaton zai dan dinga bata kudin makaranta da kudin kashewa sai dai tun a ranar farko da gane ba zai jure ba. Domin da farko bayan ta gama shiryawa tayi zaton zai kaita ne, amma sai dai suna fitowa da aka zo inda zai dauke hanya ya wuce office dinsu sai yace ta sauka a nan ta hau motar haya. Da tayi maganar kudin mota kuma sai yace mata wai ya zata tana da kudi; ta dai samu ya bata naira dubu kamar ba da son ranshi ba. Tun daga ranar ma sai ya zama ta daina damuwa tayi saui ta shirya ta bishi, yawanci sai ta jira idan ya fita sai ta kama hanya a motar haya. Kudin motar ma tana shirin ta tambayi Baffa ya dinga bata aka shiga lockdown; kuma har yanzu tana da niyyar kafin ta koma gida ta sanar da Baffanta kawai ya dinga tura mata kudin mota. Tana ta wannan tunanin taje ta dauko wayar ta kawowa Momy; ba tare da bata lokaci ba ta tura mara katin naira dubu kamar yanda ta bukata.
Nan da nan ta koma daki ta sake hayewa kan gadon Nabila sannan ta danna masa kira.
Sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ya dauka, cike da isa yana magana da kyar ya amsa sallamarta, haka ma gaisuwarta kamar ba zai amsa ba. Wannan ya sa jikinta yayi sanyi kuzarin da ta fara wayar da shi duk ya gushe.
Cikin sanyi murya tace ‘Babe, ya na jika haka? Ko baka da lafiya ne?’