Sashe 2
Mijin Marigayiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A take Mommy ta fito daga daki rike da waya jiki a sanyaye, Ahmad ya kalleta yace ‘Mommy ai an daura auren Yaya Khadija ko?’
Ta daga kai tana cewa ‘Eh, yanzu Baffanku yake gaya min an daura auren.’ ta juya ta dubi Khadija tace ‘Khadija kin zama matar aure.’
Ta fada kan kujera kamar wadda aka tura, to murna zata yi ko me? Bata taba zata za a daura aure yau ba, ta zata za ayi yanda aka saba; a kawo kudin aure a zo a sa rana sannan a shirya biki a nutse. Shikenan yanzu ta zama matar Mustapha? Ikon Allah.
Ta kai hannu ta shafa kwarmin idonta inda taji danshi; kwallace ta fado. To kukan me takeyi? Murna takeyi ko kuwa tsabar mamaki ne?
Nabila ta zauna ta doro hannunta a kafadarta tana kallon Mommy tana cewa ‘To Mommy sai mu fara shirin bikin kenan ko kaita kawai za ayi haka?’
Ta banka mata harara tana cewa ‘Sai kace wata kaza?’
Mommy tace ‘Uhm, sai dai mu jira Baffanku ya dawo muji.'
Ta koma daki ta barsu a nan.
____
To Yaya? Me kuke tunanin zai faru? Ga amarya ga ango, kuma ga lockdown a hanya.
Gaba daya tunanin Khadija ya tsaya, wannan daura auren da aka ce an yi mata yana nufin nan da ‘yan kwanakin zata tare a gidan Mustapha. Fatanta daya Daddy ya bari ayi biki don gaskiya tana son biki.
Karar wayarta ne ya katse mata tunani, tana kallon wayar tayi murmushi “My love” shine sunan da tayi saving lambar Mustapha da shi.
'Hello.' ta amsa murya kasa-kasa.
Muryarsa zakwai cike da farin ciki yace ‘Ya na ji ki haka? Ko ba kya farin ciki ne? Alhaji ya hutar da mu, kinga next weekend kawai sai a kawo min amarya ta.’
Tayi dariya ‘I was just not expecting it to happen today, but Alhamdulillah. Ai babu abinda ya fi zama da masoyi dadi.’
'Hakane. So me kike bukata na bikin, ki sami Yaya Mama kuyi lissafi zuwa an jima sai ki gaya min na turo miki ta account dinki. In sha Allah ranar Tuesday za a kawo lefe.’
'Ok, hakan yayi.’
'Common, ni ina so na ji muryarki tayi zaki zakwai kamar tawan nan.’
Tayi dariya ‘Ka kirawoni in an jima kafin nan na sha zuma zaka ji zakin da muryar zata yi.’
Suka yi sallama ta ajiye wayar ta koma ta kwanta a kan gadon cikin sanyin jiki.
Dab da azahar Yaya Mama ta karaso tare da yaranta Anisa da Jawad. Itace Babba a ‘yayan gidan su Khadija. Bayan ta gama tsokanar Khadija ta shige daki inda ta tarar da Mommy tare da kanwarta Anti Naja'atu suna ta tattauna bikin; don Baffa ya sanar da su a shirya a yi biki ranar asabar da Lahadi idan an gama sai a kai amarya.
Bayan ta gaishesu ta zauna suka cigaba da tattaunawa a kan bikin.
Jimawa kadan Yaya Mama tace ‘Ni wallahi Mommy tausayi ma Khadija take bani, Allah ya sa dai da gaske yake sonta kuma ya cigaba da kula da ita. Ga yara har hudu yana shirin hada mata da su, ai sai a hankali.’
Anti Naja tace ‘Kada ki damu ai mace komai kankantarta raino baya gagararta.’
Mommy tace ‘Yaran ma fa yana kawosu nan wajenta, kamar suna da tarbiyya da saukin hali ma.’
'To kin ji ma. Kada kiyi mata magana ma ki sa ta zata wani tashin hankali ne don na ganta tun da aka ce an daura auren nan jikinta yayi sanyi.’
Haka suka gama tattaunawarsu suka tashi.
………..
Ranar Lahadi bayan Magriba aka shirya Khadija a ka kaita gidan Mustapha
Bai zo da abokansa ba sai mutum daya wato Badaru, ba tare da bata lokaci ba suka sallami kawayen amarya Badaru ya kwashesu.
Bayan ya rufe gidan ya dawo ya sameta tana ta faman share hawaye. Ya zauna ya lallasheta har tayi shiru sannan sukayi Sallah ya bude musu abincin da ya zo da shi suka ci. Da kansa ya kwashe kayan da suka gama cin abincin sannan ya dawo ya sameta a zaune a inda ya barta.
'Yauwa, tunda mun koshi taso na nuna miki gidan naki kafin mu kwanta.’ ya fada yana murmushi.
Ta mike a kunyace, har sun kama hanyar fita daga dakin ya juyo ya dubeta yana murmushi yace ‘Bari mu fara daga nan, nan ne dakinki.’
Tayi murmushi murya kasa-kasa tace ‘Ok.’
Ya wuce ta bishi a baya ya nuna mata ragowar gidan; bayan dakinta sai dakinsa sai kuma dakin yara inda nan ne kuma dakin baki. Sai kuma parlor guda daya da dining area a dai-dai kofar kitchen.
Bayan sun gama zagayawa ya kashe fitulun sannan suka wuce dakinsa inda zasu kwana.
……….
Ranar da Khadija ta cika kwana uku da tarewa a ranar bakin danginsa da suke ta zuwa ganin amarya sun lafa, don tunda gari ya waye babu wanda ya zo har azahar tayi. Suna zaune a parlor suna hirarrakinsu aka fara kiran Sallah, ya mike yana cewa ‘Bari naje masallaci na dawo.’
‘Ok, by then nima nayi sallar nayi serving lunch.’ ta amsa itama tana mikewa.
Tayi masa a dawo lafiya ya fice ita kuma ta shige kitchen.
Kafin ya dawo ta yi Sallah ta gyara kwalliyarta sanna ta jera abincin a kan dininga table. Yana dawowa tayi masa sannu da zuwa sannan ya zauna a dining table ta zuba abinci suka fara ci. Fried rice ne tare da sauce din hanta da salad, daga gefe kuma ga hadadden zobo. Shiru sukayi kowa yana ta kai loma, sai da Mustapha ya kusa cinye abincin nasa sannan ya ajiye cokalinsa ya dauki zobon da ta zuba masa a kofin tangaran ya kora. Yana ajiye kofin ya dauki cokalinsa yana gyara abincin ya dubeta yana cewa ‘Umm! Kin iya girki fa.’
Tayi dariya tace ‘Ai da na zaci santin kurma kake da ka kasa magana.’
'Au ashe ma sa min ido kika yi.’ ya fada yana sake cika baki da abincin.
Tayi dariya itama ta cigaba da cin abincin.
Bayan ya hadiye na bakinsa yace ‘Ina ga ai ya kamata in an jima muje mu debo su Afaf ko? Tun da suka ji an kawoki suke ta zumudi.’
Ta kalleshi tana wasa da cokalinta a kan abincin saboda ta riga ta koshi, tace ‘Babe ai na zata za a barsu sai mun dan huta, kaga shekaran jiya fa na tare. Ko gajiyar biki ma ai ban gama hucewa ba.’
‘Haba, ai sai ku huta tare, kin san suma fa they missed home don tunda mahaifiyarsu ta rasu rabonsu da gida.’
'Allah sarki, ni kaina ina dokin dawowarsu nan but babe please ka bari koda zuwa next week ne na dan gama kwance kayana.’ ta fada da muryar magiya da lallashi.
Ya ture farantin gabansa ya sake cika kofinsa na zobo, ya dan gatsina fuska yace ‘Ok, amma dai ba zasu ji dadi ba. Dazu muka gama waya da su suna ta dokin dawowa wajenki.’
Ya mike ya nufi wajen TV yayinda itama ta mike ta fara tattara kwanukan tana cewa ‘Allah sarki, in sha Allah next week da ni zamu je mu daukosu kaga daga nan ma sai mu biya gaba daya mu gaida Mommy mu gaida su Hajiya sai mu dawo gida.’
'Umm!’ ya amsa yana canza channel din TV.
Ta cigaba da kwashe kwanukan tunani kala-kala yana yawo a kwakwalwarta; ta yi zaton yana dokin kasancewa da ita, ta yanda zai bari su dan kara fahimtar juna kuma su more amarcinsu kafin ya dauko yaran amma shi yana maganar yau. Babu kananan yara a gidansu amma kusan kullum suna tare da yaran Yaya Mama, ta san yara ba zasu bari ta mori amarcinta ba tunda su rayuwarsu suna bukatar kulawa ne kullum. Musamman tunda ga Shukra mai shekaru uku kacal. Sati dayan ma da tace a kara kawai dai daurewa tayi don ita da a tunaninta ta sami kamar wata uku a gidan kafin ya kawo mata yara tunda a can ma inda suke ana kula dasu. To amma bata da wani zabi, zuwa next week din sai ta bishi suje su dauko yaran.
…….
Ana fara kiran magriba yayi alwala ya dauki mukullin motarsa, ya sameta a kitchen tana tsugene a tsakiyar kitchen din tana tuka tuwon shinkafa. Motsinsa ya sa ta saurara da tukin tuwon ta juyo, ta dubeshi tace ‘Fita zaka yi? Ko masallaci zaka je?’
'Eh, daga masallacin zan wuce na dubo yara sai kuma na wuce wajen Hajiya.’
Ta dan langabe kai ‘Babe ai da ka dawo, nima sai na shirya muje na gaida Hajiyan.’
'No ki bari next week zamu je tare.’ Ya amsa yana duba wayarsa.
Ta saki tukin tuwon ta mike ta nufeshi da niyyar ya rungumeshi, sai dai ya dan kauce don haka ta gefe ta rungumoshi. Jikinta ya dan yi sanyi ta sumbaci kumatunsa tace ‘A dawo lafiya Babe, I will wait for you idan ka dawo sai muyi dinner tare. Ka gaida su Hajiya.’
'Ok.' ya amsa sannan ya fice.
.........
A parlor ya sami Daddy, bayan sun gaisa suka dan taba hira. Daddy yace ‘Wai ka debo yaranka kuwa?’
'Ban debo su ba, tace a bari sai zuwa next week idan ta gama hutawa.’ Yana wani kau da kai.
‘To babu laifi; Amma fa idan ka daukosu to ka saka ido, ka san mata yanzu basa son riko. Idan baka yi wasa ba haka za a mayar maka da yara kamar almajirai a gidanka.’
'In sha Allah zan kula, duk da ma na kula kamar bata da muguntar.’
'A'a, basu fa da tabbas, kai dai ka sa ido. Kuma ka dinga bincikar duk motsinsu.’ Ya fada yana nuna shi da yatsa.
Suka dan sake hira sannan ya shiga wajen Hajiya inda ya samesu ita da Yaya Jidda suna hira; da yake ita gidanta kusa da gidan ne wataran ma sai an yi sallar Magriba take zuwa.
Bayan sun gaisa suka cigaba da hirarsu gaba daya. Jimawa kadan Yaya Jidda tace ‘Musty ina amarya? Tsohuwar sirikar taka ta baka yaran ko har yanzun ba zata bayar ba?’
Ya gyara zama yace ‘Haba, sai kace ita ta haifa min su ai dole ta bani su.’
Hajiya tace ‘Sai yaushe zaka dauko su?’
Ta daga kai tana cewa ‘Eh, yanzu Baffanku yake gaya min an daura auren.’ ta juya ta dubi Khadija tace ‘Khadija kin zama matar aure.’
Ta fada kan kujera kamar wadda aka tura, to murna zata yi ko me? Bata taba zata za a daura aure yau ba, ta zata za ayi yanda aka saba; a kawo kudin aure a zo a sa rana sannan a shirya biki a nutse. Shikenan yanzu ta zama matar Mustapha? Ikon Allah.
Ta kai hannu ta shafa kwarmin idonta inda taji danshi; kwallace ta fado. To kukan me takeyi? Murna takeyi ko kuwa tsabar mamaki ne?
Nabila ta zauna ta doro hannunta a kafadarta tana kallon Mommy tana cewa ‘To Mommy sai mu fara shirin bikin kenan ko kaita kawai za ayi haka?’
Ta banka mata harara tana cewa ‘Sai kace wata kaza?’
Mommy tace ‘Uhm, sai dai mu jira Baffanku ya dawo muji.'
Ta koma daki ta barsu a nan.
____
To Yaya? Me kuke tunanin zai faru? Ga amarya ga ango, kuma ga lockdown a hanya.
Gaba daya tunanin Khadija ya tsaya, wannan daura auren da aka ce an yi mata yana nufin nan da ‘yan kwanakin zata tare a gidan Mustapha. Fatanta daya Daddy ya bari ayi biki don gaskiya tana son biki.
Karar wayarta ne ya katse mata tunani, tana kallon wayar tayi murmushi “My love” shine sunan da tayi saving lambar Mustapha da shi.
'Hello.' ta amsa murya kasa-kasa.
Muryarsa zakwai cike da farin ciki yace ‘Ya na ji ki haka? Ko ba kya farin ciki ne? Alhaji ya hutar da mu, kinga next weekend kawai sai a kawo min amarya ta.’
Tayi dariya ‘I was just not expecting it to happen today, but Alhamdulillah. Ai babu abinda ya fi zama da masoyi dadi.’
'Hakane. So me kike bukata na bikin, ki sami Yaya Mama kuyi lissafi zuwa an jima sai ki gaya min na turo miki ta account dinki. In sha Allah ranar Tuesday za a kawo lefe.’
'Ok, hakan yayi.’
'Common, ni ina so na ji muryarki tayi zaki zakwai kamar tawan nan.’
Tayi dariya ‘Ka kirawoni in an jima kafin nan na sha zuma zaka ji zakin da muryar zata yi.’
Suka yi sallama ta ajiye wayar ta koma ta kwanta a kan gadon cikin sanyin jiki.
Dab da azahar Yaya Mama ta karaso tare da yaranta Anisa da Jawad. Itace Babba a ‘yayan gidan su Khadija. Bayan ta gama tsokanar Khadija ta shige daki inda ta tarar da Mommy tare da kanwarta Anti Naja'atu suna ta tattauna bikin; don Baffa ya sanar da su a shirya a yi biki ranar asabar da Lahadi idan an gama sai a kai amarya.
Bayan ta gaishesu ta zauna suka cigaba da tattaunawa a kan bikin.
Jimawa kadan Yaya Mama tace ‘Ni wallahi Mommy tausayi ma Khadija take bani, Allah ya sa dai da gaske yake sonta kuma ya cigaba da kula da ita. Ga yara har hudu yana shirin hada mata da su, ai sai a hankali.’
Anti Naja tace ‘Kada ki damu ai mace komai kankantarta raino baya gagararta.’
Mommy tace ‘Yaran ma fa yana kawosu nan wajenta, kamar suna da tarbiyya da saukin hali ma.’
'To kin ji ma. Kada kiyi mata magana ma ki sa ta zata wani tashin hankali ne don na ganta tun da aka ce an daura auren nan jikinta yayi sanyi.’
Haka suka gama tattaunawarsu suka tashi.
………..
Ranar Lahadi bayan Magriba aka shirya Khadija a ka kaita gidan Mustapha
Bai zo da abokansa ba sai mutum daya wato Badaru, ba tare da bata lokaci ba suka sallami kawayen amarya Badaru ya kwashesu.
Bayan ya rufe gidan ya dawo ya sameta tana ta faman share hawaye. Ya zauna ya lallasheta har tayi shiru sannan sukayi Sallah ya bude musu abincin da ya zo da shi suka ci. Da kansa ya kwashe kayan da suka gama cin abincin sannan ya dawo ya sameta a zaune a inda ya barta.
'Yauwa, tunda mun koshi taso na nuna miki gidan naki kafin mu kwanta.’ ya fada yana murmushi.
Ta mike a kunyace, har sun kama hanyar fita daga dakin ya juyo ya dubeta yana murmushi yace ‘Bari mu fara daga nan, nan ne dakinki.’
Tayi murmushi murya kasa-kasa tace ‘Ok.’
Ya wuce ta bishi a baya ya nuna mata ragowar gidan; bayan dakinta sai dakinsa sai kuma dakin yara inda nan ne kuma dakin baki. Sai kuma parlor guda daya da dining area a dai-dai kofar kitchen.
Bayan sun gama zagayawa ya kashe fitulun sannan suka wuce dakinsa inda zasu kwana.
……….
Ranar da Khadija ta cika kwana uku da tarewa a ranar bakin danginsa da suke ta zuwa ganin amarya sun lafa, don tunda gari ya waye babu wanda ya zo har azahar tayi. Suna zaune a parlor suna hirarrakinsu aka fara kiran Sallah, ya mike yana cewa ‘Bari naje masallaci na dawo.’
‘Ok, by then nima nayi sallar nayi serving lunch.’ ta amsa itama tana mikewa.
Tayi masa a dawo lafiya ya fice ita kuma ta shige kitchen.
Kafin ya dawo ta yi Sallah ta gyara kwalliyarta sanna ta jera abincin a kan dininga table. Yana dawowa tayi masa sannu da zuwa sannan ya zauna a dining table ta zuba abinci suka fara ci. Fried rice ne tare da sauce din hanta da salad, daga gefe kuma ga hadadden zobo. Shiru sukayi kowa yana ta kai loma, sai da Mustapha ya kusa cinye abincin nasa sannan ya ajiye cokalinsa ya dauki zobon da ta zuba masa a kofin tangaran ya kora. Yana ajiye kofin ya dauki cokalinsa yana gyara abincin ya dubeta yana cewa ‘Umm! Kin iya girki fa.’
Tayi dariya tace ‘Ai da na zaci santin kurma kake da ka kasa magana.’
'Au ashe ma sa min ido kika yi.’ ya fada yana sake cika baki da abincin.
Tayi dariya itama ta cigaba da cin abincin.
Bayan ya hadiye na bakinsa yace ‘Ina ga ai ya kamata in an jima muje mu debo su Afaf ko? Tun da suka ji an kawoki suke ta zumudi.’
Ta kalleshi tana wasa da cokalinta a kan abincin saboda ta riga ta koshi, tace ‘Babe ai na zata za a barsu sai mun dan huta, kaga shekaran jiya fa na tare. Ko gajiyar biki ma ai ban gama hucewa ba.’
‘Haba, ai sai ku huta tare, kin san suma fa they missed home don tunda mahaifiyarsu ta rasu rabonsu da gida.’
'Allah sarki, ni kaina ina dokin dawowarsu nan but babe please ka bari koda zuwa next week ne na dan gama kwance kayana.’ ta fada da muryar magiya da lallashi.
Ya ture farantin gabansa ya sake cika kofinsa na zobo, ya dan gatsina fuska yace ‘Ok, amma dai ba zasu ji dadi ba. Dazu muka gama waya da su suna ta dokin dawowa wajenki.’
Ya mike ya nufi wajen TV yayinda itama ta mike ta fara tattara kwanukan tana cewa ‘Allah sarki, in sha Allah next week da ni zamu je mu daukosu kaga daga nan ma sai mu biya gaba daya mu gaida Mommy mu gaida su Hajiya sai mu dawo gida.’
'Umm!’ ya amsa yana canza channel din TV.
Ta cigaba da kwashe kwanukan tunani kala-kala yana yawo a kwakwalwarta; ta yi zaton yana dokin kasancewa da ita, ta yanda zai bari su dan kara fahimtar juna kuma su more amarcinsu kafin ya dauko yaran amma shi yana maganar yau. Babu kananan yara a gidansu amma kusan kullum suna tare da yaran Yaya Mama, ta san yara ba zasu bari ta mori amarcinta ba tunda su rayuwarsu suna bukatar kulawa ne kullum. Musamman tunda ga Shukra mai shekaru uku kacal. Sati dayan ma da tace a kara kawai dai daurewa tayi don ita da a tunaninta ta sami kamar wata uku a gidan kafin ya kawo mata yara tunda a can ma inda suke ana kula dasu. To amma bata da wani zabi, zuwa next week din sai ta bishi suje su dauko yaran.
…….
Ana fara kiran magriba yayi alwala ya dauki mukullin motarsa, ya sameta a kitchen tana tsugene a tsakiyar kitchen din tana tuka tuwon shinkafa. Motsinsa ya sa ta saurara da tukin tuwon ta juyo, ta dubeshi tace ‘Fita zaka yi? Ko masallaci zaka je?’
'Eh, daga masallacin zan wuce na dubo yara sai kuma na wuce wajen Hajiya.’
Ta dan langabe kai ‘Babe ai da ka dawo, nima sai na shirya muje na gaida Hajiyan.’
'No ki bari next week zamu je tare.’ Ya amsa yana duba wayarsa.
Ta saki tukin tuwon ta mike ta nufeshi da niyyar ya rungumeshi, sai dai ya dan kauce don haka ta gefe ta rungumoshi. Jikinta ya dan yi sanyi ta sumbaci kumatunsa tace ‘A dawo lafiya Babe, I will wait for you idan ka dawo sai muyi dinner tare. Ka gaida su Hajiya.’
'Ok.' ya amsa sannan ya fice.
.........
A parlor ya sami Daddy, bayan sun gaisa suka dan taba hira. Daddy yace ‘Wai ka debo yaranka kuwa?’
'Ban debo su ba, tace a bari sai zuwa next week idan ta gama hutawa.’ Yana wani kau da kai.
‘To babu laifi; Amma fa idan ka daukosu to ka saka ido, ka san mata yanzu basa son riko. Idan baka yi wasa ba haka za a mayar maka da yara kamar almajirai a gidanka.’
'In sha Allah zan kula, duk da ma na kula kamar bata da muguntar.’
'A'a, basu fa da tabbas, kai dai ka sa ido. Kuma ka dinga bincikar duk motsinsu.’ Ya fada yana nuna shi da yatsa.
Suka dan sake hira sannan ya shiga wajen Hajiya inda ya samesu ita da Yaya Jidda suna hira; da yake ita gidanta kusa da gidan ne wataran ma sai an yi sallar Magriba take zuwa.
Bayan sun gaisa suka cigaba da hirarsu gaba daya. Jimawa kadan Yaya Jidda tace ‘Musty ina amarya? Tsohuwar sirikar taka ta baka yaran ko har yanzun ba zata bayar ba?’
Ya gyara zama yace ‘Haba, sai kace ita ta haifa min su ai dole ta bani su.’
Hajiya tace ‘Sai yaushe zaka dauko su?’