Sashe 31
Mijin Marigayiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar asabar ce kuma tun dare ya sanar da ita da safe yara su shirya zai fita dasu, don haka tun wajen tara na safe ta bayan da suka ci abinci ta sallamesu ta koma ta kwanta. Ya dai ce mata gidan Hajia zasu je kuma suma yaran haka suka gaya mata; amma a ‘yan kwanakin nan yana yawan fita da yaran ranar da babu aiki yace wajen Hajia zai kaisu. Ta riga ta gane wajen Naja yake kaisu, sai dai bata ga dalilin da zai sa tayi masa magana ba tunda ‘yayansa ne sannan kuma gaya musu da yake suce mata gidan Hajia suka je su yake cutarwa ta hanyar koya musu karya.
Gaba dayansu suka fice banda Habib, wanda dama ya riga ya saba duk lokacin da za suyi wannan fitar shi baya binsu. A gida yake zama tare da Khadeejan da Rashida.
Sai wajen karfe biyar na yamma sannan suka dawo, lokacin ta riga ta gamamabincin dare ta zuba a flask tana kwance a daki. A dakinta yaran suka sameta tana kwance tana hutawa, suka sanar da ita sun dawo. Shukra kuwa sai ta wuce ta haye gadon ta kwanta kusa da ita tana cewa ‘Bacci kike yi Anti?’
PAGE 127
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta dan matsa jikinta tana gyara kwanciya, Khadeejan ta dan gyara kwanciyarta tana kawar da Shukran daga cikinta. Tayi dariya tana cewa ‘Na matsa ko Anti, kada na lotsewa kanina hanci.’
Tayi dariya saboda itace ta saba gaya mata hakan a duk lokacin da take son kwanciya a jikinta tunda cikin ya fara girma; domin Shukra yarinya ce mai son jikin tsiya kuma ta samu Khadeejna bata tureta. Tace ‘Yauwa, ashe dai kin gane. Kada a dinga ce miki yayar mai lotsttsen hanci.’
Suka yi dariya gaba daya; Shukra ta ci gaba da wasa da hannun Khadeejan guda daya yayinda Khadeejan take rike da daya waya a daya hannun tana chatting. Jimawa kadan cike da damuwa tace ‘Anti.’
‘Umm.’ Ta amsa ba tare da ta bar abinda take yi ba.
Tace ‘Gaskiya ni ba zan koma wajen Anti Naja ba, a wajenki zan zauna ko?’
Ta ajiye wayar tace ‘To wa yace zaki koma wajen Anti Naja kuma? Ai muna nan tare, ko ba gamu ba a gidanmu.’
Cike da damuwa tace ‘Ai itama tace aurota Abbanmu zai yi ta dawo gidanmu. Amma sai mun koma sabon gida. Shine yau da muka je wajenta take cewa Yaya Afaf idan ta tare duk wajenta zamu koma. Gaskiya ni dai ba zan koma ba ko?’
Ta dan yi shiru tunani yana nema ya birkita kwakwalwarta; duk da bai gaya mata ba ta san yana kai yaransa wajen Naja, amma maganganun da Najan take gayawa yaran basa kama da maganganun da ya dace a gaya musu a daidai wannan lokacin. Sai dai ta san babu yanda zata yi tunda shi ya bata dama.
‘Anti.’ Muryar Shukra ta katseta tana kiran sunanta.
Bayan ta amsa Shukran ta cigaba cikin damuwa ‘Tace saura wata biyu ta tare, gaskiya idan ta zo ki gaya mata ni a wajenki zan zauna ba a wajenta ba. Kuma ma na ji tana gayawa Yaya Afaf idan an koma sabongida sama take so kece a kasa, na gayawa Yaya Afaf mune a sama mu dake tace min wai daAllah can. Gaskiya kia gaya musu mune a sama.’
‘Hmm! Zan fada musu Shukra, ai mune a sama kada ki damu.’
Ta cigaba da surututa tana bawa Khadeeja labarin irin abubuwan da suke yi idan suka je gidan Naja.
PAGE 128
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Duk da Khadeeja bata yi mamakin jin cewa Naja ta san da sabon gida ba amma ta yi mamaki da ta ji cewa har Naja ta zabi part din da take so yainda ita kuma har yanzu bai ma gaya mata ita da wata matar zasu zauna a gidan ba. Ta kasa gane dabarar da Mustapha yake jin yayi da yaki gaya mata zai yi aure; amma dai zata cigaba da binsa taga karshen wulakancinsa. Ko da yake a ‘yan kwanakin nan ma yanda yake kara tubure mata ta tabbatar da tana biye masa da kullum sai sun yi fada. To sai dai bata da wannan lokacin tunda ga project dinta wanda take so ta gama kafin su fara jarrabawa wanda tana fatan Allah ya sa kada haihuwa ta zo mata har sai tayi final paper.
Haka ta ajiye wannan ma a ranta tana jiran ranar da zata titsiye Mustapha tunda haka ya zaba.
……..
Tun kafin su fara jarabawa ya sanar da ita idan ta haihu aka yi suna aka gama zuwa barka zasu koma sabon gida, saboda baya so aje a bata masa gida. Itama tsarin yayi mata don haka ba tare da wata matsala ba ta amsa. Kuma kamar yanda ya bata umarni ta fara hada kayanta da zata tafi da su duk da cewa ya gaya mata ya saka sabbin furniture a gidan.
Ranar da zata yi jarrabawar karshe ya kama yara suna hutun makaranta, kuma sai 2pm zasu shiga paper. Don haka yace idan babu matsala yanaso ta shirya da wuri su tsaya a sabon gida taga furniture din da ya siyo in ya so sai ya ajiyeta a makaranta shi da yara su wuce wajen Hajia. Ta riga ta gama karatunta don haka tun wajen sha daya ta shirya suka shiga mota gaba dayansu suka kama hanya.
Saman gidan yana dauke da parlor guda biyu karami da babba da kuma dakuna guda uku sannan da kitchen, daki daya da parlor suna tare da juna wanda dama ya sanar da ita nan ne nashi part din. Kasan kuma parlor ne guda daya, sai dakuna guda biyu wadanda suke kusa da juna sai kuma wani dakin guda daya wanda yake gafe, sannan kuma da kitchen. Parlor din kasan duk a nan aka sauke furniture din; duk da kusan kowanne yana cikin kwalinsa.
Suna shiga suka dan yayyage kwalin ita da yara suka gani.
PAGE 129
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya dubeta yana nuna dakunan kasan yana cewa ‘Sai ki zabi a wane dakin za a saka miki gadon, in ya so daya dakin kuma sai a dauko gadonki na tsohon gida a saka.’
Ta kama hanyar sama tana cewa ‘Eh hakan ma yayi; dakin wanda yake jikin nakan sai saka min sabon gadon a nan in ya so na kusa da shi sai a gyarwa ‘yan mata na ko? Shi kuma Yaya Habib sai a bashi wannan na kasan.’
Shukrace kawai ta biyota shi yana tsaye a inda yake. Ta dan juyo tana cewa ‘To kazo muje mana ka gani.’
Yayi ‘yar dariya yace ‘Na zata zaki fi son wadannan dakunan na kasa ai, kin ga sun fi girma. Kuma ai ina ga zai fi min privacy ace dakinki yana nan kasa a madadin yana kusa da nawa idan kin yi baki ina jiyoku.’
Tayi dariya tace ‘Haba dai, kuma don nice duk fadin gidan nan sai na rasa wajen sauke baki sai bedroom? Ai dama sama ba wajen saukan baki bane tunda nan kasan ma da parlor. Amma dai can ne dakina, in ya so idan ma baka so yaran su hau sama za a iya barinsu a kasa.’
Shukra tace ‘Gaskiya Abba mune a sama mu da Anti, in ya so ita Anti N…’
Kafin ta karasa Afaf ta katseta cikin daga murya tana cewa ‘To baki ji me Abban yace ba, kasan ya fi girma ne da space.’
Khadeeja tace ‘To mu dai ba ma son kasa, muna sama abin mu.’
Ta ja hannun Shukra suka haye saman.
Habib wanda yake tsaye a kusa da Abban nasu ya dubeshi yace ‘Haba Abba, dama ai sama na Anti Khadija ne.’ Kallon da Abban yayi masa ya sa ya kawar da idonsa da sauri ya waske yana cewa ‘Bari naje na tayasu zabn dakin.’
Haka ya hakura shima ya bisu saman inda khadeeja ta nuna masa dakin da yake jikin nasa tace shi take so, dayan kuma wanda yake gefe daya sai a barwa yara.
Bashi da wata hujja da zai bata a kan hanata daukan dakin sama, kuma har yanzu baya jin ya shirya gaya mata cewa zai kara aure, ya fi so sai ta haihu tukunna saboda kada ma yaji tausayinta idan tace zata tayar masa da hankali. Haka suka gama zagayensu a cikin gidan sannan suka shiga mota suka nufi BUK don su kaita.
PAGE 130
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Har suka isa makarantar bata daina mamakin Mustapha ba; ta kasa gane sai yaushe zai daina yi mata wannan karyar. Kuma ta kasa gane dalilin da yasa yake fifita bukatar Naja da son zuciyarta a kan tata, amma dai haka zata cigaba da biye masa ta ga gudun ruwansa.
………
Kwanansu biyu da gama jarrabawa Khadeeja ta haifi yaronta, don haka ko kwana bata yi a asibiti ba aka wuce da ita gidanta. Sai daga baya aka kawo mata Anti Binta wadda kanwa ce a wajen Mommy. Tun a asibiti Mustapha ya sanar da su ya sakawa yaro suna Muhammad; sunan Baffan Khadeeja. Daga baya Nabila tayi masa lakabi da Hammad.
Nan da nan aka shiga hada-hadar shirya bikin suna; kuma alokacin Mustapha ya sanar da ita idan an yi suna da sati biyu zasu koma sabon gida.
Ranar kwana biyu da haihuwa Mustapha ya sameta a dakinta da daddare, tana zaune a gefen gado da baby a cinyarta tana kallosa tana murmushi. Ya ajiye shopping bag din dake hannunsa sannan ya zauna akusa da ita ya shafa kan baby yace ‘Shikenan kuma kin mayar min da yaro abun kallo kamar wata TV ko?’
Tayi ‘yar dariya tace ‘To ina laifi, ina yaba halittar Allah ne.’
Ya matsar da ledar kusa da ita yana cewa ‘Ga wannan ‘yan office dinmu ne suka bayar a kawowa Baby.’
Ta karba ta dan buda ta leka sannan ta mayar ta ajiye tana cewa ‘Mun gode, Allah ya saka da alkhairi. Ai dole Muhammad ya kawo tukuici tunda an yi masa takwara.’
Gaba dayansu suka fice banda Habib, wanda dama ya riga ya saba duk lokacin da za suyi wannan fitar shi baya binsu. A gida yake zama tare da Khadeejan da Rashida.
Sai wajen karfe biyar na yamma sannan suka dawo, lokacin ta riga ta gamamabincin dare ta zuba a flask tana kwance a daki. A dakinta yaran suka sameta tana kwance tana hutawa, suka sanar da ita sun dawo. Shukra kuwa sai ta wuce ta haye gadon ta kwanta kusa da ita tana cewa ‘Bacci kike yi Anti?’
PAGE 127
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta dan matsa jikinta tana gyara kwanciya, Khadeejan ta dan gyara kwanciyarta tana kawar da Shukran daga cikinta. Tayi dariya tana cewa ‘Na matsa ko Anti, kada na lotsewa kanina hanci.’
Tayi dariya saboda itace ta saba gaya mata hakan a duk lokacin da take son kwanciya a jikinta tunda cikin ya fara girma; domin Shukra yarinya ce mai son jikin tsiya kuma ta samu Khadeejna bata tureta. Tace ‘Yauwa, ashe dai kin gane. Kada a dinga ce miki yayar mai lotsttsen hanci.’
Suka yi dariya gaba daya; Shukra ta ci gaba da wasa da hannun Khadeejan guda daya yayinda Khadeejan take rike da daya waya a daya hannun tana chatting. Jimawa kadan cike da damuwa tace ‘Anti.’
‘Umm.’ Ta amsa ba tare da ta bar abinda take yi ba.
Tace ‘Gaskiya ni ba zan koma wajen Anti Naja ba, a wajenki zan zauna ko?’
Ta ajiye wayar tace ‘To wa yace zaki koma wajen Anti Naja kuma? Ai muna nan tare, ko ba gamu ba a gidanmu.’
Cike da damuwa tace ‘Ai itama tace aurota Abbanmu zai yi ta dawo gidanmu. Amma sai mun koma sabon gida. Shine yau da muka je wajenta take cewa Yaya Afaf idan ta tare duk wajenta zamu koma. Gaskiya ni dai ba zan koma ba ko?’
Ta dan yi shiru tunani yana nema ya birkita kwakwalwarta; duk da bai gaya mata ba ta san yana kai yaransa wajen Naja, amma maganganun da Najan take gayawa yaran basa kama da maganganun da ya dace a gaya musu a daidai wannan lokacin. Sai dai ta san babu yanda zata yi tunda shi ya bata dama.
‘Anti.’ Muryar Shukra ta katseta tana kiran sunanta.
Bayan ta amsa Shukran ta cigaba cikin damuwa ‘Tace saura wata biyu ta tare, gaskiya idan ta zo ki gaya mata ni a wajenki zan zauna ba a wajenta ba. Kuma ma na ji tana gayawa Yaya Afaf idan an koma sabongida sama take so kece a kasa, na gayawa Yaya Afaf mune a sama mu dake tace min wai daAllah can. Gaskiya kia gaya musu mune a sama.’
‘Hmm! Zan fada musu Shukra, ai mune a sama kada ki damu.’
Ta cigaba da surututa tana bawa Khadeeja labarin irin abubuwan da suke yi idan suka je gidan Naja.
PAGE 128
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Duk da Khadeeja bata yi mamakin jin cewa Naja ta san da sabon gida ba amma ta yi mamaki da ta ji cewa har Naja ta zabi part din da take so yainda ita kuma har yanzu bai ma gaya mata ita da wata matar zasu zauna a gidan ba. Ta kasa gane dabarar da Mustapha yake jin yayi da yaki gaya mata zai yi aure; amma dai zata cigaba da binsa taga karshen wulakancinsa. Ko da yake a ‘yan kwanakin nan ma yanda yake kara tubure mata ta tabbatar da tana biye masa da kullum sai sun yi fada. To sai dai bata da wannan lokacin tunda ga project dinta wanda take so ta gama kafin su fara jarrabawa wanda tana fatan Allah ya sa kada haihuwa ta zo mata har sai tayi final paper.
Haka ta ajiye wannan ma a ranta tana jiran ranar da zata titsiye Mustapha tunda haka ya zaba.
……..
Tun kafin su fara jarabawa ya sanar da ita idan ta haihu aka yi suna aka gama zuwa barka zasu koma sabon gida, saboda baya so aje a bata masa gida. Itama tsarin yayi mata don haka ba tare da wata matsala ba ta amsa. Kuma kamar yanda ya bata umarni ta fara hada kayanta da zata tafi da su duk da cewa ya gaya mata ya saka sabbin furniture a gidan.
Ranar da zata yi jarrabawar karshe ya kama yara suna hutun makaranta, kuma sai 2pm zasu shiga paper. Don haka yace idan babu matsala yanaso ta shirya da wuri su tsaya a sabon gida taga furniture din da ya siyo in ya so sai ya ajiyeta a makaranta shi da yara su wuce wajen Hajia. Ta riga ta gama karatunta don haka tun wajen sha daya ta shirya suka shiga mota gaba dayansu suka kama hanya.
Saman gidan yana dauke da parlor guda biyu karami da babba da kuma dakuna guda uku sannan da kitchen, daki daya da parlor suna tare da juna wanda dama ya sanar da ita nan ne nashi part din. Kasan kuma parlor ne guda daya, sai dakuna guda biyu wadanda suke kusa da juna sai kuma wani dakin guda daya wanda yake gafe, sannan kuma da kitchen. Parlor din kasan duk a nan aka sauke furniture din; duk da kusan kowanne yana cikin kwalinsa.
Suna shiga suka dan yayyage kwalin ita da yara suka gani.
PAGE 129
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya dubeta yana nuna dakunan kasan yana cewa ‘Sai ki zabi a wane dakin za a saka miki gadon, in ya so daya dakin kuma sai a dauko gadonki na tsohon gida a saka.’
Ta kama hanyar sama tana cewa ‘Eh hakan ma yayi; dakin wanda yake jikin nakan sai saka min sabon gadon a nan in ya so na kusa da shi sai a gyarwa ‘yan mata na ko? Shi kuma Yaya Habib sai a bashi wannan na kasan.’
Shukrace kawai ta biyota shi yana tsaye a inda yake. Ta dan juyo tana cewa ‘To kazo muje mana ka gani.’
Yayi ‘yar dariya yace ‘Na zata zaki fi son wadannan dakunan na kasa ai, kin ga sun fi girma. Kuma ai ina ga zai fi min privacy ace dakinki yana nan kasa a madadin yana kusa da nawa idan kin yi baki ina jiyoku.’
Tayi dariya tace ‘Haba dai, kuma don nice duk fadin gidan nan sai na rasa wajen sauke baki sai bedroom? Ai dama sama ba wajen saukan baki bane tunda nan kasan ma da parlor. Amma dai can ne dakina, in ya so idan ma baka so yaran su hau sama za a iya barinsu a kasa.’
Shukra tace ‘Gaskiya Abba mune a sama mu da Anti, in ya so ita Anti N…’
Kafin ta karasa Afaf ta katseta cikin daga murya tana cewa ‘To baki ji me Abban yace ba, kasan ya fi girma ne da space.’
Khadeeja tace ‘To mu dai ba ma son kasa, muna sama abin mu.’
Ta ja hannun Shukra suka haye saman.
Habib wanda yake tsaye a kusa da Abban nasu ya dubeshi yace ‘Haba Abba, dama ai sama na Anti Khadija ne.’ Kallon da Abban yayi masa ya sa ya kawar da idonsa da sauri ya waske yana cewa ‘Bari naje na tayasu zabn dakin.’
Haka ya hakura shima ya bisu saman inda khadeeja ta nuna masa dakin da yake jikin nasa tace shi take so, dayan kuma wanda yake gefe daya sai a barwa yara.
Bashi da wata hujja da zai bata a kan hanata daukan dakin sama, kuma har yanzu baya jin ya shirya gaya mata cewa zai kara aure, ya fi so sai ta haihu tukunna saboda kada ma yaji tausayinta idan tace zata tayar masa da hankali. Haka suka gama zagayensu a cikin gidan sannan suka shiga mota suka nufi BUK don su kaita.
PAGE 130
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Har suka isa makarantar bata daina mamakin Mustapha ba; ta kasa gane sai yaushe zai daina yi mata wannan karyar. Kuma ta kasa gane dalilin da yasa yake fifita bukatar Naja da son zuciyarta a kan tata, amma dai haka zata cigaba da biye masa ta ga gudun ruwansa.
………
Kwanansu biyu da gama jarrabawa Khadeeja ta haifi yaronta, don haka ko kwana bata yi a asibiti ba aka wuce da ita gidanta. Sai daga baya aka kawo mata Anti Binta wadda kanwa ce a wajen Mommy. Tun a asibiti Mustapha ya sanar da su ya sakawa yaro suna Muhammad; sunan Baffan Khadeeja. Daga baya Nabila tayi masa lakabi da Hammad.
Nan da nan aka shiga hada-hadar shirya bikin suna; kuma alokacin Mustapha ya sanar da ita idan an yi suna da sati biyu zasu koma sabon gida.
Ranar kwana biyu da haihuwa Mustapha ya sameta a dakinta da daddare, tana zaune a gefen gado da baby a cinyarta tana kallosa tana murmushi. Ya ajiye shopping bag din dake hannunsa sannan ya zauna akusa da ita ya shafa kan baby yace ‘Shikenan kuma kin mayar min da yaro abun kallo kamar wata TV ko?’
Tayi ‘yar dariya tace ‘To ina laifi, ina yaba halittar Allah ne.’
Ya matsar da ledar kusa da ita yana cewa ‘Ga wannan ‘yan office dinmu ne suka bayar a kawowa Baby.’
Ta karba ta dan buda ta leka sannan ta mayar ta ajiye tana cewa ‘Mun gode, Allah ya saka da alkhairi. Ai dole Muhammad ya kawo tukuici tunda an yi masa takwara.’