Sashe 26
Mijin Marigayiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya kalleta cike da takaici; wai wannan wacce irin dakikiyar yarinya ce? Yace ta dafa abincin ma sai kuma ya gaya mata abincin da zata dafa. Kamar zai fice kuma sai ya tsaya yace ‘Ki dafa indomie.’
‘To.’ Ta amsa jikinta na rawa ta juya ta shige store domin dauko indomie.
Yana dawowa parlor din ya jiyo Afaf tana hayaniya da Shukra a kan shiryawa, har ya nufi dakin sai kuma ya fasa ya wuce kofar daki Khadeeja ya kwankwasa kofar a hankali yana cewa ‘Khadija ki bude mana.’
Babu wanda ya bashi amsa don haka ya koma parlor din ya zauna yana jiyo hayaniyar yaran a dakinsu suna shiryawa. Jimawa kadan ya tashi ya nufi dakin inda ya sa hannu ya fara kokarin tayasu shiryawa. Nan da nan suka gama sannan ya tasosu a gaba suka fito inda ya saka su a gaba suka sha shayi da burodi sannan a gurguje Rashida ta zuba musu indmie dinsu a flask ya tasa su a gaba suka fice.
Khadeeja tana jin fitarsu da mota ta fito daga dakin a shirye ta sallami Rashida ta sanar da ita idan ya dawo ta fice ta tafi makota in ya so idan zai fita sai yayi mata magana ta dawo; Haka suka saba tunda Shukra ta shiga makaranta; idan dai ba tare da yara zai fita ba sai dai Rashida ta je makota ta jira idan ya gama zai fita sannan ta dawo ta shiga gidan.
Bayan ta gama sallamar Rashida ta fice ta tafi makaranta.
………
Suna dab da karasawa makarantar aka rufe gate din, gaba daya masu gadi da sauran ma’aikatan suka shige ciki suka rufe kofa; wanda hakan yake nufi babu yaron da zai sake shiga. Ya tsaya ya cije lebe na dan lokaci sannan ya kunna motar suka kama hanyar komawa gida.
Nasreen tace ‘Mun makara, gashi bamu taba makara ba.’
Yace ‘E, kun tsaya kuna ta fada baku shirya da wuri ba.’
Afaf tace ‘Abba Anti bata lafiya ne?’
Ya shafa kansa yana cewa ‘Eh, bata jin dadi.’
PAGE 107
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Suna Shigowa gidan suka tara da Rashida a tsaye a bakin kofa kamar yanda ta saba jiransa, tana ganin su ta bisu suka shige. Shi kuma Abbansu ya karasa kofar dakin Khadeeja ya fara kwankwasawa yana yi yana cewa ‘Khadeeja daAllah ki bude mana.’
Rashida ta fito daga dakin su Afaf tace ‘Antin ta tafi makaranta.’
Ya kalleta da mamaki yace ‘Makaranta? Yaushe?’
‘Bayan kun fita.’
Ya wuce dakinsa ya barta a nan.
To me Khadija take nufi ne? Daga yin abu ta ma ki ta zauna ayi magana tana ta wulakanci, gashi har ta sa yara sun rasa makaranta. Yanzu gashi dole ya fita ya barsu a gidan su kadai abinda baya so. Amma wannan wulakancin na Khadeeja fa ya fara yawa, ta ma ki ta saurareshi gaba daya. Yanzu ya take so ayi?
Haka ya wuce dakinsa ya zauna ya fara kiran wayar Khadeeja amma har ya gaji da kira bata dauka ba. Ya duba lokaci yaga karfe takwas da rabi, gashi yana da meeting karfe tara. Don haka a gurguje ya tashi ya shiga wanka ya shirya. Ko abinci bai tsaya ci ba ya fice ya bar yaran.
……….
Babu wanda ta gayawa yanda suka yi da Mustapha, don ko su Rahma bata cewa komai ba; su kuma da suka kula bata son magana sai kawai suka kyaleta. Haka tayi zamanta a makaranta har wajen karfe biyar na yamma sannan ta kamo hanya ta dawo gidan. Tana shigowa yara suka fara yi mata oyoyo; da murnarta ta amsa sannu da zuwansu kamar yanda ta saba. Ta kalli Afaf tace ‘Bari na je daki na sha magani na huta, kaina ciwo yake yi.’
Ba tare da ta saurari amsarta ba ta shige dakin ta turo kofa.
……….
Sai bayan sallar isha’i sannan ya dawo, lokacin Afaf ta sa Rashida ta dafa musu taliya sun ci abncin dare saboda Khadeeja tace kada wanda ya sake buga mata kofa.
Yana shigowa gidan ita ya fara tambaya suka ce masa tana daki, sai dai ga mamakinsa yana taba kofar ya jita a rufe. Nasreen ce ta sanar da shi cewa tace a dina buga mata kofa bata lafiya. Don haka shima sai kawai ya kyaleta ya cigaba da harkokinsa har sai da yara suka kwanta.
Wajen karfe goma na dare ya sake kwankwasa mata kofar, tayi banza da shi bata ce komai ba. Ya matsa jikin kofar yace ‘Wallahi Khadeeja idan baki bude kofar nan ba zan balla ta.’
PAGE 108
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Tana daga ciki ta dauki ‘yar saman rigar baccina ta saka sanna ta zo ta bude masa kofar tana rike da wayarta tana chatting. Ta koma ciki ta karasa kan gado ta zauna ta mike kafarta ba tare da ta ce masa komai ba. Yana daga tsaye ya kare mata kallo sannan yace ‘Wai wanne irin wulakanci ne wannan kike yi ne Khadeeja? Kin bar min yara sun makara a makaranta kuma kin fice kin bar gida ba tare da wani bayani ba?’
‘To ai ka san dai yau ina da lecture ko?’ ta bashi amsa sannan ta sake mayar da hankali a kan wayarta.
‘To don me baki tashi kin shirya yara ba kuma da kika dawo kika sake rufe kofa kika barsu.’
‘Au wai Najan bata zo ba? Ai na zata tayi musu komai tunda yau itace da aiki.’
Ya cije lebe sannan ya ja dogon tsaki ya fesar da iska saboda yanda Khadeeja take kureshi ‘Na gaya miki babu komai atsakanina da ita sakatariyata ce kawai, don Allah wai me kike so nayi miki ne a kan wannan maganar. Idan kuma don taje makarantar yara ne to kiyi hakuri ba zata sake zuwa ba, babu wata alaka tsakanina da ita dama sai ta office.’
‘Ai naga alama.’ Ta fada ba tare da ta daina kallon wayara ba.
A fusace yace Khadeeja ni nake miki magana kina danna waya ko kallo ban isheki ba?’
Ta ajiye wayar a gefenta ta kalleshi tace ‘Shike nan, na ji duk abinda ka fada.’
‘Please kada ki sake rufe kofar nan, kuma ga yara can sun kwanta da safe ki tashe su da wuri kada su makara.’
‘Ok.’
Har ya juya zai fita ya dan tsaya yace ‘Kuma kin san kema ba a nan kika saba kwana ba.’
‘Ok.’
Ya fice ya barta.
Ta murguda baki kamar yana kallonta tace ‘Dan rainin hankali, baka yi laushi ba tukunna kaje ka dauko Naja ta zo ta dinga yi maka hidimar kai da yaran.’
Yana fita ta zame tayi kwanciyarta sai dai bata rufe kofar ba. Tana jinsa ya dawo dakin ya leka fuskarta tayi kamar bacci take, don haka ya fice ya barta bayan ya kashe mata fitila.
PAGE 109
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Yayi zaton kamar yanda ta amsa masa da daddare zata tashi ta shirya yara, sai dai abinda tayi jiya shi ta sake maimaitawa. Ta saka mukulli ta kulle dakin, ya buga har ya gaji bata bude ba; don haka ba tare da bata lokaci ba ya tsaya a kan yara suka shirya ya kwashesu ya kai su makaranta. Kafin ya dawo ta fice ta bar masa Rashida a gidan. Takaici ne ya sake kamashi; to me Khadeeja ta mayar da shi ne? wannan wane kalar taurin kai ne take yi haka? Kuma me take nufi? Yanzu me take so yayi mata; yaya ma zai yi da ita don gaskiya idan ba so take ya doketa ba bai san me zai yi mata ba.
Haka ya shirya ya fice ya nufi office.
Har ya kusa karasawa office din dabara ta fado masa; ya karkata kan motar ya nufi gidan su Khadeeja. Gara yaje ya kai kararta waje Baffa in ya so su tsawatar mata don shi yanzu idan ba duka ba bai san me take so yayi mata ba. Ya ci sa’a ya sami Baffa yana shirin fita, bayan sun gaisa Baffa yace ‘Lafiya kuke dai na ganka da sassafe ko?’
Nan ya mayar masa da abinda ya faru da kuma yanda Khadeejan take rufe kanta a daki, sai dai ce masa yayi ya rasa Khadeejan ne a waya shiyasa ya tura sakatariyar tasa.
Baffa yayi dariya yace ‘Kishi ne nasu na mata ya motsa, ka san a kan wata macen komai son da matarka take maka to za aji kanku. Kada ka damu bayan Magriba ka daukota ku zo nan. Zan kirawota don ma kada tace zata yi taurin kai.’
‘To Baffa, na gode.’
Yayi musu sallama ya fice yana jin dadin matakin da ya dauka tunda ya san ko babu komai Baffa zai yi mata fada kuma ya san dole ta shiga hayyacinta.
_____
Suna shirin shiga lecture wayarta tayi kara, tana dubawa taga Baffanta ne don haka ta ja da baya ta nemi waje ta amsa. Bayan sun gaisa yace ‘Khadeeja, na cewa Mustapha ku zo bayan magriba ke da shi kin ji ko?’
Tace ‘Um Baffa yau? Wani abu ya faru ne?’
‘Babu abinda ya faru, ku dai zo din.’
‘To Baffa in sha Allahu zamu zo, in ya dawo zan gaya masa.’
‘Kada ki damu na gaya masa ma, yanzu ya bar nan.’
Ta amsa suka yi sallama da Baffa tana dariya, don ta san inda zancen ya dosa, ta gane Mustapha kararta ya kai duk da bata zata haka ba.
Page 110
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta jiyo motsin shigowar Mustapha gidan amma bata yi zaton zai yi saurin tafiya ba, don haka ma ta jira sai da ta gama abinda takeyi tunda ta jiyoshi da Baffa a tsakar gida. Sai dai ga mamakinta ko da ta fito Baffa ta tarar shi kadai, yana shirin shigewa mota tayi sauri ta karasa. Tace ‘Naji kamar kai da Mustapha ne, ko har ya tafi ne?’
Ya tsaya yana rike da murfin mota yana cewa ‘Shine, matar tasa ce ta fara gwada masa tutsun nata shine ya taho kawo kara da sassafe.’
‘Ikon Allah, Khadija Iya-rigima. Me tayi kuma?’
‘To.’ Ta amsa jikinta na rawa ta juya ta shige store domin dauko indomie.
Yana dawowa parlor din ya jiyo Afaf tana hayaniya da Shukra a kan shiryawa, har ya nufi dakin sai kuma ya fasa ya wuce kofar daki Khadeeja ya kwankwasa kofar a hankali yana cewa ‘Khadija ki bude mana.’
Babu wanda ya bashi amsa don haka ya koma parlor din ya zauna yana jiyo hayaniyar yaran a dakinsu suna shiryawa. Jimawa kadan ya tashi ya nufi dakin inda ya sa hannu ya fara kokarin tayasu shiryawa. Nan da nan suka gama sannan ya tasosu a gaba suka fito inda ya saka su a gaba suka sha shayi da burodi sannan a gurguje Rashida ta zuba musu indmie dinsu a flask ya tasa su a gaba suka fice.
Khadeeja tana jin fitarsu da mota ta fito daga dakin a shirye ta sallami Rashida ta sanar da ita idan ya dawo ta fice ta tafi makota in ya so idan zai fita sai yayi mata magana ta dawo; Haka suka saba tunda Shukra ta shiga makaranta; idan dai ba tare da yara zai fita ba sai dai Rashida ta je makota ta jira idan ya gama zai fita sannan ta dawo ta shiga gidan.
Bayan ta gama sallamar Rashida ta fice ta tafi makaranta.
………
Suna dab da karasawa makarantar aka rufe gate din, gaba daya masu gadi da sauran ma’aikatan suka shige ciki suka rufe kofa; wanda hakan yake nufi babu yaron da zai sake shiga. Ya tsaya ya cije lebe na dan lokaci sannan ya kunna motar suka kama hanyar komawa gida.
Nasreen tace ‘Mun makara, gashi bamu taba makara ba.’
Yace ‘E, kun tsaya kuna ta fada baku shirya da wuri ba.’
Afaf tace ‘Abba Anti bata lafiya ne?’
Ya shafa kansa yana cewa ‘Eh, bata jin dadi.’
PAGE 107
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Suna Shigowa gidan suka tara da Rashida a tsaye a bakin kofa kamar yanda ta saba jiransa, tana ganin su ta bisu suka shige. Shi kuma Abbansu ya karasa kofar dakin Khadeeja ya fara kwankwasawa yana yi yana cewa ‘Khadeeja daAllah ki bude mana.’
Rashida ta fito daga dakin su Afaf tace ‘Antin ta tafi makaranta.’
Ya kalleta da mamaki yace ‘Makaranta? Yaushe?’
‘Bayan kun fita.’
Ya wuce dakinsa ya barta a nan.
To me Khadija take nufi ne? Daga yin abu ta ma ki ta zauna ayi magana tana ta wulakanci, gashi har ta sa yara sun rasa makaranta. Yanzu gashi dole ya fita ya barsu a gidan su kadai abinda baya so. Amma wannan wulakancin na Khadeeja fa ya fara yawa, ta ma ki ta saurareshi gaba daya. Yanzu ya take so ayi?
Haka ya wuce dakinsa ya zauna ya fara kiran wayar Khadeeja amma har ya gaji da kira bata dauka ba. Ya duba lokaci yaga karfe takwas da rabi, gashi yana da meeting karfe tara. Don haka a gurguje ya tashi ya shiga wanka ya shirya. Ko abinci bai tsaya ci ba ya fice ya bar yaran.
……….
Babu wanda ta gayawa yanda suka yi da Mustapha, don ko su Rahma bata cewa komai ba; su kuma da suka kula bata son magana sai kawai suka kyaleta. Haka tayi zamanta a makaranta har wajen karfe biyar na yamma sannan ta kamo hanya ta dawo gidan. Tana shigowa yara suka fara yi mata oyoyo; da murnarta ta amsa sannu da zuwansu kamar yanda ta saba. Ta kalli Afaf tace ‘Bari na je daki na sha magani na huta, kaina ciwo yake yi.’
Ba tare da ta saurari amsarta ba ta shige dakin ta turo kofa.
……….
Sai bayan sallar isha’i sannan ya dawo, lokacin Afaf ta sa Rashida ta dafa musu taliya sun ci abncin dare saboda Khadeeja tace kada wanda ya sake buga mata kofa.
Yana shigowa gidan ita ya fara tambaya suka ce masa tana daki, sai dai ga mamakinsa yana taba kofar ya jita a rufe. Nasreen ce ta sanar da shi cewa tace a dina buga mata kofa bata lafiya. Don haka shima sai kawai ya kyaleta ya cigaba da harkokinsa har sai da yara suka kwanta.
Wajen karfe goma na dare ya sake kwankwasa mata kofar, tayi banza da shi bata ce komai ba. Ya matsa jikin kofar yace ‘Wallahi Khadeeja idan baki bude kofar nan ba zan balla ta.’
PAGE 108
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Tana daga ciki ta dauki ‘yar saman rigar baccina ta saka sanna ta zo ta bude masa kofar tana rike da wayarta tana chatting. Ta koma ciki ta karasa kan gado ta zauna ta mike kafarta ba tare da ta ce masa komai ba. Yana daga tsaye ya kare mata kallo sannan yace ‘Wai wanne irin wulakanci ne wannan kike yi ne Khadeeja? Kin bar min yara sun makara a makaranta kuma kin fice kin bar gida ba tare da wani bayani ba?’
‘To ai ka san dai yau ina da lecture ko?’ ta bashi amsa sannan ta sake mayar da hankali a kan wayarta.
‘To don me baki tashi kin shirya yara ba kuma da kika dawo kika sake rufe kofa kika barsu.’
‘Au wai Najan bata zo ba? Ai na zata tayi musu komai tunda yau itace da aiki.’
Ya cije lebe sannan ya ja dogon tsaki ya fesar da iska saboda yanda Khadeeja take kureshi ‘Na gaya miki babu komai atsakanina da ita sakatariyata ce kawai, don Allah wai me kike so nayi miki ne a kan wannan maganar. Idan kuma don taje makarantar yara ne to kiyi hakuri ba zata sake zuwa ba, babu wata alaka tsakanina da ita dama sai ta office.’
‘Ai naga alama.’ Ta fada ba tare da ta daina kallon wayara ba.
A fusace yace Khadeeja ni nake miki magana kina danna waya ko kallo ban isheki ba?’
Ta ajiye wayar a gefenta ta kalleshi tace ‘Shike nan, na ji duk abinda ka fada.’
‘Please kada ki sake rufe kofar nan, kuma ga yara can sun kwanta da safe ki tashe su da wuri kada su makara.’
‘Ok.’
Har ya juya zai fita ya dan tsaya yace ‘Kuma kin san kema ba a nan kika saba kwana ba.’
‘Ok.’
Ya fice ya barta.
Ta murguda baki kamar yana kallonta tace ‘Dan rainin hankali, baka yi laushi ba tukunna kaje ka dauko Naja ta zo ta dinga yi maka hidimar kai da yaran.’
Yana fita ta zame tayi kwanciyarta sai dai bata rufe kofar ba. Tana jinsa ya dawo dakin ya leka fuskarta tayi kamar bacci take, don haka ya fice ya barta bayan ya kashe mata fitila.
PAGE 109
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Yayi zaton kamar yanda ta amsa masa da daddare zata tashi ta shirya yara, sai dai abinda tayi jiya shi ta sake maimaitawa. Ta saka mukulli ta kulle dakin, ya buga har ya gaji bata bude ba; don haka ba tare da bata lokaci ba ya tsaya a kan yara suka shirya ya kwashesu ya kai su makaranta. Kafin ya dawo ta fice ta bar masa Rashida a gidan. Takaici ne ya sake kamashi; to me Khadeeja ta mayar da shi ne? wannan wane kalar taurin kai ne take yi haka? Kuma me take nufi? Yanzu me take so yayi mata; yaya ma zai yi da ita don gaskiya idan ba so take ya doketa ba bai san me zai yi mata ba.
Haka ya shirya ya fice ya nufi office.
Har ya kusa karasawa office din dabara ta fado masa; ya karkata kan motar ya nufi gidan su Khadeeja. Gara yaje ya kai kararta waje Baffa in ya so su tsawatar mata don shi yanzu idan ba duka ba bai san me take so yayi mata ba. Ya ci sa’a ya sami Baffa yana shirin fita, bayan sun gaisa Baffa yace ‘Lafiya kuke dai na ganka da sassafe ko?’
Nan ya mayar masa da abinda ya faru da kuma yanda Khadeejan take rufe kanta a daki, sai dai ce masa yayi ya rasa Khadeejan ne a waya shiyasa ya tura sakatariyar tasa.
Baffa yayi dariya yace ‘Kishi ne nasu na mata ya motsa, ka san a kan wata macen komai son da matarka take maka to za aji kanku. Kada ka damu bayan Magriba ka daukota ku zo nan. Zan kirawota don ma kada tace zata yi taurin kai.’
‘To Baffa, na gode.’
Yayi musu sallama ya fice yana jin dadin matakin da ya dauka tunda ya san ko babu komai Baffa zai yi mata fada kuma ya san dole ta shiga hayyacinta.
_____
Suna shirin shiga lecture wayarta tayi kara, tana dubawa taga Baffanta ne don haka ta ja da baya ta nemi waje ta amsa. Bayan sun gaisa yace ‘Khadeeja, na cewa Mustapha ku zo bayan magriba ke da shi kin ji ko?’
Tace ‘Um Baffa yau? Wani abu ya faru ne?’
‘Babu abinda ya faru, ku dai zo din.’
‘To Baffa in sha Allahu zamu zo, in ya dawo zan gaya masa.’
‘Kada ki damu na gaya masa ma, yanzu ya bar nan.’
Ta amsa suka yi sallama da Baffa tana dariya, don ta san inda zancen ya dosa, ta gane Mustapha kararta ya kai duk da bata zata haka ba.
Page 110
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta jiyo motsin shigowar Mustapha gidan amma bata yi zaton zai yi saurin tafiya ba, don haka ma ta jira sai da ta gama abinda takeyi tunda ta jiyoshi da Baffa a tsakar gida. Sai dai ga mamakinta ko da ta fito Baffa ta tarar shi kadai, yana shirin shigewa mota tayi sauri ta karasa. Tace ‘Naji kamar kai da Mustapha ne, ko har ya tafi ne?’
Ya tsaya yana rike da murfin mota yana cewa ‘Shine, matar tasa ce ta fara gwada masa tutsun nata shine ya taho kawo kara da sassafe.’
‘Ikon Allah, Khadija Iya-rigima. Me tayi kuma?’