Sashe 12
Mijin Marigayiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
………
Tun a daren Anti Iyami ta kirawo Mommy ta sanar da ita halin da ake ciki, sai dai bata gaya mata cewa Khadeejan tace gida zata taho ba. Ta dai sanar da ita cewa tana hannunta idan akwai wani abu zasu ji zuwa wayewar gari.
Tana tsaye aka yiwa Khadeeja wankin ciki sannan aka bata daki, ta saka mata drip da alluranta sannan ta hada mata sahyi mai kauri. Ta sakata a gaba bayan ta shanye sannan ta zuba mata shayi da kwai ta cinye sannan ta ajiye mata saucer da kankana da lemon bawo tace ta shanye kafin a jima.
Ta sha tambayoyi a wajen Anti Iyami wadda take kokarin gane dalilin da yasa Khadeejan take son tafiya gida; sai dai bata sami komai ba don da a tunaninta ko Mustaphan yana abusing dinta ne.
PAGE 48
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
ita kuma ta sanar da ita kawai bata da lafiya ne sannan kuma ga aikin gida da raino wanda yayi mata yawa shi yasa take son ta je gida ta huta.
_______
A gajiye ya shiga gidan wajen karfe tara na dare, yana shiga yaran suka taso da gudu gaba daya tun kafin ya gama rufe kofar motar suba cewa ‘Abba ina Anti Khadeeja?’
Ya dauki shukura ya kana hannun Nasreen yana cewa ‘Tana asibita, likita ya kwantar da ita, amma gobe in sha Allahu zan je na taho da ita.’
Ya tattara su suka shige cikin gidan.
Yana shiga bayan Ummi tayi masa sannu da zuwa ya sallameta ya fito ya rakata sai da ta shiga gida ta kirawo masa babanta yayi godiya sannan ya koma gida. Sai da ya biya sallar Magriba da Isha’I duk da yunwar da yake ji sannan ya zo ya zauna a parlor a gajiya, ya dubi Afaf wadda take kwance tana yin game a tab dinta yace ‘Afaf dauko min flask da kayan shayi.’
Ta mike ta shiga kitchen din, jimawa kadan ta futo dauke da kayan shayin bayan ta ajiye tace Abba babu ruwan zafi a flask ka jira na dafa maka, wanda Anti ta zuba mun sha shayi dashi mu da Ummi.’
‘No, barshi kawai. Dauko min zobo ki kawo min ragowar abincin da kuka ajiye na ci, yunwa nake ji.’
Kafin ta bashi amsa Habib yace ‘Abba ai tun kafin ku fita zobon ya bare a nan, ka manta? Kuma dama shi kenan wanda Anti ta zuba ragowar na jiya ne.’
Kafin yace wani abu Afaf tace ‘Abba babu fa abincin ma sai dai ragowar rice and stew, gaba daya dankalin muka cinye kuma da peppersoup din, amma akwai ragowar watermelon a fridge. Ko na dafa maka indomie?’
Ya kalleta yana shafa kai na dan lokaci, ya ma rasa me zai ce mata sabod yanda gaba daya ya jigata saboda yunwa, coke kawai ya samu a asibiti da wani guntun burodi ya ci. Ya zata zasu rage abincin amma wai duk sun ciye.
Muryar Afaf ce ta katse shi tana cewa ‘Bari kawai na dafa maka indomie din Abba.’
‘No, bari na shiga kitchen din na gani.’ Ya fada yana mikewa tsaye.
Ya dan dauki lokaci yana kallon kitchen din bai ma san ta inda zai fara ba; har ya dauki tukunya zai dafa indomie sai kuma ya tuna ai akwai cereal, don haka ya mayar da tukunyar ya ajiyeta a muhallinta. Ya zuba ruwan zafi a kettle ya jona
PAGE 49
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya zuba ruwan zafi a kettle ya tafasa ya hada cereal, ya ajiye ya fiddo kankana daga fridge ya yanka sannan ya dauko ya dawo parlor din.
Yana zama Shukra ta matso tana dariya ‘Abba zan sha golden morn din.’
Ya bita da kallo da cokali a hannunsa; bata taba bashi takaici ba kamar a wannan lokacin don ya tabbatar sun koshi tunda gashi sun cinye duk wannan uban abincin da Khadeeja ta dafa. Ya dubi Afaf yace ‘Tashi ki dauko cereal, ki hado min da tea flask da komai na hada mata.’
Kafin Afaf ta dawo Nasreen tace ‘Abba nima zan sha.’
Don haka tana kawowa ya sa ta koma ta karo kofi, ya hada musu cereal din su biyun.
Babu wadda ta sha cokali uku a cikinsu, suka tashi suka bar masa a nan. Kafin ya gama cinye nasa abincin duk sun fara gyangyadi don haka ya sa Afaf ta dauko musu kayan baccinsu ya shiryasu bayan ya rakasu sunyi brush sun yi fitsari. Bayan sun kwanta sannan Afaf da Habib suma suka shirya, Afaf ta zauna a gefen gado tayi tsuru-tsuru shima Habib sai ya hau katifarsa ya kwanta yana zare ido.
Yana tsaye daga bakin kofa yace ‘Yaya dai Afaf? Ki kwanta mana, ko akwai wata damuwa ne?’
Ta jijjiga kai tace ‘Kawai tunawa nayi da Mommy, itama muna bacci ta mutu.’
Ya gaji sosai ga kansa yana sarawa, babu abinda zai iya yi musu na lallashi, ya bude baki a gajiye yace ‘In sha Allahu babu abinda zai sami Anti, kuyi addu’a ku kwanta kuyi bacci kawai.’
Halifa shima ya tashi zaune yana share kwalla ‘Wallahi Abba ni ba zan ma iya baccin ba, Allah ya sa dai kada Anti Khadeejan ma ta mutu ta barmu. Har yanzu idan na tuna Mommynmu sai na yi kuka.’
Kafin yayi magana itama Afafa din hawaye ya fara bin fuskarta, ta sunkuyar da kai ta sa masa kuka harda shassheka.
Ji yayi kamar ya dora hannu a ka ya sa ihu; ina ma yaran nana zasu barshi ya huta, yanzu ya zai yi da su? Manyan cikinsu da yake ganin sune ba zasu bashi matsala ba sune suke so su hanashi bacci. Ya karasa ya zauna a kusa da Afaf ya rungumota yana cewa ‘In sha Allahu babu abinda zai sameta, ku daina kuka kuyi mata addu’a Allah ya bata lafiya. Goben nan ma zaku ga an sallamota.’
PAGE 50
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta fara share hawayenta, Habib wanda shima ya taso ya dawo kusa da ita yace ‘Abba to ka kirawo mana ita a waya mu yi mata sannu.’
Ya zaro wayarsa daga aljihu yana cewa ‘To ai da bana son kiranta saboda kar na dameta don an yi mata allurai, ban sani ba ko harda ta bacci a ciki. Amma bari na kirawota sau daya idan ta daga shikenan idan kuma bata daga ba sai mu hakura da safe ma sake kira.’
Ya lalubo lambarta ya danna mata kira, sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ta daga. Murya kasa-kasa tace ‘Hello.’
Yace ‘Hello, Khadeeja ba kiyi bacci ba?’
‘Na dan yi, farkawa dai nayi kuma naji wayar tana ringing. Ai tun dazu aka gama wankin cikin har na dan ci abinci.’
‘Sannu. Wankin cikin ba wahala kenan?’
‘Hmmm! Akwai wahala ba kadan ba, kawai dai da an gama aka bawa mutum maguguna sai ya sami relief.’
‘Sannu. Afaf ce dama ita da Habibi wai ba zasu iya barci ba sai sun yi miki sannu.’
Tayi murmushi mai sauti domin ta ji dadi har cikin ranta, ta tabbatar cewa yaran nan suna kaunarta kuma da zai barta da su komai nasu zai zo da sauki amma shi komai gani yake kamar zata cuce su. Muryar Afaf ce ta katseta bayan da Abbanta ya bata wayar ‘Anti.’
‘Na’am Afaf, ya aka yi ba kiyi bacci ba.’
‘Babu komai Anti, ya jikin naki? Ke ya aka yi bakiyi baccin ba?
Tayi ‘yar dariya tace ‘Yanzu zan yi Afaf, kuma na sami lafiya don likitan ma ya ce gobe za a sallame ni.’
Suka dan taba hira sannan tayi mata sallama ta mikawa Habib wayar. Bayan sun gama gaba daya ya karbi wayar ya katse yayi mata sai da safe. Ya yi musu sai da safe suka kwanta, har zai kashe fitilar Afaf tace ‘Abba kada ka kashe mana fitilar, in an jima ka zo ka kashe.’
Haka ya bar musu fitilar ya fice.
Can bayan awa daya ya gama abinda yake yana so ya kwanta saboda ya gaji ya zo zai kashe musu fitilar, yana kashewa Afaf da Habib suka hada baki a lokaci guda suka ce ‘Abba kada ka kashe fitilar.’
Da mamaki yace ‘Kai! Me kuke baku yi barci ba?’
Afaf tace ‘Abba to ni dai na kasa bacci, da ma zaka taya mu kwana.’
Habib yace ‘Eh wallahi Abba don ni wallahi tsoro nake ji.’
Takaici ya kamashi, to yanzu ya zai yi? Taya su kwanan zai yi ko kuwa barinsu zai yi a haka su
PAGE 51
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Takaici ya kamashi, to yanzu ya zai yi? Taya su kwanan zai yi ko kuwa barinsu zai yi a haka suna zare ido yaje ya kwanta? Wannan wacce irin fitna ce a daren nan gashi ya gaji.
Baya son barinsu su kadai don haka ya wuce dakinsa yaje ya shirya ya rufo gidan sannan ya dawo nan dakin; katifar Habib karama ce ya san ba zata ishesu ba don haka kawai ya gyarawa Nasreen da Shukra kwanciya ya dan sami waje a gefen gadon ya kwanta bayan Khadeeja ta kwanta a daya gefen. Yayi addu’a ya tofa musu sannan yace kowa ya rufe idonsa kada ya sake jin motsinsu.
Tunda ya kwanta yake jin wani dan doyi haka, idan iska ta busa sai ya ji kamar doyin ya buso cikin daki idan iskar ta wuce kuma sai ya daina ji. A haka bai san lokacin da bacci ya daukeshi ba.
‘Subhanallahi!’ ya fada bayan yayi firgigit ya tashi, ya kai hannunsa ya taba inda yake kwance daidai duwawunsa yaji shi a cikin ruwa sosai. Ya daga hannun yana kallo da tsananan mamaki ‘Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un.’ Ya sake fada a fili.
Tun a daren Anti Iyami ta kirawo Mommy ta sanar da ita halin da ake ciki, sai dai bata gaya mata cewa Khadeejan tace gida zata taho ba. Ta dai sanar da ita cewa tana hannunta idan akwai wani abu zasu ji zuwa wayewar gari.
Tana tsaye aka yiwa Khadeeja wankin ciki sannan aka bata daki, ta saka mata drip da alluranta sannan ta hada mata sahyi mai kauri. Ta sakata a gaba bayan ta shanye sannan ta zuba mata shayi da kwai ta cinye sannan ta ajiye mata saucer da kankana da lemon bawo tace ta shanye kafin a jima.
Ta sha tambayoyi a wajen Anti Iyami wadda take kokarin gane dalilin da yasa Khadeejan take son tafiya gida; sai dai bata sami komai ba don da a tunaninta ko Mustaphan yana abusing dinta ne.
PAGE 48
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
ita kuma ta sanar da ita kawai bata da lafiya ne sannan kuma ga aikin gida da raino wanda yayi mata yawa shi yasa take son ta je gida ta huta.
_______
A gajiye ya shiga gidan wajen karfe tara na dare, yana shiga yaran suka taso da gudu gaba daya tun kafin ya gama rufe kofar motar suba cewa ‘Abba ina Anti Khadeeja?’
Ya dauki shukura ya kana hannun Nasreen yana cewa ‘Tana asibita, likita ya kwantar da ita, amma gobe in sha Allahu zan je na taho da ita.’
Ya tattara su suka shige cikin gidan.
Yana shiga bayan Ummi tayi masa sannu da zuwa ya sallameta ya fito ya rakata sai da ta shiga gida ta kirawo masa babanta yayi godiya sannan ya koma gida. Sai da ya biya sallar Magriba da Isha’I duk da yunwar da yake ji sannan ya zo ya zauna a parlor a gajiya, ya dubi Afaf wadda take kwance tana yin game a tab dinta yace ‘Afaf dauko min flask da kayan shayi.’
Ta mike ta shiga kitchen din, jimawa kadan ta futo dauke da kayan shayin bayan ta ajiye tace Abba babu ruwan zafi a flask ka jira na dafa maka, wanda Anti ta zuba mun sha shayi dashi mu da Ummi.’
‘No, barshi kawai. Dauko min zobo ki kawo min ragowar abincin da kuka ajiye na ci, yunwa nake ji.’
Kafin ta bashi amsa Habib yace ‘Abba ai tun kafin ku fita zobon ya bare a nan, ka manta? Kuma dama shi kenan wanda Anti ta zuba ragowar na jiya ne.’
Kafin yace wani abu Afaf tace ‘Abba babu fa abincin ma sai dai ragowar rice and stew, gaba daya dankalin muka cinye kuma da peppersoup din, amma akwai ragowar watermelon a fridge. Ko na dafa maka indomie?’
Ya kalleta yana shafa kai na dan lokaci, ya ma rasa me zai ce mata sabod yanda gaba daya ya jigata saboda yunwa, coke kawai ya samu a asibiti da wani guntun burodi ya ci. Ya zata zasu rage abincin amma wai duk sun ciye.
Muryar Afaf ce ta katse shi tana cewa ‘Bari kawai na dafa maka indomie din Abba.’
‘No, bari na shiga kitchen din na gani.’ Ya fada yana mikewa tsaye.
Ya dan dauki lokaci yana kallon kitchen din bai ma san ta inda zai fara ba; har ya dauki tukunya zai dafa indomie sai kuma ya tuna ai akwai cereal, don haka ya mayar da tukunyar ya ajiyeta a muhallinta. Ya zuba ruwan zafi a kettle ya jona
PAGE 49
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya zuba ruwan zafi a kettle ya tafasa ya hada cereal, ya ajiye ya fiddo kankana daga fridge ya yanka sannan ya dauko ya dawo parlor din.
Yana zama Shukra ta matso tana dariya ‘Abba zan sha golden morn din.’
Ya bita da kallo da cokali a hannunsa; bata taba bashi takaici ba kamar a wannan lokacin don ya tabbatar sun koshi tunda gashi sun cinye duk wannan uban abincin da Khadeeja ta dafa. Ya dubi Afaf yace ‘Tashi ki dauko cereal, ki hado min da tea flask da komai na hada mata.’
Kafin Afaf ta dawo Nasreen tace ‘Abba nima zan sha.’
Don haka tana kawowa ya sa ta koma ta karo kofi, ya hada musu cereal din su biyun.
Babu wadda ta sha cokali uku a cikinsu, suka tashi suka bar masa a nan. Kafin ya gama cinye nasa abincin duk sun fara gyangyadi don haka ya sa Afaf ta dauko musu kayan baccinsu ya shiryasu bayan ya rakasu sunyi brush sun yi fitsari. Bayan sun kwanta sannan Afaf da Habib suma suka shirya, Afaf ta zauna a gefen gado tayi tsuru-tsuru shima Habib sai ya hau katifarsa ya kwanta yana zare ido.
Yana tsaye daga bakin kofa yace ‘Yaya dai Afaf? Ki kwanta mana, ko akwai wata damuwa ne?’
Ta jijjiga kai tace ‘Kawai tunawa nayi da Mommy, itama muna bacci ta mutu.’
Ya gaji sosai ga kansa yana sarawa, babu abinda zai iya yi musu na lallashi, ya bude baki a gajiye yace ‘In sha Allahu babu abinda zai sami Anti, kuyi addu’a ku kwanta kuyi bacci kawai.’
Halifa shima ya tashi zaune yana share kwalla ‘Wallahi Abba ni ba zan ma iya baccin ba, Allah ya sa dai kada Anti Khadeejan ma ta mutu ta barmu. Har yanzu idan na tuna Mommynmu sai na yi kuka.’
Kafin yayi magana itama Afafa din hawaye ya fara bin fuskarta, ta sunkuyar da kai ta sa masa kuka harda shassheka.
Ji yayi kamar ya dora hannu a ka ya sa ihu; ina ma yaran nana zasu barshi ya huta, yanzu ya zai yi da su? Manyan cikinsu da yake ganin sune ba zasu bashi matsala ba sune suke so su hanashi bacci. Ya karasa ya zauna a kusa da Afaf ya rungumota yana cewa ‘In sha Allahu babu abinda zai sameta, ku daina kuka kuyi mata addu’a Allah ya bata lafiya. Goben nan ma zaku ga an sallamota.’
PAGE 50
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta fara share hawayenta, Habib wanda shima ya taso ya dawo kusa da ita yace ‘Abba to ka kirawo mana ita a waya mu yi mata sannu.’
Ya zaro wayarsa daga aljihu yana cewa ‘To ai da bana son kiranta saboda kar na dameta don an yi mata allurai, ban sani ba ko harda ta bacci a ciki. Amma bari na kirawota sau daya idan ta daga shikenan idan kuma bata daga ba sai mu hakura da safe ma sake kira.’
Ya lalubo lambarta ya danna mata kira, sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ta daga. Murya kasa-kasa tace ‘Hello.’
Yace ‘Hello, Khadeeja ba kiyi bacci ba?’
‘Na dan yi, farkawa dai nayi kuma naji wayar tana ringing. Ai tun dazu aka gama wankin cikin har na dan ci abinci.’
‘Sannu. Wankin cikin ba wahala kenan?’
‘Hmmm! Akwai wahala ba kadan ba, kawai dai da an gama aka bawa mutum maguguna sai ya sami relief.’
‘Sannu. Afaf ce dama ita da Habibi wai ba zasu iya barci ba sai sun yi miki sannu.’
Tayi murmushi mai sauti domin ta ji dadi har cikin ranta, ta tabbatar cewa yaran nan suna kaunarta kuma da zai barta da su komai nasu zai zo da sauki amma shi komai gani yake kamar zata cuce su. Muryar Afaf ce ta katseta bayan da Abbanta ya bata wayar ‘Anti.’
‘Na’am Afaf, ya aka yi ba kiyi bacci ba.’
‘Babu komai Anti, ya jikin naki? Ke ya aka yi bakiyi baccin ba?
Tayi ‘yar dariya tace ‘Yanzu zan yi Afaf, kuma na sami lafiya don likitan ma ya ce gobe za a sallame ni.’
Suka dan taba hira sannan tayi mata sallama ta mikawa Habib wayar. Bayan sun gama gaba daya ya karbi wayar ya katse yayi mata sai da safe. Ya yi musu sai da safe suka kwanta, har zai kashe fitilar Afaf tace ‘Abba kada ka kashe mana fitilar, in an jima ka zo ka kashe.’
Haka ya bar musu fitilar ya fice.
Can bayan awa daya ya gama abinda yake yana so ya kwanta saboda ya gaji ya zo zai kashe musu fitilar, yana kashewa Afaf da Habib suka hada baki a lokaci guda suka ce ‘Abba kada ka kashe fitilar.’
Da mamaki yace ‘Kai! Me kuke baku yi barci ba?’
Afaf tace ‘Abba to ni dai na kasa bacci, da ma zaka taya mu kwana.’
Habib yace ‘Eh wallahi Abba don ni wallahi tsoro nake ji.’
Takaici ya kamashi, to yanzu ya zai yi? Taya su kwanan zai yi ko kuwa barinsu zai yi a haka su
PAGE 51
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Takaici ya kamashi, to yanzu ya zai yi? Taya su kwanan zai yi ko kuwa barinsu zai yi a haka suna zare ido yaje ya kwanta? Wannan wacce irin fitna ce a daren nan gashi ya gaji.
Baya son barinsu su kadai don haka ya wuce dakinsa yaje ya shirya ya rufo gidan sannan ya dawo nan dakin; katifar Habib karama ce ya san ba zata ishesu ba don haka kawai ya gyarawa Nasreen da Shukra kwanciya ya dan sami waje a gefen gadon ya kwanta bayan Khadeeja ta kwanta a daya gefen. Yayi addu’a ya tofa musu sannan yace kowa ya rufe idonsa kada ya sake jin motsinsu.
Tunda ya kwanta yake jin wani dan doyi haka, idan iska ta busa sai ya ji kamar doyin ya buso cikin daki idan iskar ta wuce kuma sai ya daina ji. A haka bai san lokacin da bacci ya daukeshi ba.
‘Subhanallahi!’ ya fada bayan yayi firgigit ya tashi, ya kai hannunsa ya taba inda yake kwance daidai duwawunsa yaji shi a cikin ruwa sosai. Ya daga hannun yana kallo da tsananan mamaki ‘Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un.’ Ya sake fada a fili.