Sashe 7
Farautar Mayu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washegari
A asibiti duk muka haɗu,ko kaɗan ban yi ma A'ishah maganar kiranta da ban ɗauka ba hasali ma ban so wata doguwar hira ta haɗa mu.
Ina ƙoƙarin saka wa wata mata tiyon fitsari A'ishah ta matso kusa da ni,ta ce “jiya Mansur na tambayar ki” sai na yi shiru kamar ban ji ta ba,ta sake maimaita min sai na ce “ki jira har mu fita mana,ki duba sauran patients ko akwai wanda ba a yi masa aiki ba ” na yi tunanin na rabu da ita kenan amma mu na fito wa ta sake tara ta da zancen “jiya sai da ya tambaye ni ,sam bai ji daɗi da bai baki kuɗin taxi ba”
Na ce “ba komai ana tare,ki tuna min don Allah zan baki kuɗin anko sai ki sayo min”
“Ok to babu matsala,amma Mansur ya ce min abokansa sun shirya party kin ga ya zama dole a sake fitar da wata ankon ”
“ A'ishah yanzu fa babu kuɗi ba lallai kowa ya iya sayen har anko biyu ba”
“Zan yi masa magana to,ƙila su abokan su saya maku”
“Hum!” kawai na yi,bisanin na ce “wai ita Fatimah ba za ta zo ta kama aiki ba ne?”
“Kanta ke ciwo ta na can baya wurin ƙofar emergency ”
Da sauri na kewaya ta bayan na sameta a kwance kamar ba likita ba.“Fatimah?” na kira sunanta,ta buɗe ido dakyar ta dube ni ai ban san lokacin da na yi zaune ba na ɗauko kanta na ɗora a cinyata.
“Mine ne taƙamaimai abin da ke damun ki?”
Murya na ɗan sarƙe wa ta ce “ A'ishah ce sai hirar mijin da za ta aura take yi min,ni kuma wallahi mugun tsoronsa nake ji.Ban so ko kaɗan ana kiran sunansa” shiru na yi na ɗan wani lokaci bisanin na ce “yaushe kika fara jin tsoron nasa?”
“Jiya”
“Bayan kun dawo daga restaurant ko kuma kafin mu je?”
“Bayan mun dawo” ta ban amsa ta na wani irin tari,na lumshe ido ‘ tabbas zargina ya zama gaskiya.Saurayin A'ishah ba mutumen kirki ba ne,to amma wace iri ce ɓoyayyar fuskarsa? Ban sani ba!’ na faɗa a zuci tare kuma da tunanin mafita.
Can dubara ta faɗo min na ce “Fatimah a Addinin ku ba a sanar da ku yadda ake karye asiri ba?”
“Mi ya kawo zancen Addini kuma?” cewar Fatimah don na santa sarai,ba tun yau take guje duk hirar da za ta kawo banbancin Addinai ba.
“Ke dai ki ban amsa” na sake faɗa,ta ce “eh an sanar da mu mana,gaba ɗaya Alkur'ani waraka ce akan dukkan ko wace matsala”
Ta na gama faɗa min na ce “ok jira ni” sai na sauke kanta kamar yadda na tarar da shi tun farko bisanin na koma can ciki.Direct office ɗin Dr Haleema na nufa,mace ce mai matsayi babba sannan ma'abociyar Addini ga ta kuma da sauƙin kai ba ta hantarar na ƙasa da ita.
A zaune na tarar da ita ta na duba wasu takardu ,da murmushi ta dube ni ta na mai cewa “Ayodele dama ke ce ke buga ƙofa? To zauna”
Na zauna tare da gaisheta bayan ta amsa na ce “Dr don Allah a Musulunce wane abu ne ina nufin addu'a ko kuma magani wanda yake saurin kare asirin da mutum ya ci”
Cike da kulawa ta ce “sanamaki! Ganye ne mai matuƙar amfani wurin kare tasirin asirin da mutum ya ci ,in an tafasa shi sai a yi addu'a cikinsa a sha”
“A ina zan same shi don Allah?”
“Wurin masu sayar da ganye ko kuma Islamique center,mike damun ki Ayodele?”
“Babu komai Dr na gode,jira ina dawo wa”
Ina fito wa daga office ɗinta na je na shiga ɗakinmu inda na aje jakkata,kuɗi na ɗauko sannan na fita bakin hanya.Na samu mai taxi na yi masa bayanin inda zai kai ni,wata cibiyar sayar da maganin musulunci ya kai ni.A can na sayo sanamiki mai kantin ya haɗo min da zuma,sannan na dawo asibiti.
Tun daga nesa nake hangen Dr Jaleel ya na masifa,ina zuwa ya ce “daga ina kike? Wa ya baki izinin fita?”
“Ka yi haƙuri matsala ce ta ujila ” na furta ina mai sunne kai domin yin ladabi.
“Su majinyatan da kika bari fa? In wata matsala ta faru ki sani a bakin aikin ki” nan ya shiga yin min masifa kamar wata ƴarsa kafin yayi gaba.
Office ɗin Dr Haleema na sake komawa na nuna mata ,“Ayodele ki faɗa min abin da ke faruwa mana sannan ba ko wane lokaci ba fa ake shansa”
“Dr Fatimah ce babu lafiya,kuma na tabbata sihiri ne ke ɗawainiya da ita ki taimaka min ki yi min addu'o'in ciki na bata ta sha don ta galabaita sosai” shiru ta yi,bisanin kuma ta ɗauko moɗar ƙarfe wacce take dafa Lipton a ciki, da ita ta yi amfani wurin tafasa Sanamakin bayan nan ta zuba zuma ta shiga yin karatu ciki.Na yi mata godiya na karɓa,inda na bar Fatimah nan na same ta.Dakyar ta iya tashi zaune ta yi Bismillah ta sha,a nan take zufa ta karye mata.Sai ta fara sauke ajiyar zuciya bisanin ta ce “Ayodele cikina na murɗawa toilet zan shiga ” da sauri ta miƙe,na take mata baya har muka isa banɗakin da aka tanada don likitoci.
A wannan wunin tun ina ƙirga adadin da Fatimah ta kewaya har lissafi ya ɓace min, zawayi kawai take mai ɗan uban wari don ko ni da ke tsaye bakin toilet ɗin ina jin warinsa.A ƙarshe dai har ni sai da na shiga toilet ɗin don ta galabaita sosai,idonta tuni sun faɗa ta yi zuru.Ganin an ɗauki sama da minti ashirin ba ta samu wata murɗawar cikin ba,na taimaka mata ta yi wanka sannan mu ka fito.A ɗakinmu ta kwanta,sai a lokacin A'ishah ta san da ciwon yayi tsanani.Ƙarin ruwa na saka mata,bayan ta sha lemu exotic baiwar Allah sai bacci.
A'isha ta tsaya tare da ita ni kuma na fita na hau aiki don kusan ban yi komai ba.Sai ƙarfe tara na dare na nufi ɗakinmu,duk bacci suke.Na taɓa wuyan Fatimah na ji babu zazzaɓi ,na je na haye gado sai bacci.
“Yaanhun! Uhun ! Uhun!” shashekar kuka ta tashe ni daga bacci,na lalubo wayata na duba.Ƙarfe biyu ta gota,na ja tsuki tare da fita na nufi MUTUWARE don tuni ruhina ya lamunta da lamarin da ke faruwa da ni.
Ɓangaren mata na shiga inda ake aje gawa,kwaɗon kawai na taɓa ya buɗe kansa na ja ƙofar na shiga sanyi AC ya ratsa ni sosai bisanin na yi tozali da wata sabuwar gawa don ko wanka ba yi mata ba.Mu na haɗa ido da ita ta bar kukan,a gajiye nake hakan yasa nake jin haushin tashe ni daga baccin da ta yi.
“Sai ki tashi ki faɗa min abin da yasa kika jawo ni izuwa nan” na faɗa ina waige-waige don neman wurin da zan zauna,sai dai ban farga ba na ji wani hannu ya jawo ni da mugun ƙarfi na yi baya tare da faɗa wa cikin akwatin mutuwa.....
Mai son complete book ɗin nan 800 via
2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank
DM +22795045822
[25/04 09:08] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU*
Page 6
Kiciniyar fita daga cikin akwatin gawar na fara sai dai ga mamakina wata gawar na gani a tsaye kan ƙafafunta ta na ƙoƙarin danna ni ciki.Da dukkan alamu akwatinta ne,cikin wata irin murya ta maso duniya take cewa “ki zauna madadina don Allah na ga ke lamarin duniya bai sha maki kai ba,ban shirya zuwa can mazaunar fatale da ruhika ba”
Idona na ware sosai kan matar, datijuwa ce a ƙalla ta kai shekara hamsin da ɗoriya fara ce tasss sai tsagen fuskarta na kurmawanci da ya fito raɗo-raɗo.
Tabon goshina ne na fara jin ya na motsi,kamar almara sai gani na fito daga cikin akwatin na tsaya kan ƙafafuna.
Gawa ta fashe da kuka,cikin tsawa na ce “je ki koma makwancin ki,wato lokacin da malamai ke yi muku wa'azi kar ku biye ma ruɗin duniya ku na yawon dare amma kuka yi kunnen uwar shegu da su kuke fita cikin dare farautar bayin Allah.Yanzu kuma da zanzaro ya tonon gidan Rina gari ya kwaɓe miki za ki neman ki dawo duniyarmu?”
Idonta na zubar da hawaye ta shiga akwati ta kwanta wani haske ya fita daga goshina ya daketa tsit kake ji har esprit ɗin nata ya bar motsi,na maido dubana ga ɗayar wacce ke shashekar kuka na zuba mata Mayun idona masu masifar kaifi na ce “ ke kuma ina jin ki”
Cikin kuka ta fara yi min bayani “wannan da kike gani mahaifiyata ce,ta ja ni izuwa wani ƙauye ne don yin shagali ita da ƙawayenta a can suka nemi da ta bada jinina su sha da ta ƙiya ne hanyarmu ta dawowa mu ka yi hatsari.Kin ga ban mutu ba sun ɗaure ni da azargagi ne,shirinsu shi ne in an kai ni maƙabarta su je su haƙo ni su tsotsen jini”
A ɗan takaitaccen bayaninta na fahimci mahaifiyarta ta na cikin wata ƙungiyar Mayu ce masu shan jini,sannan duk shekara su na gudanar da bikin ƙara danƙon zumunci inda a dole wata za ta bayar da kyautar jini daga cikin ahalinta,kamar ɗa,jika ko ƙane.
Kallon tsaf na yi mata,sai yanzu na lura da goshinta da gefen bakinta duk a fashe suke alamun buguwa.Tunani na fara ta inda zan taimakonta,sai dai na kasa samun mafita don ban san fuskokin masu son kaita ƙasa ba.
“Ki taimaka min kar ki bari a kai ni maƙabarta da raina ban mutu ba sun juyar da hankulan mutane ne kawai ake min kallon gawa ” muryarta ta katse min tunani.
Na ja dogon numfashi bisanin na ce “ki na ji na,a halin yanzu banda mafita amma na yi miki alƙawari zan cece ki ko bayan an haƙa miki kabari ne an saka ki ci to zan zo gare ki”
Fararen idonta ta zuba min uwanda sam ba su da ɗigon baƙin ciki,na jinjina mata kai alamar tabbatar wa kan ƙudirina.Ban sani ba ko ta yarda da ni ɗari bisa ɗari,amma a sannu na ga ruhinta da ke dabaibaye da wasu Kambu ya ɗan samu salama.
Sai da na shafi fuskarta bisanin na fito,direct ɗakinmu na wuce sai na tarar da Fatimah a zaune.
A asibiti duk muka haɗu,ko kaɗan ban yi ma A'ishah maganar kiranta da ban ɗauka ba hasali ma ban so wata doguwar hira ta haɗa mu.
Ina ƙoƙarin saka wa wata mata tiyon fitsari A'ishah ta matso kusa da ni,ta ce “jiya Mansur na tambayar ki” sai na yi shiru kamar ban ji ta ba,ta sake maimaita min sai na ce “ki jira har mu fita mana,ki duba sauran patients ko akwai wanda ba a yi masa aiki ba ” na yi tunanin na rabu da ita kenan amma mu na fito wa ta sake tara ta da zancen “jiya sai da ya tambaye ni ,sam bai ji daɗi da bai baki kuɗin taxi ba”
Na ce “ba komai ana tare,ki tuna min don Allah zan baki kuɗin anko sai ki sayo min”
“Ok to babu matsala,amma Mansur ya ce min abokansa sun shirya party kin ga ya zama dole a sake fitar da wata ankon ”
“ A'ishah yanzu fa babu kuɗi ba lallai kowa ya iya sayen har anko biyu ba”
“Zan yi masa magana to,ƙila su abokan su saya maku”
“Hum!” kawai na yi,bisanin na ce “wai ita Fatimah ba za ta zo ta kama aiki ba ne?”
“Kanta ke ciwo ta na can baya wurin ƙofar emergency ”
Da sauri na kewaya ta bayan na sameta a kwance kamar ba likita ba.“Fatimah?” na kira sunanta,ta buɗe ido dakyar ta dube ni ai ban san lokacin da na yi zaune ba na ɗauko kanta na ɗora a cinyata.
“Mine ne taƙamaimai abin da ke damun ki?”
Murya na ɗan sarƙe wa ta ce “ A'ishah ce sai hirar mijin da za ta aura take yi min,ni kuma wallahi mugun tsoronsa nake ji.Ban so ko kaɗan ana kiran sunansa” shiru na yi na ɗan wani lokaci bisanin na ce “yaushe kika fara jin tsoron nasa?”
“Jiya”
“Bayan kun dawo daga restaurant ko kuma kafin mu je?”
“Bayan mun dawo” ta ban amsa ta na wani irin tari,na lumshe ido ‘ tabbas zargina ya zama gaskiya.Saurayin A'ishah ba mutumen kirki ba ne,to amma wace iri ce ɓoyayyar fuskarsa? Ban sani ba!’ na faɗa a zuci tare kuma da tunanin mafita.
Can dubara ta faɗo min na ce “Fatimah a Addinin ku ba a sanar da ku yadda ake karye asiri ba?”
“Mi ya kawo zancen Addini kuma?” cewar Fatimah don na santa sarai,ba tun yau take guje duk hirar da za ta kawo banbancin Addinai ba.
“Ke dai ki ban amsa” na sake faɗa,ta ce “eh an sanar da mu mana,gaba ɗaya Alkur'ani waraka ce akan dukkan ko wace matsala”
Ta na gama faɗa min na ce “ok jira ni” sai na sauke kanta kamar yadda na tarar da shi tun farko bisanin na koma can ciki.Direct office ɗin Dr Haleema na nufa,mace ce mai matsayi babba sannan ma'abociyar Addini ga ta kuma da sauƙin kai ba ta hantarar na ƙasa da ita.
A zaune na tarar da ita ta na duba wasu takardu ,da murmushi ta dube ni ta na mai cewa “Ayodele dama ke ce ke buga ƙofa? To zauna”
Na zauna tare da gaisheta bayan ta amsa na ce “Dr don Allah a Musulunce wane abu ne ina nufin addu'a ko kuma magani wanda yake saurin kare asirin da mutum ya ci”
Cike da kulawa ta ce “sanamaki! Ganye ne mai matuƙar amfani wurin kare tasirin asirin da mutum ya ci ,in an tafasa shi sai a yi addu'a cikinsa a sha”
“A ina zan same shi don Allah?”
“Wurin masu sayar da ganye ko kuma Islamique center,mike damun ki Ayodele?”
“Babu komai Dr na gode,jira ina dawo wa”
Ina fito wa daga office ɗinta na je na shiga ɗakinmu inda na aje jakkata,kuɗi na ɗauko sannan na fita bakin hanya.Na samu mai taxi na yi masa bayanin inda zai kai ni,wata cibiyar sayar da maganin musulunci ya kai ni.A can na sayo sanamiki mai kantin ya haɗo min da zuma,sannan na dawo asibiti.
Tun daga nesa nake hangen Dr Jaleel ya na masifa,ina zuwa ya ce “daga ina kike? Wa ya baki izinin fita?”
“Ka yi haƙuri matsala ce ta ujila ” na furta ina mai sunne kai domin yin ladabi.
“Su majinyatan da kika bari fa? In wata matsala ta faru ki sani a bakin aikin ki” nan ya shiga yin min masifa kamar wata ƴarsa kafin yayi gaba.
Office ɗin Dr Haleema na sake komawa na nuna mata ,“Ayodele ki faɗa min abin da ke faruwa mana sannan ba ko wane lokaci ba fa ake shansa”
“Dr Fatimah ce babu lafiya,kuma na tabbata sihiri ne ke ɗawainiya da ita ki taimaka min ki yi min addu'o'in ciki na bata ta sha don ta galabaita sosai” shiru ta yi,bisanin kuma ta ɗauko moɗar ƙarfe wacce take dafa Lipton a ciki, da ita ta yi amfani wurin tafasa Sanamakin bayan nan ta zuba zuma ta shiga yin karatu ciki.Na yi mata godiya na karɓa,inda na bar Fatimah nan na same ta.Dakyar ta iya tashi zaune ta yi Bismillah ta sha,a nan take zufa ta karye mata.Sai ta fara sauke ajiyar zuciya bisanin ta ce “Ayodele cikina na murɗawa toilet zan shiga ” da sauri ta miƙe,na take mata baya har muka isa banɗakin da aka tanada don likitoci.
A wannan wunin tun ina ƙirga adadin da Fatimah ta kewaya har lissafi ya ɓace min, zawayi kawai take mai ɗan uban wari don ko ni da ke tsaye bakin toilet ɗin ina jin warinsa.A ƙarshe dai har ni sai da na shiga toilet ɗin don ta galabaita sosai,idonta tuni sun faɗa ta yi zuru.Ganin an ɗauki sama da minti ashirin ba ta samu wata murɗawar cikin ba,na taimaka mata ta yi wanka sannan mu ka fito.A ɗakinmu ta kwanta,sai a lokacin A'ishah ta san da ciwon yayi tsanani.Ƙarin ruwa na saka mata,bayan ta sha lemu exotic baiwar Allah sai bacci.
A'isha ta tsaya tare da ita ni kuma na fita na hau aiki don kusan ban yi komai ba.Sai ƙarfe tara na dare na nufi ɗakinmu,duk bacci suke.Na taɓa wuyan Fatimah na ji babu zazzaɓi ,na je na haye gado sai bacci.
“Yaanhun! Uhun ! Uhun!” shashekar kuka ta tashe ni daga bacci,na lalubo wayata na duba.Ƙarfe biyu ta gota,na ja tsuki tare da fita na nufi MUTUWARE don tuni ruhina ya lamunta da lamarin da ke faruwa da ni.
Ɓangaren mata na shiga inda ake aje gawa,kwaɗon kawai na taɓa ya buɗe kansa na ja ƙofar na shiga sanyi AC ya ratsa ni sosai bisanin na yi tozali da wata sabuwar gawa don ko wanka ba yi mata ba.Mu na haɗa ido da ita ta bar kukan,a gajiye nake hakan yasa nake jin haushin tashe ni daga baccin da ta yi.
“Sai ki tashi ki faɗa min abin da yasa kika jawo ni izuwa nan” na faɗa ina waige-waige don neman wurin da zan zauna,sai dai ban farga ba na ji wani hannu ya jawo ni da mugun ƙarfi na yi baya tare da faɗa wa cikin akwatin mutuwa.....
Mai son complete book ɗin nan 800 via
2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank
DM +22795045822
[25/04 09:08] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU*
Page 6
Kiciniyar fita daga cikin akwatin gawar na fara sai dai ga mamakina wata gawar na gani a tsaye kan ƙafafunta ta na ƙoƙarin danna ni ciki.Da dukkan alamu akwatinta ne,cikin wata irin murya ta maso duniya take cewa “ki zauna madadina don Allah na ga ke lamarin duniya bai sha maki kai ba,ban shirya zuwa can mazaunar fatale da ruhika ba”
Idona na ware sosai kan matar, datijuwa ce a ƙalla ta kai shekara hamsin da ɗoriya fara ce tasss sai tsagen fuskarta na kurmawanci da ya fito raɗo-raɗo.
Tabon goshina ne na fara jin ya na motsi,kamar almara sai gani na fito daga cikin akwatin na tsaya kan ƙafafuna.
Gawa ta fashe da kuka,cikin tsawa na ce “je ki koma makwancin ki,wato lokacin da malamai ke yi muku wa'azi kar ku biye ma ruɗin duniya ku na yawon dare amma kuka yi kunnen uwar shegu da su kuke fita cikin dare farautar bayin Allah.Yanzu kuma da zanzaro ya tonon gidan Rina gari ya kwaɓe miki za ki neman ki dawo duniyarmu?”
Idonta na zubar da hawaye ta shiga akwati ta kwanta wani haske ya fita daga goshina ya daketa tsit kake ji har esprit ɗin nata ya bar motsi,na maido dubana ga ɗayar wacce ke shashekar kuka na zuba mata Mayun idona masu masifar kaifi na ce “ ke kuma ina jin ki”
Cikin kuka ta fara yi min bayani “wannan da kike gani mahaifiyata ce,ta ja ni izuwa wani ƙauye ne don yin shagali ita da ƙawayenta a can suka nemi da ta bada jinina su sha da ta ƙiya ne hanyarmu ta dawowa mu ka yi hatsari.Kin ga ban mutu ba sun ɗaure ni da azargagi ne,shirinsu shi ne in an kai ni maƙabarta su je su haƙo ni su tsotsen jini”
A ɗan takaitaccen bayaninta na fahimci mahaifiyarta ta na cikin wata ƙungiyar Mayu ce masu shan jini,sannan duk shekara su na gudanar da bikin ƙara danƙon zumunci inda a dole wata za ta bayar da kyautar jini daga cikin ahalinta,kamar ɗa,jika ko ƙane.
Kallon tsaf na yi mata,sai yanzu na lura da goshinta da gefen bakinta duk a fashe suke alamun buguwa.Tunani na fara ta inda zan taimakonta,sai dai na kasa samun mafita don ban san fuskokin masu son kaita ƙasa ba.
“Ki taimaka min kar ki bari a kai ni maƙabarta da raina ban mutu ba sun juyar da hankulan mutane ne kawai ake min kallon gawa ” muryarta ta katse min tunani.
Na ja dogon numfashi bisanin na ce “ki na ji na,a halin yanzu banda mafita amma na yi miki alƙawari zan cece ki ko bayan an haƙa miki kabari ne an saka ki ci to zan zo gare ki”
Fararen idonta ta zuba min uwanda sam ba su da ɗigon baƙin ciki,na jinjina mata kai alamar tabbatar wa kan ƙudirina.Ban sani ba ko ta yarda da ni ɗari bisa ɗari,amma a sannu na ga ruhinta da ke dabaibaye da wasu Kambu ya ɗan samu salama.
Sai da na shafi fuskarta bisanin na fito,direct ɗakinmu na wuce sai na tarar da Fatimah a zaune.