Sashe 18
Farautar Mayu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A cikin wannan daren ne na soma karanta littafin tarihi wanda ya ƙunshi rayuwar jarumai da kuma irin gwagwarmayar da suka yi fama a kai.Na samu sirrika dayawa,na yaƙi da kuma yadda ake sarrafa maita ta sigogi daban-daban.
Wannan littafin ya ƙara saka mawa zuciyata cewa duk inda babu magic to lalle babu rayuwa mai inganci, Magic shi ne komai na duniya a cikinsa ne za ka samu ƴanci da kuma gata.Rufe shi na yi tare da raɓawa gefen Debora na kwanta,ina lumshe idona na soma jin wani irin motsi a cikin kunnena tamkar ƙwaro na tafiya.Ƙara nutsuwa na yi sai na soma jin tamkar ana yi mini magana ne,amma ta ina? Ban sani ba.Ji na yi ana danne ni ana saukar mini nauyi,na furzar da huci mai zafi jin wasu kalmomi daga wata murya da ban san mamallakinta ba.
“ A duk inda kike a faɗin duniyar nan sai na nemo ki,ni ne nan zan kashe ki da hannuna ƙaramar matsafiya muguwa mai idanun maciji” muryar namiji ce amma ban san wane ne ba, sannan ban fahimci abin da yake nufi ba har ya ƙara yin wani furucin “ina ma ace annabi sulaiman bai yi wafati ba,da na roƙi alfarmarsa ya tura rundunar aljanu su gana miki azabar da ta fi ƙarfin tsafinki ”
Saurin buɗe idona na yi,ina mai tambayar kaina “wane ne kuma Annabi Sulaiman?” sai dai banda amsar wannan tambayar,in akwai wanda zai faɗa mini ita to bai wuce Deborah ba wannan yasa na kasa haƙuri na kai hannu na shafi fuskarta.Ta buɗe idonta tarau a kaina,sai dai babu ɗigon baƙi a cikinsu da alamu har yanzu ba ta dawo daga balaguron ruhi ba.
“Wane ne Annabi Sulaiman?” na tambaye ta,idanunta ne suka dawo normal nan take ta tashi zaune sannan ta bani amsa da cewa “ ya kasance ɗa ga Annabi Dawuda shi ma kuma annabin Ubangijin Ka'aba ne.Yana da matuƙar power don a tarihin annabawa shi ne kaɗai ya mulki mutane da kuma aljanai,sannan kuma yana iya yin magana da dabbobi da kuma jarirai waɗanda bakinsu bai buɗe ba.Ya yi mulki cikin hikima da adalci ga al'ummarsa”
Zuciyata ce na ji tana wani irin bugawa na jin bayanin da Deborah ta yi mini.Kamar mai tsoron sake jin wata buwayar na ce “amma me Annabin ke nufi?”
“Mutum mai isar da wahayi daga Ubangijin Ka'aba zuwa ga al'umma ” ta bani amsa kai tsaye.Ban ce mata komai ba sai tashi da na yi na fito waje ina kallon taurari ina kuma juya kalamanta.
Ƙofar gidan na ji ana bugawa,na je na buɗe sai na ga gungun matsafan garin ne da alamu sun fito maitar dare ne suka biyo.
“Ranki shi daɗe mun samu baƙuwar fuska a yankin nan,wani mutum ne maharbi mun tsince shi a wata gona yana bacci.Mun ɗaure shi da duk wata igiyar tsafi amma ta ƙi yin tasiri a kansa saboda girman tsafinsa wannan dalilin ne yasa muka zo zuwa gare ki” ɗaya daga cikinsu ya faɗa .
Raina a mugun ɓace na ce “me yasa ba ku kashe shi ba?”
Kallon juna suka yi kafin wani kuma daga cikinsu ya ce “ kamar dai yadda ya faɗa miki ɗin ne,tsafinsa nada matuƙar ƙarfi da dukkan alamu mutum ne na daban ko a duniyar ruhaniya”
Ban ce komai ba na yi gaba a fusace yayin da su kuma suka take mini baya.Tun kafin na isa gonar nake jiyo numfashin baƙin tsafinsa,ina isa ya yi saurin tashi tsaye muna fuskantar juna.Ɗan saurayi ne da ba zai haura shekara ashirin da takwas ba,sanye yake cikin kayan maharba ya rine gefen fuskarsa da baƙin abu yayin da kuma ƙirjinsa aka zana wata baƙar kunama.
Ban tsaya tambayar wane ne shi ba na kai masa farmaki,ya tare kafin kuma mu shiga masayar kalaman tsafi muna haɗawa kuma da yaƙin gangar jiki.Kamar yadda suka faɗa ɗin tabbas shi ɗin na daban ne,ban ida fahimtar haka ba sai da ya kai ni ƙasa ya saita kibiyar tsafinsa daidai idona.
Yana jan wani numfashi ya furta “kafin a farmaki baƙo a fara tambayarsa da wace aniya ya zo,duk waɗannan matakan tsaron na ruhikan ruwa da kika saka ba su iya tare ni na shigo yankin nan ba sai ke ce kike tunanin za ki hana ni yin abin da na zo yi?” shi abin da ya furta,amma duk da haka ban saurare shi ba na fito da wuƙar mahaifina na daɓa masa ita a ƙirji daidai kunamarsa yayi wata irin kururuwa da ta saka dajin amsa wa kafin ƙyafta ido sai ganin kunamu muka yi suna zubowa kamar ana ruwa.....
[28/04 13:15] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐
"""""""""""""""""""""""
LoVe aNd HoRrOr StOry☠️
```MRS SADAUKI```💫✍️
FCWA☀️
____________________________________________
05
Yadda baƙaƙen kunamun suka dabaibaye jikina shi ya fi komai ɗaga mini hankali,ga shi kuma masarafin tsafina ya ƙi aiki.Idona ƙurrr kan mutumin da na cakawa wuƙa yana tsaye ƙyam kan ƙafafunsa,yayin da kuma kunamun suka buɗe hannuwansu da alamu umarninsa suke jira su shiga harbata.
Tafin hannunsa ya buɗe ya soma yin furuci cikin Yaren tsafi wanda ya sha banban da nawa,a hankali duk kunamun suka yi ɓata dabo sai a lokacin na yunƙura na tashi zaune ina kallonsa cike da mamakin me yasa bai kashe ni ba kamar yadda na yi yunƙuri.
“Wane ne kai?” na tambaye shi.Bai bani amsa ba sai nuni da yayi mini da wuƙata wacce har zuwa yanzu tana nitse a cikin ƙirjinsa.A hankali na miƙe tare da zuwa na ciro wuƙar,abin mamaki sam babu ko da ɗigon jini da ya zuba illa kawai alamun an huda ƙirjin.
“Banah!” ya bani amsa,na maimaita sunan a bayyane kafin na ce “me ya kawo ka YANKIN MUTUWA?”
“Ke!” ya bani amsa kai tsaye,kallon ban gane ba na yi masa kafin na ce “ni kuma?”
Kai ya jinjina mini kafin ya ciro wata sarƙa da ke a wuyansa mai tambarin gumki ya miƙo mini,na karɓa tare da juya ta sannan na ɗago na dube shi.
“Ba ki ga komai ba?” ya tambaye ni.
“Me kake son nuna mini?”
“Duba da kyau dai” ya sake faɗa ,sai na nutsu da kyau nan ne na ga gumkin jikin sarƙar zanen mace ne da ƙusumbi a bayanta.
Na shafi ƙusumbin da ɗan yatsana,nan take ya kawo wani haske kamar an kunna ƙwan lantarki.Banah ya matso kusa da ni shi ma ya ɗora nasa yatsan kan nawa sai hasken ya ƙaru a hankali kuma muka fara yin sama ƙafafuwanmu suka bar ƙasa muka lula can cikin iska.
Mutanen gari ne suka fara fitowa,sai kuma suka shiga yin kiɗa da bushe-bushe yayin da wasu kuma suke rawa.Ban taɓa tunanin cewa wai hakan aure ne muka ƙulla ni da Banah ba sai da wasu ruhika suka bayyana a gare mu suka yi mana bushara da hakan tare kuma da ƙara mana power.
Sarƙar nan mai hoton gumkin mace da ƙusumbi ita ce kabancin sadakina,ita Banah ya saka mini a wuya kafin mu sauko ƙasa.
Gefe na koma ina kallonsa,ba mummuna ne ba amma kuma ba za a kira shi da mai kyau ba.A kallon farko za ka tabbatar da cewa shi jarumi ne a fagen tsafi,kumatuna da ya shafa shi ya katse mini ɗan guntun nazarin da nake yi a kansa.
“Tunanin me kike yi?” ya tambaye ni,da sauri na juya masa baya ina mai basa amsa da cewa “ ban san wane ne kai ba,daga ina kake kuma amma kai tsaye ka zo ka aure ni ba tare da neman shawarata ba”
“Naomi ba fa ni ne na tsara haka ba,allolin prophecy suka ga dacewar mu haɗu ni da ke domin mu cika alƙawarin da magabatanmu suka ɗauko”
Da sauri na juyo ina kallonsa na ce “to ka riƙe ni matsayin abokiyar aiki kawai” ina gama faɗar haka na soma tafiya cikin rangaji saboda yanayin larurata.Ina jin yana take mini sawu har muka isa gida,Deborah na tarar a tsaye kamar mai jiran zuwana.
Da ido ta tambaye ni shi kuma wancan na bayana? Na juya na dube shi da sauri ya ƙaraso ya gabatar da kansa ga Deborah sai na ga yanayin fuskarta sam babu annuri.
“Zo ina son yin magana da ke” ta faɗa tare da kama hannuna muka shiga cikin ɗaki.
“Ta ya aka yi ya zama mijinki alhalin tarihi bai nuna za ki yi aure ba a doron duniya?” Deborah ta tambaye ni tana wani tsure ni da ido.
Ni ma ɗin kallonta na tsaya yi saboda gaskiyar da ta fito daga bakinta wacce na san ita kanta ba san ta faɗe ta ba.
“ Ba zan yi aure ba?” na tambaye ta,sai a lokacin kuma na ga ta sha jinin jikinta tare da soma yin kame-kame .
“ Tun yaushe kika gano haka?” na sake jefo mata wata tambayar.
Ta yi ɗan ƙasa da murya tare da sauke idonta daga cikin nawa ta ce “tun ranar da Umma za ta bar garin nan zuwa neman tarihi a wasu guraren , ta shaida mini cewa ba za ki taɓa yin aure ba muddin alamomin prophecy sun bayyana a gare ki.Ita ce da kanta ta nuna mini tsanin nan da ke cikin ruwa,ni kuma na ja ki muka je”
Sosai na ji ɗaci har ƙasan raina jin wai ba zan yi aure ba alhalin a duniyar nan babu abin da na fi so kamar na yi aure na haifi yara.A daidai wannan lokaci ne kuma na ji wani abu game da Banah,ko da a ce auren bogi ne to zan karɓe shi ko ba komai dai za a kira ni sawun ma'aurata kuma zan haifi ƴaƴa.
“Ƙusumbin da ke gare ki ba zai taɓa barin maza su yi sha'awarki ba,in akwai waɗanda da za su so ki to ki sani mata ne ƴan uwanki ” Deborah ta faɗa tare da kamo hannuna alamun rarrashi.
“Wannan furucin naki duk ƙarya ne,kin faɗi haka ne saboda kin jima kina sha'awarta wannan dalili ne ma yasa kika tunzura ta har kika kai ta karɓa muƙamin iko alhalin wa'adin karɓarsa bai yi ba.Kin san cewa muddin Maa nada rai ba za ki taɓa samun Naomi ba” Banah ya faɗa yana mai shigowa ɗakin.
Kallon tsana Deborah ta soma binsa da shi kafin ta ce “muddin ina raye ba zan taɓa bari ka cutar da Nao ba”
Wannan littafin ya ƙara saka mawa zuciyata cewa duk inda babu magic to lalle babu rayuwa mai inganci, Magic shi ne komai na duniya a cikinsa ne za ka samu ƴanci da kuma gata.Rufe shi na yi tare da raɓawa gefen Debora na kwanta,ina lumshe idona na soma jin wani irin motsi a cikin kunnena tamkar ƙwaro na tafiya.Ƙara nutsuwa na yi sai na soma jin tamkar ana yi mini magana ne,amma ta ina? Ban sani ba.Ji na yi ana danne ni ana saukar mini nauyi,na furzar da huci mai zafi jin wasu kalmomi daga wata murya da ban san mamallakinta ba.
“ A duk inda kike a faɗin duniyar nan sai na nemo ki,ni ne nan zan kashe ki da hannuna ƙaramar matsafiya muguwa mai idanun maciji” muryar namiji ce amma ban san wane ne ba, sannan ban fahimci abin da yake nufi ba har ya ƙara yin wani furucin “ina ma ace annabi sulaiman bai yi wafati ba,da na roƙi alfarmarsa ya tura rundunar aljanu su gana miki azabar da ta fi ƙarfin tsafinki ”
Saurin buɗe idona na yi,ina mai tambayar kaina “wane ne kuma Annabi Sulaiman?” sai dai banda amsar wannan tambayar,in akwai wanda zai faɗa mini ita to bai wuce Deborah ba wannan yasa na kasa haƙuri na kai hannu na shafi fuskarta.Ta buɗe idonta tarau a kaina,sai dai babu ɗigon baƙi a cikinsu da alamu har yanzu ba ta dawo daga balaguron ruhi ba.
“Wane ne Annabi Sulaiman?” na tambaye ta,idanunta ne suka dawo normal nan take ta tashi zaune sannan ta bani amsa da cewa “ ya kasance ɗa ga Annabi Dawuda shi ma kuma annabin Ubangijin Ka'aba ne.Yana da matuƙar power don a tarihin annabawa shi ne kaɗai ya mulki mutane da kuma aljanai,sannan kuma yana iya yin magana da dabbobi da kuma jarirai waɗanda bakinsu bai buɗe ba.Ya yi mulki cikin hikima da adalci ga al'ummarsa”
Zuciyata ce na ji tana wani irin bugawa na jin bayanin da Deborah ta yi mini.Kamar mai tsoron sake jin wata buwayar na ce “amma me Annabin ke nufi?”
“Mutum mai isar da wahayi daga Ubangijin Ka'aba zuwa ga al'umma ” ta bani amsa kai tsaye.Ban ce mata komai ba sai tashi da na yi na fito waje ina kallon taurari ina kuma juya kalamanta.
Ƙofar gidan na ji ana bugawa,na je na buɗe sai na ga gungun matsafan garin ne da alamu sun fito maitar dare ne suka biyo.
“Ranki shi daɗe mun samu baƙuwar fuska a yankin nan,wani mutum ne maharbi mun tsince shi a wata gona yana bacci.Mun ɗaure shi da duk wata igiyar tsafi amma ta ƙi yin tasiri a kansa saboda girman tsafinsa wannan dalilin ne yasa muka zo zuwa gare ki” ɗaya daga cikinsu ya faɗa .
Raina a mugun ɓace na ce “me yasa ba ku kashe shi ba?”
Kallon juna suka yi kafin wani kuma daga cikinsu ya ce “ kamar dai yadda ya faɗa miki ɗin ne,tsafinsa nada matuƙar ƙarfi da dukkan alamu mutum ne na daban ko a duniyar ruhaniya”
Ban ce komai ba na yi gaba a fusace yayin da su kuma suka take mini baya.Tun kafin na isa gonar nake jiyo numfashin baƙin tsafinsa,ina isa ya yi saurin tashi tsaye muna fuskantar juna.Ɗan saurayi ne da ba zai haura shekara ashirin da takwas ba,sanye yake cikin kayan maharba ya rine gefen fuskarsa da baƙin abu yayin da kuma ƙirjinsa aka zana wata baƙar kunama.
Ban tsaya tambayar wane ne shi ba na kai masa farmaki,ya tare kafin kuma mu shiga masayar kalaman tsafi muna haɗawa kuma da yaƙin gangar jiki.Kamar yadda suka faɗa ɗin tabbas shi ɗin na daban ne,ban ida fahimtar haka ba sai da ya kai ni ƙasa ya saita kibiyar tsafinsa daidai idona.
Yana jan wani numfashi ya furta “kafin a farmaki baƙo a fara tambayarsa da wace aniya ya zo,duk waɗannan matakan tsaron na ruhikan ruwa da kika saka ba su iya tare ni na shigo yankin nan ba sai ke ce kike tunanin za ki hana ni yin abin da na zo yi?” shi abin da ya furta,amma duk da haka ban saurare shi ba na fito da wuƙar mahaifina na daɓa masa ita a ƙirji daidai kunamarsa yayi wata irin kururuwa da ta saka dajin amsa wa kafin ƙyafta ido sai ganin kunamu muka yi suna zubowa kamar ana ruwa.....
[28/04 13:15] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐
"""""""""""""""""""""""
LoVe aNd HoRrOr StOry☠️
```MRS SADAUKI```💫✍️
FCWA☀️
____________________________________________
05
Yadda baƙaƙen kunamun suka dabaibaye jikina shi ya fi komai ɗaga mini hankali,ga shi kuma masarafin tsafina ya ƙi aiki.Idona ƙurrr kan mutumin da na cakawa wuƙa yana tsaye ƙyam kan ƙafafunsa,yayin da kuma kunamun suka buɗe hannuwansu da alamu umarninsa suke jira su shiga harbata.
Tafin hannunsa ya buɗe ya soma yin furuci cikin Yaren tsafi wanda ya sha banban da nawa,a hankali duk kunamun suka yi ɓata dabo sai a lokacin na yunƙura na tashi zaune ina kallonsa cike da mamakin me yasa bai kashe ni ba kamar yadda na yi yunƙuri.
“Wane ne kai?” na tambaye shi.Bai bani amsa ba sai nuni da yayi mini da wuƙata wacce har zuwa yanzu tana nitse a cikin ƙirjinsa.A hankali na miƙe tare da zuwa na ciro wuƙar,abin mamaki sam babu ko da ɗigon jini da ya zuba illa kawai alamun an huda ƙirjin.
“Banah!” ya bani amsa,na maimaita sunan a bayyane kafin na ce “me ya kawo ka YANKIN MUTUWA?”
“Ke!” ya bani amsa kai tsaye,kallon ban gane ba na yi masa kafin na ce “ni kuma?”
Kai ya jinjina mini kafin ya ciro wata sarƙa da ke a wuyansa mai tambarin gumki ya miƙo mini,na karɓa tare da juya ta sannan na ɗago na dube shi.
“Ba ki ga komai ba?” ya tambaye ni.
“Me kake son nuna mini?”
“Duba da kyau dai” ya sake faɗa ,sai na nutsu da kyau nan ne na ga gumkin jikin sarƙar zanen mace ne da ƙusumbi a bayanta.
Na shafi ƙusumbin da ɗan yatsana,nan take ya kawo wani haske kamar an kunna ƙwan lantarki.Banah ya matso kusa da ni shi ma ya ɗora nasa yatsan kan nawa sai hasken ya ƙaru a hankali kuma muka fara yin sama ƙafafuwanmu suka bar ƙasa muka lula can cikin iska.
Mutanen gari ne suka fara fitowa,sai kuma suka shiga yin kiɗa da bushe-bushe yayin da wasu kuma suke rawa.Ban taɓa tunanin cewa wai hakan aure ne muka ƙulla ni da Banah ba sai da wasu ruhika suka bayyana a gare mu suka yi mana bushara da hakan tare kuma da ƙara mana power.
Sarƙar nan mai hoton gumkin mace da ƙusumbi ita ce kabancin sadakina,ita Banah ya saka mini a wuya kafin mu sauko ƙasa.
Gefe na koma ina kallonsa,ba mummuna ne ba amma kuma ba za a kira shi da mai kyau ba.A kallon farko za ka tabbatar da cewa shi jarumi ne a fagen tsafi,kumatuna da ya shafa shi ya katse mini ɗan guntun nazarin da nake yi a kansa.
“Tunanin me kike yi?” ya tambaye ni,da sauri na juya masa baya ina mai basa amsa da cewa “ ban san wane ne kai ba,daga ina kake kuma amma kai tsaye ka zo ka aure ni ba tare da neman shawarata ba”
“Naomi ba fa ni ne na tsara haka ba,allolin prophecy suka ga dacewar mu haɗu ni da ke domin mu cika alƙawarin da magabatanmu suka ɗauko”
Da sauri na juyo ina kallonsa na ce “to ka riƙe ni matsayin abokiyar aiki kawai” ina gama faɗar haka na soma tafiya cikin rangaji saboda yanayin larurata.Ina jin yana take mini sawu har muka isa gida,Deborah na tarar a tsaye kamar mai jiran zuwana.
Da ido ta tambaye ni shi kuma wancan na bayana? Na juya na dube shi da sauri ya ƙaraso ya gabatar da kansa ga Deborah sai na ga yanayin fuskarta sam babu annuri.
“Zo ina son yin magana da ke” ta faɗa tare da kama hannuna muka shiga cikin ɗaki.
“Ta ya aka yi ya zama mijinki alhalin tarihi bai nuna za ki yi aure ba a doron duniya?” Deborah ta tambaye ni tana wani tsure ni da ido.
Ni ma ɗin kallonta na tsaya yi saboda gaskiyar da ta fito daga bakinta wacce na san ita kanta ba san ta faɗe ta ba.
“ Ba zan yi aure ba?” na tambaye ta,sai a lokacin kuma na ga ta sha jinin jikinta tare da soma yin kame-kame .
“ Tun yaushe kika gano haka?” na sake jefo mata wata tambayar.
Ta yi ɗan ƙasa da murya tare da sauke idonta daga cikin nawa ta ce “tun ranar da Umma za ta bar garin nan zuwa neman tarihi a wasu guraren , ta shaida mini cewa ba za ki taɓa yin aure ba muddin alamomin prophecy sun bayyana a gare ki.Ita ce da kanta ta nuna mini tsanin nan da ke cikin ruwa,ni kuma na ja ki muka je”
Sosai na ji ɗaci har ƙasan raina jin wai ba zan yi aure ba alhalin a duniyar nan babu abin da na fi so kamar na yi aure na haifi yara.A daidai wannan lokaci ne kuma na ji wani abu game da Banah,ko da a ce auren bogi ne to zan karɓe shi ko ba komai dai za a kira ni sawun ma'aurata kuma zan haifi ƴaƴa.
“Ƙusumbin da ke gare ki ba zai taɓa barin maza su yi sha'awarki ba,in akwai waɗanda da za su so ki to ki sani mata ne ƴan uwanki ” Deborah ta faɗa tare da kamo hannuna alamun rarrashi.
“Wannan furucin naki duk ƙarya ne,kin faɗi haka ne saboda kin jima kina sha'awarta wannan dalili ne ma yasa kika tunzura ta har kika kai ta karɓa muƙamin iko alhalin wa'adin karɓarsa bai yi ba.Kin san cewa muddin Maa nada rai ba za ki taɓa samun Naomi ba” Banah ya faɗa yana mai shigowa ɗakin.
Kallon tsana Deborah ta soma binsa da shi kafin ta ce “muddin ina raye ba zan taɓa bari ka cutar da Nao ba”