Sashe 2
Farautar Mayu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kasancewar banda abun hawa yasa na zo bakin titi,dakyar na samu taxi ita ma wata tsohuwa ce.Gidan baya na zauna,mutum uku na taras a ciki hakan yasa duk mu ka matse.
“Mtsw ! ” ta kusa da ni ta ja tsaki a karo na uku,na kasa haƙuri na ce “ya dai?”
Kamar jira take in tanka ta ce “ah toh! Gari yanzu ya lalace ko ina ka je sai ka ji ana zancen Mayu ! Abun baƙin ciki har da yara ƙanana suke kama wa”
Ni kuwa na ce “kuma wallahi in kika bincika kaso casa'in na Mayun garin nan tsofi ne....” ban rufe baki ba motar ta yi wani ƙuuu! Ta tsaya.
“To shikenan kun yi sara da mutum sama sai ku fito!” shi ne abin da mai taxi ɗin ya faɗa ya na mai jan tsuki,sai kuma ya fita.
Ƴan dube-dube ya yi bisanin ya umarci kowa ya fito,duk mu ka sauka sai wani tsoho da ke gaba mai cin goro bakinsa duk yayi ja.
“Ka yi haƙuri ba su san da kai ciki ba ne shi yasa har suka tsokane ka” mai taxi ya faɗa cikin wata irin murya mai rauni.
Kamar wani sarki tsohon nan ya fito tare da tsirtar da yawu abun mamaki sai suka zuba ga jikina da kuma na matar da muke hirar.
Dariyar shaƙiyanci ya fara bisanin ya ce “halan ku baƙi ne a Abengourou? Na ce ku baƙi ne?” kamar wasu ƴaƴansa haka yake mana ihu,tuni wannan matar ta zube ƙasa ta na basa haƙuri.
Raina ne na ji ya ƙara ɓaci,zuciyata ta kawo min wuya.Ban san mi ya shiga kaina ba kawai dai na samu bakina da furta “dara ta ci gida !” sai tsohon ya ɗago da ƙarfi ya na kallona,jikinsa har rawa yake wurin ƙetara wa bakin kwalta ya karɓo ruwan leda ya zo ya fara wanke daidai inda ya tsirta min yawunsa masu ɗauke da jan goro.
Na lumshe ido ina jin zuciyata na ɗan doka wa tare da ƙoƙarin yaƙarta akan tafarfasa da take.
Cikin taxi mu ka koma don kuwa ta tashi,fafur tsohon nan ya ƙi shiga direba sai magiya yake.
Har za mu tafi na ce “ita kuma wannan da ka riƙe?”
Jikinsa na rawa ya ɓallo goro ya bata,na dubeta na yi mata alama da ta karɓa hannunta na rawa ta amsa tare da kai goron baki,mai taxi yayi mata key.
Mun ɗan tafi kaɗan matar ta fara aman baƙin wani abu kamar ranta zai fita,a dole duk mu ka sauka daga taxi ɗin na tari wata sai gida.
“Washhh! Na gaji” shi ne abin da na furta ina mai zube wa kan tabarmar kaba wacce Momah ke zaune ta na gyaran wake.
Wani kallo take bi na da shi wanda yasa na tsargu na ce “Momah ya dai ?”
Sai ta ja wata doguwar ajiyar zuciya ta ce “wa kika tsokana a saman hanya?”
“Da aka yi mi fa?” na tambayeta.
“Idon ki na ga sun canza launi” ta ban amsa.
Na yi ƴar dariya tare da canza zancen “babu ruwan ƙanƙara masu sanyi?”
“Babu sai dai ki sha na tulu,ɗiyar Asabe ta rasu duk can aka saye ƙanƙarar ”
“Wace daga ciki?”
“Zeinab mana! Ai kin san dama ta jima babu lafiya”
Na dafe ƙirji na ce “tun yaushe a ba ta da lafiya? Ban sani ba”
“Eh to ba a fi sati ba! Don a gida aka yi jinyar ta ba kowa ya san da rashin lafiyar ba”
Jiki babu ƙwari na miƙe don sosai mutuwar ta dake ni a kaf faɗin unguwarmu gidansu kawai nake shiga.Ina tafiya sai na ji kamar ana take min baya na waigo sai dai ban ga kowa ba.Ɗaki na shiga na cire kaya,ɗaurin ƙirji na yi na fito na yi wanka.
Bayan na gama na zuba kunu a roba na fara sha kenan wayata ta ɗau ringing,na ɗauka ban kai ga magana ba na ji muryar A'ishah na ce min “Albishirin ki?An kawo kuɗin aurena yanzu haka har an tsayar da ranar buki?” cike da murna na shiga tambayarta “da gaske? A'isha kar fa a ce ƙarya kike min”
“Allah gaske ne! Ki zo Please ”
Na ja dogon numfashi na ce “sai dai zuwa gobe tun da yau akwai inda zan je”
“Ke dalla wacce magana kuma kike? Ko ma ina za ki je ki jingine tafiyar kawai ki zo nan kin ga fa Fatimah nan”
Jin haka yasa na ce “ok gani nan zuwa!” sai ta kashe ,ni kuma na miƙe na je na saka kaya ko mai ban shafa ba na fito na sanar da Momah.
“Masha Allah! Ki dai dawo da wuri kin ga zan shiga gidan mutuwa zuwa biyar na marice”
“To Momah!” na amsa tare da fitowa waje.Cak na tsaya ina kallon yadda unguwar ta ɗauki wani duhu har wani hayaƙi ke tashi.Cike da mamaki sai na ga na ƙofar gidansu Zeinab ya fi yawa,a fili na furta “to! Mi kuma ke faruwa?” kiran A'ishah da ya shigo shi yasa na watsar na nufi bakin titi na samu abun hawa sai gidansu.
Ai kuwa gaskiya ne an kawo lefen ,ina shiga na ta gani mutane masu zuwa yin barka.Bayan na gaishe da Mamarta na wuce ɗakinta,nan mu ka ta yin ihun murna tare da tsara yadda bikin zai kasance.Bayan mun ci abinci ne na yi tambaya “ A'isha wai wane ne za ki aura?”
“Cousin ɗina ne! Dama kin san tun farko ya nuna ya na sona sai kuma abun ya watse tun da ya tafi Lagos to ya dawo shi ne fa aka kawo lefe” ta ban amsa cike da murna.
“Aikin mi yake na ga lefen Masha Allah kamar matar gwamna” cewar Fatimah,na karɓe zancen da “ai kuwa dai! Ko bra da pant kawai abun kallo ne uwa uba sarƙoƙin da na gani har da na zinare”
“Na faɗa maku Lagos ya je wurin diga ya samo kuɗi sosai yanzu haka ya fara kasuwanci!” A'ishah ta faɗa .
“Fatimah saura ke! Ki cewa Nasir ya fito kawai mu sha biki!” na faɗa cikin zolaya,ta kai min dundu a baya ta ce “ Allah kiyaye min ni Dr nake so”
Duk muka fiddo ido waje , A'ishah ta ce “wannan masifaffen? Tabbb! Ayodele kin san kuwa ɗazu da na wuce ta gaban su na ji ya na bai wa Dr Jameela labarin ki wai kin ceci wata su sun yi zaton ta mutu”
Wani irin ras na ji,yayin da kaina ya sara kamar zai tsage.Ba don ace na yi ƙarya ba da zan iya cewa har mahudanar jinina ta sauya tsarin gudu.
Dakyar na iya cewa “bacci ma nake ji bari na kwanta kafin a jima na tafi gida”
“Munafuka yanzu da kika ga lokacin sallah yayi ko?”
Na dubi Fatimah da idona da nake jin tamkar ana yi min masanye bisanin na lumshe su ba tare da na bata amsa ba.Ina jin lokacin da ta ci gaba da cewa “ A'isha ni kuwa lamarin Ayodele na ban tsoro idonta wani sa'in sai su koma kamar na damusa ”
Duniyar da na lula wacce take kusan zahiri ba mafarki ba yasa ban sake jin hirarsu ba.
Ranar da Momah ta zo min da zancen za mu tashi daga unguwar da muke zuwa wannan da muke ciki,ba zan manta a ranar da mu ka dira sai da na kwana da ciwo ƙafa mai tsanani.Maƙociyarmu Asabe ce take shaida mana unguwar Mayu sun yawaita duk da har yanzu ba a san su wane ne ba amma mu tashi tsaye wurin addu'o'i.Na sha daga bisanin na warke,abu guda da kuma ba zan manta ba kusan tsofin unguwarmu ba na shiri da su.
A cikin baccin nan na ja wata ajiyar zuciya ganin Zeinab ta nufo ni idonta shaɓe-shaɓe da hawaye,bayanta kuma tsofin unguwarmu ne ke biye da ita ko wacce daga cikinsu da wuƙa a hannunta.
“Ayodele? Ayodele? Lafiyar ki?” na ji muryar A'ishah wacce ta tashe ni daga bacci,na buɗe ido dakyar bisanin na lumshe su Zeinab ta sake bayyana gare ni sai dai nacin A'ishah ya saka na tashi daga baccin ba don na so ba.
“Haba sai ki tsora mutum! Haka kike bacci dama? Ninshari ne wannan kamar kururuwar damusa a cikin daji” ta faɗi haka ta na mai kallona.
“Ina Fatimah ?” shi ne abin da na tambaye ta.
“Ta tafi gida mana,tashi mu je don Allah ki yi min rakiya daga can sai mu wuce gidan ku” .
Toilet na shiga na wanke fuskata sannan muka wuce gun tela,bayan sun gama tattauna komai muka samu taxi zuwa gidanmu.
Rana tsaka ne wantsar,duk an yi gudu ba za a wuce ƙarfe uku ba.
“Ayodele sallar gawa ce ake yi wai ” cewar A'isha don ta riga ni fita daga taxi,na ziro ƙafata kenan idona yayi tozali da gawar Zeinab wacce maza suka sa a gaba su na sallata.
Gadan-gadan na nufe wurin, A'ishah ta riƙe hannuna daga baya ta na cewa “ina za ki kuma?” na fizge hannuna na je na yi tsaye kusa da makara ina mai ɗaga hannu na ce “ku dakata! Ba ta mutu ba ga ta a zaune ta na faman kuka”
Farin likafanin da aka rufeta na yaye daidai fuskarta,ni kaina ban san mine ne na faɗa ba ko kuma na yi sai Zeinab ta tashi zaune daram da ƙugunta “Allahu Akbar! Allahu Akbar! Allahu Akbar!” maza suka fara yin kabbara kafin wani lokaci har labari ya kai cikin gida.
Sam ban ga tawowar Momah ba sai ganinta na yi a gabana cikin ɓacin rai ta fizgo ni mu ka fito dandazon jama'a,ƙiiii take ja na zuwa gidanmu har mu ka shiga.
Daidai tsakiyar gida ta wani tura ni na faɗi ƙasa,cikin ɓacin rai take cewa “wannan wace irin masifa ce? Gadon tsiya,gadon jaraba! Ayodeleeee!” sai kuma ta yi shiru ta na mai dafe saitin zuciyarta,da azama na miƙe ina mai tare ta don kar ta faɗi sai inaaaa tuni Momah ta rinjaye ni ta faɗi ƙasa warwas....
[24/04 14:49] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU*
3
“Mtsw ! ” ta kusa da ni ta ja tsaki a karo na uku,na kasa haƙuri na ce “ya dai?”
Kamar jira take in tanka ta ce “ah toh! Gari yanzu ya lalace ko ina ka je sai ka ji ana zancen Mayu ! Abun baƙin ciki har da yara ƙanana suke kama wa”
Ni kuwa na ce “kuma wallahi in kika bincika kaso casa'in na Mayun garin nan tsofi ne....” ban rufe baki ba motar ta yi wani ƙuuu! Ta tsaya.
“To shikenan kun yi sara da mutum sama sai ku fito!” shi ne abin da mai taxi ɗin ya faɗa ya na mai jan tsuki,sai kuma ya fita.
Ƴan dube-dube ya yi bisanin ya umarci kowa ya fito,duk mu ka sauka sai wani tsoho da ke gaba mai cin goro bakinsa duk yayi ja.
“Ka yi haƙuri ba su san da kai ciki ba ne shi yasa har suka tsokane ka” mai taxi ya faɗa cikin wata irin murya mai rauni.
Kamar wani sarki tsohon nan ya fito tare da tsirtar da yawu abun mamaki sai suka zuba ga jikina da kuma na matar da muke hirar.
Dariyar shaƙiyanci ya fara bisanin ya ce “halan ku baƙi ne a Abengourou? Na ce ku baƙi ne?” kamar wasu ƴaƴansa haka yake mana ihu,tuni wannan matar ta zube ƙasa ta na basa haƙuri.
Raina ne na ji ya ƙara ɓaci,zuciyata ta kawo min wuya.Ban san mi ya shiga kaina ba kawai dai na samu bakina da furta “dara ta ci gida !” sai tsohon ya ɗago da ƙarfi ya na kallona,jikinsa har rawa yake wurin ƙetara wa bakin kwalta ya karɓo ruwan leda ya zo ya fara wanke daidai inda ya tsirta min yawunsa masu ɗauke da jan goro.
Na lumshe ido ina jin zuciyata na ɗan doka wa tare da ƙoƙarin yaƙarta akan tafarfasa da take.
Cikin taxi mu ka koma don kuwa ta tashi,fafur tsohon nan ya ƙi shiga direba sai magiya yake.
Har za mu tafi na ce “ita kuma wannan da ka riƙe?”
Jikinsa na rawa ya ɓallo goro ya bata,na dubeta na yi mata alama da ta karɓa hannunta na rawa ta amsa tare da kai goron baki,mai taxi yayi mata key.
Mun ɗan tafi kaɗan matar ta fara aman baƙin wani abu kamar ranta zai fita,a dole duk mu ka sauka daga taxi ɗin na tari wata sai gida.
“Washhh! Na gaji” shi ne abin da na furta ina mai zube wa kan tabarmar kaba wacce Momah ke zaune ta na gyaran wake.
Wani kallo take bi na da shi wanda yasa na tsargu na ce “Momah ya dai ?”
Sai ta ja wata doguwar ajiyar zuciya ta ce “wa kika tsokana a saman hanya?”
“Da aka yi mi fa?” na tambayeta.
“Idon ki na ga sun canza launi” ta ban amsa.
Na yi ƴar dariya tare da canza zancen “babu ruwan ƙanƙara masu sanyi?”
“Babu sai dai ki sha na tulu,ɗiyar Asabe ta rasu duk can aka saye ƙanƙarar ”
“Wace daga ciki?”
“Zeinab mana! Ai kin san dama ta jima babu lafiya”
Na dafe ƙirji na ce “tun yaushe a ba ta da lafiya? Ban sani ba”
“Eh to ba a fi sati ba! Don a gida aka yi jinyar ta ba kowa ya san da rashin lafiyar ba”
Jiki babu ƙwari na miƙe don sosai mutuwar ta dake ni a kaf faɗin unguwarmu gidansu kawai nake shiga.Ina tafiya sai na ji kamar ana take min baya na waigo sai dai ban ga kowa ba.Ɗaki na shiga na cire kaya,ɗaurin ƙirji na yi na fito na yi wanka.
Bayan na gama na zuba kunu a roba na fara sha kenan wayata ta ɗau ringing,na ɗauka ban kai ga magana ba na ji muryar A'ishah na ce min “Albishirin ki?An kawo kuɗin aurena yanzu haka har an tsayar da ranar buki?” cike da murna na shiga tambayarta “da gaske? A'isha kar fa a ce ƙarya kike min”
“Allah gaske ne! Ki zo Please ”
Na ja dogon numfashi na ce “sai dai zuwa gobe tun da yau akwai inda zan je”
“Ke dalla wacce magana kuma kike? Ko ma ina za ki je ki jingine tafiyar kawai ki zo nan kin ga fa Fatimah nan”
Jin haka yasa na ce “ok gani nan zuwa!” sai ta kashe ,ni kuma na miƙe na je na saka kaya ko mai ban shafa ba na fito na sanar da Momah.
“Masha Allah! Ki dai dawo da wuri kin ga zan shiga gidan mutuwa zuwa biyar na marice”
“To Momah!” na amsa tare da fitowa waje.Cak na tsaya ina kallon yadda unguwar ta ɗauki wani duhu har wani hayaƙi ke tashi.Cike da mamaki sai na ga na ƙofar gidansu Zeinab ya fi yawa,a fili na furta “to! Mi kuma ke faruwa?” kiran A'ishah da ya shigo shi yasa na watsar na nufi bakin titi na samu abun hawa sai gidansu.
Ai kuwa gaskiya ne an kawo lefen ,ina shiga na ta gani mutane masu zuwa yin barka.Bayan na gaishe da Mamarta na wuce ɗakinta,nan mu ka ta yin ihun murna tare da tsara yadda bikin zai kasance.Bayan mun ci abinci ne na yi tambaya “ A'isha wai wane ne za ki aura?”
“Cousin ɗina ne! Dama kin san tun farko ya nuna ya na sona sai kuma abun ya watse tun da ya tafi Lagos to ya dawo shi ne fa aka kawo lefe” ta ban amsa cike da murna.
“Aikin mi yake na ga lefen Masha Allah kamar matar gwamna” cewar Fatimah,na karɓe zancen da “ai kuwa dai! Ko bra da pant kawai abun kallo ne uwa uba sarƙoƙin da na gani har da na zinare”
“Na faɗa maku Lagos ya je wurin diga ya samo kuɗi sosai yanzu haka ya fara kasuwanci!” A'ishah ta faɗa .
“Fatimah saura ke! Ki cewa Nasir ya fito kawai mu sha biki!” na faɗa cikin zolaya,ta kai min dundu a baya ta ce “ Allah kiyaye min ni Dr nake so”
Duk muka fiddo ido waje , A'ishah ta ce “wannan masifaffen? Tabbb! Ayodele kin san kuwa ɗazu da na wuce ta gaban su na ji ya na bai wa Dr Jameela labarin ki wai kin ceci wata su sun yi zaton ta mutu”
Wani irin ras na ji,yayin da kaina ya sara kamar zai tsage.Ba don ace na yi ƙarya ba da zan iya cewa har mahudanar jinina ta sauya tsarin gudu.
Dakyar na iya cewa “bacci ma nake ji bari na kwanta kafin a jima na tafi gida”
“Munafuka yanzu da kika ga lokacin sallah yayi ko?”
Na dubi Fatimah da idona da nake jin tamkar ana yi min masanye bisanin na lumshe su ba tare da na bata amsa ba.Ina jin lokacin da ta ci gaba da cewa “ A'isha ni kuwa lamarin Ayodele na ban tsoro idonta wani sa'in sai su koma kamar na damusa ”
Duniyar da na lula wacce take kusan zahiri ba mafarki ba yasa ban sake jin hirarsu ba.
Ranar da Momah ta zo min da zancen za mu tashi daga unguwar da muke zuwa wannan da muke ciki,ba zan manta a ranar da mu ka dira sai da na kwana da ciwo ƙafa mai tsanani.Maƙociyarmu Asabe ce take shaida mana unguwar Mayu sun yawaita duk da har yanzu ba a san su wane ne ba amma mu tashi tsaye wurin addu'o'i.Na sha daga bisanin na warke,abu guda da kuma ba zan manta ba kusan tsofin unguwarmu ba na shiri da su.
A cikin baccin nan na ja wata ajiyar zuciya ganin Zeinab ta nufo ni idonta shaɓe-shaɓe da hawaye,bayanta kuma tsofin unguwarmu ne ke biye da ita ko wacce daga cikinsu da wuƙa a hannunta.
“Ayodele? Ayodele? Lafiyar ki?” na ji muryar A'ishah wacce ta tashe ni daga bacci,na buɗe ido dakyar bisanin na lumshe su Zeinab ta sake bayyana gare ni sai dai nacin A'ishah ya saka na tashi daga baccin ba don na so ba.
“Haba sai ki tsora mutum! Haka kike bacci dama? Ninshari ne wannan kamar kururuwar damusa a cikin daji” ta faɗi haka ta na mai kallona.
“Ina Fatimah ?” shi ne abin da na tambaye ta.
“Ta tafi gida mana,tashi mu je don Allah ki yi min rakiya daga can sai mu wuce gidan ku” .
Toilet na shiga na wanke fuskata sannan muka wuce gun tela,bayan sun gama tattauna komai muka samu taxi zuwa gidanmu.
Rana tsaka ne wantsar,duk an yi gudu ba za a wuce ƙarfe uku ba.
“Ayodele sallar gawa ce ake yi wai ” cewar A'isha don ta riga ni fita daga taxi,na ziro ƙafata kenan idona yayi tozali da gawar Zeinab wacce maza suka sa a gaba su na sallata.
Gadan-gadan na nufe wurin, A'ishah ta riƙe hannuna daga baya ta na cewa “ina za ki kuma?” na fizge hannuna na je na yi tsaye kusa da makara ina mai ɗaga hannu na ce “ku dakata! Ba ta mutu ba ga ta a zaune ta na faman kuka”
Farin likafanin da aka rufeta na yaye daidai fuskarta,ni kaina ban san mine ne na faɗa ba ko kuma na yi sai Zeinab ta tashi zaune daram da ƙugunta “Allahu Akbar! Allahu Akbar! Allahu Akbar!” maza suka fara yin kabbara kafin wani lokaci har labari ya kai cikin gida.
Sam ban ga tawowar Momah ba sai ganinta na yi a gabana cikin ɓacin rai ta fizgo ni mu ka fito dandazon jama'a,ƙiiii take ja na zuwa gidanmu har mu ka shiga.
Daidai tsakiyar gida ta wani tura ni na faɗi ƙasa,cikin ɓacin rai take cewa “wannan wace irin masifa ce? Gadon tsiya,gadon jaraba! Ayodeleeee!” sai kuma ta yi shiru ta na mai dafe saitin zuciyarta,da azama na miƙe ina mai tare ta don kar ta faɗi sai inaaaa tuni Momah ta rinjaye ni ta faɗi ƙasa warwas....
[24/04 14:49] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU*
3