Sashe 10
Farautar Mayu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yau saura kwana uku bikin ta,ina ji ta na bai wa Fatimah labari “Oga dai ya matsu a yi aurenmu,kin san a baya ya sha wuya sosai wurin soyayyata yanzu lokaci yayi da zai cika burinsa”
Fatimah ta ce “ai ke ma ga shi sai zumuɗi kike,na matsu mu miƙa ki gidan Mansur ko hankalinmu ya kwanta”
“Ai fa dai na matsu wallahi ”
“Ayodele kin ji yaran zamani ko?” Fatimah ta sako sunana,ina jin lokacin da A'ishah ta ja tsuki.
Ina cika takardu na ajiye na kalle ta na ce “da wa kike?” shiru ta yi ba ta ban amsa,na miƙe a hassale Fatimah ta sha gabana ta na cewa “don Allah ki yi haƙuri! Kin ga dai ba ta ce da ke take ba”
“To da uban wa take?”
“Ba ta dai ce ke ba, A'ishah don Allah tashi ki yi tafiyar ki tun da lokacin tashi yayi” cewar Fatimah,kamar jira take ta ɗauki jakarta ta fice.
Sosai Fatimah ta yi ta danna zuciyata tare da roƙona kan na je bikinta na nuna mata ba komai ba ce duniya,bisanin ita ma ta tafi.
Sai da na gama cika takardu sannan na fito. “Ƴan mata?”
Da mamaki nake kallon shi na ce “kai ne?”
“Eh wallahi na zo wurin abokina,ashe wannan asibitin kike aiki ?”
“Eh! Wurin wa ka zo?”
“Dr Jaleel mana,kin san abokina ne yanzu haka shi nake jira za mu wuce gidana”
“Ok yayi”
“Ba ki faɗa min sunan ki ba,tun ranar nan dai da na rage miki hanya na ji kin burge ni” karon farko da na taɓa jin haka daga namiji,sai abun ya ban dariya ban kai ga magana ba Dr Jaleel ya fito hakan yasa na yi tafiyata.
Tun daga nesa nake tsinkayen yadda mutane suka yi dandazo a ƙofar gidanmu.Gabana tuni ya fara dakan uku-uku,ina iso wa wasu suka fara faɗin “Ga ta nan!” can kusan ƙyauren gidanmu na ga Momah a rakuɓe idonta sun yi ja jawur,kallon mutane kuwa tuni ya dawo kaina......
Mai son complete 800 ne via
2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank
DM +22795045822
[28/04 07:41] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU*
Page 8
Da sauri na nufi Momah ina mai tambayar ta “mi ya faru? Lafiya kike kuka?” ba ta kai ga bani amsa ba na ji an wani jawo ni ta baya ,dakyar na iya miƙe wa kan ƙafafuna na juyo ina fuskantar shi.Namiji ne dattijo wanda ya ba shekara saba'in baya ,shi ne ya jawo ni yayin da sauran tsofin da suka haɗa maza da mata suka yo gaba.
“Yau dai asirin ki ya tonu,shegiyar yarinya ashe mayya ce ke shi ne kika fake da sunan ceto kike.Wancan Kambun maitar da kika rufe shi muke so ki tono kafin Sarkin Mayu ya ƙara so ” ya faɗa ya na mai yin nuni da inda na rufe Kambun Kunkuru.
Banda haske babu abin da wurin yake ,wanda a bayyane yake kowa na ganinsa har da normal mutane.A daidai wannan lokaci ba zan iya yin wani dogon tunani ba ballantana na samo mafita ,duk ma ba wannan ba halin da Momah ke ciki shi ya fi ɗagan hankali.
Tsofin unguwarmu sai zagi ne suke a gaban jama'a, miyagun kalamai wanda duk mai zuciya ba zai iya jura ba.Sosai na yi mamakin dalilin da yasa ban ji sarawar kai ba ,saɓanin sauran lokuta da nake harzuƙa na ɗauki ɓoyayyar fuskata.
A na haka har Sarkin Mayu ya iso,sosai na yi mamaki ganin mutumen nan da muka taɓa haɗuwa cikin taxi.Bayani suka fara yi masa,shi kuma yayi kamar bai taɓa gani na ba tare da umarta ta “je ki haƙo abin da kika ɓoye”
Sai a lokacin na juya na dubi Momah,jiki a sanyayye na duƙa na buɗe ramen tare da ciron Kambun Kunkuru.Haskensa ya ƙara yawaita kan lokacin da yake cikin ƙasa,Sarkin Mayu ya karɓe shi ya na cewa “kin ji kunya ƴar ƙanƙanuwar yarinya da ke amma kin zama muguwa mayya kawai” da mugun sauri na rumtse ido ina jin hawaye na min zuba.
Mutane ne suka fara suratai akan sai mun tashi mun bar masu unguwa,zagi kam ya fi cika buhu babu kalar baƙar maganar da ba a faɗa wa Momah.Ita kuka ni kuka,Sarkin Mayu ya ƙara ɗaukar magana inda yake cewa “na baku nan da awa ɗaya kacal ku tashi ku bar nan ko kuma na sa a ƙone ku da ranku”
Jama'a suka ɗau ihu,da mugun sauri Momah ta shiga gida na take mata baya.A ɗaki na tarar da ita ta na gangamar kaya,rasa abin da zan ce mata na yi kawai sai na faɗa jikinta ina kuka.
“Kukan mi kike? Ina ce ke kika saya mana wulaƙancin da kuɗin ki,tun ranar da kika zo da abin nan sai da na ce ki mayar mai shi abinsa amma kika yi kunnen uwar shegu da ni” ta ida faɗa ta na mai ture ni na yi baya.
Daga inda nake ina jiyo hargowar mutane sai juya suke mana cikin gida tare da zaginmu.Cikin ƙanƙanen lokaci Momah ta haɗa kayanmu,dakyar da siɗin goshi muka samu mu ka isa bakin hanya.Ɗaiɗaikun mutane ne kawai ke tausaya mana,ciki kuwa har da Asabe don a gidanta ma Momah ta kai ajiyar sauran kaya.
A wannan wunin mu ka bazama neman haya sai dai kamar abun tsiya ba mu samu ba,sai a wata unguwa mai ƙarancin mutane kamar za a fita gari shi ma ɗaki ne ciki guda.A haka dai mu ka share mu ka zauna bayan Momah ta kwaso sauran kayanmu.
★
Komai na ta tafiya cikin tsari, musamman bikin da ya kasance tuwona maina ne.Amayar da angon duk ƴan uwa ne,sosai abun ya tafi cikin tsari. A'ishah sai rawar kai take,abokanta kuwa duk sun haɗu wurin kanmu . Fatimah kuwa sai ƙoƙarin kiran Ayodele take a waya saboda rabonta da ita wajen kwana biyu wayarta ma ba ta shiga,cikin wannan zullumi dai ta yi shagalin bikin.
Ranar ɗaurin aure tamkar babu gobe haka aka yi abun hauka musamman ɓangaren Mansur da yake taƙama da Nera.Motocin ɗaukar amarya kaf ɗinsu babu tsohuwa sun jeru rasss sai wacce ranka ya yi ma za ka shiga.A haka aka miƙa A'isha tamfatsetsen gidan mai kama da aljannar duniya,duk yadda ta so Fatimah ta tsaya fafur ta ƙi don dama kan babur ɗinta ta je ko kaɗan ba ta saki jiki da abokan Mansur ba don ƴan magana kan ce sai hali ya zo ɗaya ake abota.
Bayan kowa ya watse Mansur ya shigo tare da abokansa.Kallo ɗaya za ka yi wa gizner jikinsu ka ga Nera ce ke magana,suratansu suka fara ita dai A'ishah ta na rakuɓe sai da suka matsa mata ne ta ɗan ɗage mayafinta.Amanar abokinsu suka bata bisanin yayi masu rakiya ya dawo shi ɗaya.
“Ki sauko mu ci abinci mana” ya faɗa ya na mai jawo hannunta,cike da mamaki A'isha ta bisa har suka baje kan capet.Ta sha ji daga abokaina abu na farko da ake yi in an kai amarya sallah ce domin nuna godiya ga Ubangiji,amma sai ta yi masa uzuri da tunanin ko yunwa yake ji shi yasa.Ba ta kai ƙarshen mamakinta ba sai bayan da suka cika tumbinansu Mansur ya fara aika mata saƙonnin soyayya har ya kai da ya kusanceta,ko Bismillah ba ta ji yayi ba ballantana wai addu'a.
Washegari
Tsabar gajiya da ta yi ya saka ta rasa sallar asubah,hasken rana ne ya daki fuskarta ya sa ta yunƙura ta tashi zaune ta na kallon window.Gefenta kuwa Mansur ne ke ta sharar baccinsa,ta kai hannu ta na jijiga shi “Ogana ka tashi ka kai ni toilet ka min wanka please ba zan iya tashi ba” a shagwaɓe take fitar da harufan har ta ci nasarar tayar da shi.
Ya buɗe idonsa ya zuba mata su ,iya kallon da watsa mata kaɗai sai da gabanta ya faɗi.
“Mine ne?”
“Wanka za min ”
“Can a gidanku wa ke yi miki?”
Ras gaban A'isha ya faɗi jin furucinsa sun yi hannun riga da wanda ya sha faɗa mata satin aurensu.
Dakyar ta ƙoƙarta ta je ta yi wanka ta zo ta gabatar da sallah.Ta na nan zauna har Mansur ya tashi daga bacci,direct wurin drower ya wuce ya fitar da kaya masu kyau ya saka.
“Ka manta ba ka yi wanka ba fa ” ta faɗa ganin bilhaƙi yake shirin,“uban waye ya faɗa miki manta wa na yi?” Mansur ya faɗa a zafafe ya na kallonta.
“Ka yi haƙuri ”shi ne kawai abin da ta iya furta wa.
“Ki tashi ki ɗora min breakfast!” ya faɗa ya na mai fesa turare.
“To” ta amsa tare da tashi.Tsabar takaici sai da ta zubar da hawaye ,amma a haka ta haɗa masa frite da gasashen kifi don ta ga kusan akwai komai.
Kan table ɗin cin abinci ta ajiye bisanin ta wuce bedroom,waya ta tarar da shi ya na yi sai magana yake cikin ladabi.Da ace mahaifinsa na da rai da to babu shakka za ta ce da shi ne yake waya.
Bayan ya gama ne ya zo ya rungume ta tare da cewa “har kin gama?” kai ta jinjina masa,“ok mu je”
Falo suka koma a tare suka ci abincin, Mansur na yi mata hirar soyayya hakan ya kuma ƙulle mata kai.
“Zan tafi wurin aiki,tun ɗazu shugaba ke jirana” ya faɗa tare da miƙe wa tsaye.
“Aiki kuma? A cikin satin aurenmu?”
“To sai aka yi mi? Kin ga ban so sakarci sai na dawo” ya na gama faɗa ya fice. A'isha ta zube kan salon ta na jin wata irin damuwa na dabaibaye ta,tun kafin aje ko ina auren Mansur ya fice mata a rai.“Babu wankan janaba ballantana a yi maganar sallah anya kuwa na auru? Mine ne ma ya hana shi ko fuska da baki ya wanke?” ta furta hawayen takaici na zubo mata bisanin ta ɓingire bacci.
Hayaniyar ƙawayenta ce ta tashe ta,sosai ta yi murnar zuwan su.Sauran kazar jiya ta ɗauko masu kafin a hau hira da girke-girke cike da nishaɗin ƙawarsu ta auri mai kuɗi kowacce ta sasaɓe zane ta ci abubuwa na kayan daɗi ta ƙoshi da za a tafi gida kuwa har da yin tsaraba.
AYODELE
Fatimah ta ce “ai ke ma ga shi sai zumuɗi kike,na matsu mu miƙa ki gidan Mansur ko hankalinmu ya kwanta”
“Ai fa dai na matsu wallahi ”
“Ayodele kin ji yaran zamani ko?” Fatimah ta sako sunana,ina jin lokacin da A'ishah ta ja tsuki.
Ina cika takardu na ajiye na kalle ta na ce “da wa kike?” shiru ta yi ba ta ban amsa,na miƙe a hassale Fatimah ta sha gabana ta na cewa “don Allah ki yi haƙuri! Kin ga dai ba ta ce da ke take ba”
“To da uban wa take?”
“Ba ta dai ce ke ba, A'ishah don Allah tashi ki yi tafiyar ki tun da lokacin tashi yayi” cewar Fatimah,kamar jira take ta ɗauki jakarta ta fice.
Sosai Fatimah ta yi ta danna zuciyata tare da roƙona kan na je bikinta na nuna mata ba komai ba ce duniya,bisanin ita ma ta tafi.
Sai da na gama cika takardu sannan na fito. “Ƴan mata?”
Da mamaki nake kallon shi na ce “kai ne?”
“Eh wallahi na zo wurin abokina,ashe wannan asibitin kike aiki ?”
“Eh! Wurin wa ka zo?”
“Dr Jaleel mana,kin san abokina ne yanzu haka shi nake jira za mu wuce gidana”
“Ok yayi”
“Ba ki faɗa min sunan ki ba,tun ranar nan dai da na rage miki hanya na ji kin burge ni” karon farko da na taɓa jin haka daga namiji,sai abun ya ban dariya ban kai ga magana ba Dr Jaleel ya fito hakan yasa na yi tafiyata.
Tun daga nesa nake tsinkayen yadda mutane suka yi dandazo a ƙofar gidanmu.Gabana tuni ya fara dakan uku-uku,ina iso wa wasu suka fara faɗin “Ga ta nan!” can kusan ƙyauren gidanmu na ga Momah a rakuɓe idonta sun yi ja jawur,kallon mutane kuwa tuni ya dawo kaina......
Mai son complete 800 ne via
2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank
DM +22795045822
[28/04 07:41] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU*
Page 8
Da sauri na nufi Momah ina mai tambayar ta “mi ya faru? Lafiya kike kuka?” ba ta kai ga bani amsa ba na ji an wani jawo ni ta baya ,dakyar na iya miƙe wa kan ƙafafuna na juyo ina fuskantar shi.Namiji ne dattijo wanda ya ba shekara saba'in baya ,shi ne ya jawo ni yayin da sauran tsofin da suka haɗa maza da mata suka yo gaba.
“Yau dai asirin ki ya tonu,shegiyar yarinya ashe mayya ce ke shi ne kika fake da sunan ceto kike.Wancan Kambun maitar da kika rufe shi muke so ki tono kafin Sarkin Mayu ya ƙara so ” ya faɗa ya na mai yin nuni da inda na rufe Kambun Kunkuru.
Banda haske babu abin da wurin yake ,wanda a bayyane yake kowa na ganinsa har da normal mutane.A daidai wannan lokaci ba zan iya yin wani dogon tunani ba ballantana na samo mafita ,duk ma ba wannan ba halin da Momah ke ciki shi ya fi ɗagan hankali.
Tsofin unguwarmu sai zagi ne suke a gaban jama'a, miyagun kalamai wanda duk mai zuciya ba zai iya jura ba.Sosai na yi mamakin dalilin da yasa ban ji sarawar kai ba ,saɓanin sauran lokuta da nake harzuƙa na ɗauki ɓoyayyar fuskata.
A na haka har Sarkin Mayu ya iso,sosai na yi mamaki ganin mutumen nan da muka taɓa haɗuwa cikin taxi.Bayani suka fara yi masa,shi kuma yayi kamar bai taɓa gani na ba tare da umarta ta “je ki haƙo abin da kika ɓoye”
Sai a lokacin na juya na dubi Momah,jiki a sanyayye na duƙa na buɗe ramen tare da ciron Kambun Kunkuru.Haskensa ya ƙara yawaita kan lokacin da yake cikin ƙasa,Sarkin Mayu ya karɓe shi ya na cewa “kin ji kunya ƴar ƙanƙanuwar yarinya da ke amma kin zama muguwa mayya kawai” da mugun sauri na rumtse ido ina jin hawaye na min zuba.
Mutane ne suka fara suratai akan sai mun tashi mun bar masu unguwa,zagi kam ya fi cika buhu babu kalar baƙar maganar da ba a faɗa wa Momah.Ita kuka ni kuka,Sarkin Mayu ya ƙara ɗaukar magana inda yake cewa “na baku nan da awa ɗaya kacal ku tashi ku bar nan ko kuma na sa a ƙone ku da ranku”
Jama'a suka ɗau ihu,da mugun sauri Momah ta shiga gida na take mata baya.A ɗaki na tarar da ita ta na gangamar kaya,rasa abin da zan ce mata na yi kawai sai na faɗa jikinta ina kuka.
“Kukan mi kike? Ina ce ke kika saya mana wulaƙancin da kuɗin ki,tun ranar da kika zo da abin nan sai da na ce ki mayar mai shi abinsa amma kika yi kunnen uwar shegu da ni” ta ida faɗa ta na mai ture ni na yi baya.
Daga inda nake ina jiyo hargowar mutane sai juya suke mana cikin gida tare da zaginmu.Cikin ƙanƙanen lokaci Momah ta haɗa kayanmu,dakyar da siɗin goshi muka samu mu ka isa bakin hanya.Ɗaiɗaikun mutane ne kawai ke tausaya mana,ciki kuwa har da Asabe don a gidanta ma Momah ta kai ajiyar sauran kaya.
A wannan wunin mu ka bazama neman haya sai dai kamar abun tsiya ba mu samu ba,sai a wata unguwa mai ƙarancin mutane kamar za a fita gari shi ma ɗaki ne ciki guda.A haka dai mu ka share mu ka zauna bayan Momah ta kwaso sauran kayanmu.
★
Komai na ta tafiya cikin tsari, musamman bikin da ya kasance tuwona maina ne.Amayar da angon duk ƴan uwa ne,sosai abun ya tafi cikin tsari. A'ishah sai rawar kai take,abokanta kuwa duk sun haɗu wurin kanmu . Fatimah kuwa sai ƙoƙarin kiran Ayodele take a waya saboda rabonta da ita wajen kwana biyu wayarta ma ba ta shiga,cikin wannan zullumi dai ta yi shagalin bikin.
Ranar ɗaurin aure tamkar babu gobe haka aka yi abun hauka musamman ɓangaren Mansur da yake taƙama da Nera.Motocin ɗaukar amarya kaf ɗinsu babu tsohuwa sun jeru rasss sai wacce ranka ya yi ma za ka shiga.A haka aka miƙa A'isha tamfatsetsen gidan mai kama da aljannar duniya,duk yadda ta so Fatimah ta tsaya fafur ta ƙi don dama kan babur ɗinta ta je ko kaɗan ba ta saki jiki da abokan Mansur ba don ƴan magana kan ce sai hali ya zo ɗaya ake abota.
Bayan kowa ya watse Mansur ya shigo tare da abokansa.Kallo ɗaya za ka yi wa gizner jikinsu ka ga Nera ce ke magana,suratansu suka fara ita dai A'ishah ta na rakuɓe sai da suka matsa mata ne ta ɗan ɗage mayafinta.Amanar abokinsu suka bata bisanin yayi masu rakiya ya dawo shi ɗaya.
“Ki sauko mu ci abinci mana” ya faɗa ya na mai jawo hannunta,cike da mamaki A'isha ta bisa har suka baje kan capet.Ta sha ji daga abokaina abu na farko da ake yi in an kai amarya sallah ce domin nuna godiya ga Ubangiji,amma sai ta yi masa uzuri da tunanin ko yunwa yake ji shi yasa.Ba ta kai ƙarshen mamakinta ba sai bayan da suka cika tumbinansu Mansur ya fara aika mata saƙonnin soyayya har ya kai da ya kusanceta,ko Bismillah ba ta ji yayi ba ballantana wai addu'a.
Washegari
Tsabar gajiya da ta yi ya saka ta rasa sallar asubah,hasken rana ne ya daki fuskarta ya sa ta yunƙura ta tashi zaune ta na kallon window.Gefenta kuwa Mansur ne ke ta sharar baccinsa,ta kai hannu ta na jijiga shi “Ogana ka tashi ka kai ni toilet ka min wanka please ba zan iya tashi ba” a shagwaɓe take fitar da harufan har ta ci nasarar tayar da shi.
Ya buɗe idonsa ya zuba mata su ,iya kallon da watsa mata kaɗai sai da gabanta ya faɗi.
“Mine ne?”
“Wanka za min ”
“Can a gidanku wa ke yi miki?”
Ras gaban A'isha ya faɗi jin furucinsa sun yi hannun riga da wanda ya sha faɗa mata satin aurensu.
Dakyar ta ƙoƙarta ta je ta yi wanka ta zo ta gabatar da sallah.Ta na nan zauna har Mansur ya tashi daga bacci,direct wurin drower ya wuce ya fitar da kaya masu kyau ya saka.
“Ka manta ba ka yi wanka ba fa ” ta faɗa ganin bilhaƙi yake shirin,“uban waye ya faɗa miki manta wa na yi?” Mansur ya faɗa a zafafe ya na kallonta.
“Ka yi haƙuri ”shi ne kawai abin da ta iya furta wa.
“Ki tashi ki ɗora min breakfast!” ya faɗa ya na mai fesa turare.
“To” ta amsa tare da tashi.Tsabar takaici sai da ta zubar da hawaye ,amma a haka ta haɗa masa frite da gasashen kifi don ta ga kusan akwai komai.
Kan table ɗin cin abinci ta ajiye bisanin ta wuce bedroom,waya ta tarar da shi ya na yi sai magana yake cikin ladabi.Da ace mahaifinsa na da rai da to babu shakka za ta ce da shi ne yake waya.
Bayan ya gama ne ya zo ya rungume ta tare da cewa “har kin gama?” kai ta jinjina masa,“ok mu je”
Falo suka koma a tare suka ci abincin, Mansur na yi mata hirar soyayya hakan ya kuma ƙulle mata kai.
“Zan tafi wurin aiki,tun ɗazu shugaba ke jirana” ya faɗa tare da miƙe wa tsaye.
“Aiki kuma? A cikin satin aurenmu?”
“To sai aka yi mi? Kin ga ban so sakarci sai na dawo” ya na gama faɗa ya fice. A'isha ta zube kan salon ta na jin wata irin damuwa na dabaibaye ta,tun kafin aje ko ina auren Mansur ya fice mata a rai.“Babu wankan janaba ballantana a yi maganar sallah anya kuwa na auru? Mine ne ma ya hana shi ko fuska da baki ya wanke?” ta furta hawayen takaici na zubo mata bisanin ta ɓingire bacci.
Hayaniyar ƙawayenta ce ta tashe ta,sosai ta yi murnar zuwan su.Sauran kazar jiya ta ɗauko masu kafin a hau hira da girke-girke cike da nishaɗin ƙawarsu ta auri mai kuɗi kowacce ta sasaɓe zane ta ci abubuwa na kayan daɗi ta ƙoshi da za a tafi gida kuwa har da yin tsaraba.
AYODELE