Sashe 11
Farautar Mayu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tun da muka dawo sabon gida Momah ke fushi da ni mai tsanani ,duk uban haƙuri da magiyar da na ta yi mata kanzil ba ta ce min ba.Hakan ya jefa raunatacen ruhina a cakwakiyar matsala,na bar cin abinci kan ƙa'ida,na kashe wayata aiki ma sam na bar zuwa.Amma hakan bai sa Momah ta tausaya min ba.
Kamar kullum wuraren ƙarfe takwas na dare na fito ƙofar gida na yi zaune,unguwar tsit take ko tsuntsu babu.
Wani mutum na ga ya bi ya wuce ta gaban ya nufi wani ɗan gangare,na bi bayansa da kallo kawai ina mamakinsa don yau kusan sau uku kenan da ina ganinsa.
Zuciyata ce ta raya min na bi bayansa,kamar aikaka haka na miƙe har da haɗa wa da gudu na take masa baya.Mun yi tafiya mai ƴar nisa bisanin na tsaya,domin ya kai wurin da ke da tsananin duhu ba zan iya shiga ba.
Idona ne ya sauka ga allon sanarwa mai ɗauke da sunan MAƘABARTA,gabana ya bada ras! ‘Ko shakka babu irin mutanen nan ne masu haƙo kabari don yi aikin asiri ko tsafi’ na faɗa a zuci ina mai ƙara ɗan yin gaba ina ɗigirgire ko Allah ya sa na hango wani abu.Daga bayana na ji an dafa kafaɗa,da mugun sauri na juyo muka haɗa ido a take hanjin cikina suka hautsana.....
[28/04 07:43] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU*
Page 9
A lokacin da na juyo na fuskance shi,a sa'ilin ne kuma na tantance fuskarsa duk da ƙarancin haske da ke wurin.Fuskarsa baƙa ƙirin ce mai ɗauke da ƙwalayen idanuwa babu komai sai gurbinsu da ya bai wa jini damar gangaro wa kan lamutsatsun kumatunsa.
Zuciyata ta fara rawa,hankalina ya tashi farashin tsorona ya ninku ainun ina ta ƙoƙarin cira ƙafata sai dai bai bani damar ba domin kuwa tamkar an dasa ni haka nake a tsaye ƙiƙam.
“Mi bil'adama yake a duniyarmu?” ita ce tambayarsa.
Gabana ya ƙara bada wani sautin rasss,tsabar firgici ban san lokacin da na furta “Ayodele yau kin ɗebo ruwan dafa kan ki”
“Ayodele? Ayodele?” ya maimaita sunan har sau biyu cike da mamaki,bisanin ya ci gaba da cewa “ƴar sarki Lassey?” A daidai wannan gaɓa samaniya ta ɗauki wani irin rugugi da kuma wata irin walƙiya.
Da sauri na lumshe ido jin saukar ruwan sama,wanda suka zame min tamkar wankewar tsoron da ya aure ni.Ji na nake kamar ina kan gajiyar izzata wacce nake juya gawa tare da yin magana da su ba tare da na ji tsoro ba.
Na ji saukar hannunsa akan kafaɗa a karo na biyu,“barka da zuwa duniyar ababen bauta,haƙiƙa ƙarfin ruhinki da nacinsa ya jawo ki izuwa nan.Zo ki yi ziyara gun dangin kakannin ki”
Na ware idona,a yanzu kam ban san mi ya shige ni ba sam ba na jin tsoronsa haka fuskarsa ma ba na ganin muninta.
Tamkar raƙumi da akala ya yi min jagora izuwa tsakiyar maƙabartar wacce take maƙil da kaburbura.
Wasu sanaye ya shiga ambato dukkanninsu babu ɗaya na musulmi,kamar almara sai na fara ganinsu su na fito wa daga cikin kabarinsu su na yin zaune.
Gabatar min da su ya fara ɗai baya ɗayan har aka kawo kan wani tsoho ya nuna min shi da hannu ya ce “kin ga wannan shi ne kakan ki Sarki Octbar,shi ya haifi mahaifin ki Sarki Lassey,waccan kuma da kike gani Yayar baban ki ce sunanta Déborah bayan ta sauka daga mulki mahaifin ki ya hau.Je ki gare su na san za su baki saƙo ,bayan nan sai na kai ki gun ababen bauta”
Gun wanda ya kira da Kakana na je na yi tsayi,hannuna ya kama bai yi magana ba sai jimƙe shi kawai da yayi.Tamkar yadda ake turan abu a xender haka na fara jin sabbin abubuwa na ratsa jijiyoyin hannuna su na shiga magudanar jinina wanda don dole na lumshe ido.
Ya na sake min hannu ya shige ƙarƙashin ƙasa,“ungo wannan zoben ki saka shi,na san komai daren daɗewa za ki je Victoria Falls duk da mahaifiyar ki ba ta so.In kin je ki gaishe min da ƙanena ” Déborah ta faɗa ta na saka min wani tsobe a yatsana manuniya na hagun.
“Mu je” na ji muryarsa, “André kar ka kaita ko ina ka mayar da ita duniya,a halin yanzu akwai tazara mai ƙarfi ita da karagar mulkinta.In lokaci yayi ababen bauta su za su neme ta da kansu,amma mi zai hana ka nuna mata ababen tarihin shahararrun matsafa da kuma yadda suke wanzar da tsafin?”
Sai da ya dube ni da kyau bisanin ya jinjina kansa , Déborah ta ɓace ma ganina a kuma daidai wannan lokaci na tsinci kaina cikin wani hatsabibin daji.Na fara waige-waige,wani irin “wuhummm! Zummm!” nake jin ma'adanar sautina na zuƙo min ai kuwa na toshe kunne,ashe hakan shi ake kiran ainahin ga wofi wai harare cikin duhu don hakan da na yi bai canza zane ba.
“Haƙuri za ki yi da sannu za ki saba”cewar André ,bisanin ya shiga nuna min wasu itatuwa wanda suka fi ɗaukar hankalina su ne wanda suke jere su uku an yi masu ado na penti masu nuni da kalolin tsafi da asiri (mai son ƙarin bayani ya nemi littafina na ƳAN ƘUNGIYAR ASIRI)
Mun yi yawo sosai sai bayanin abubuwa yake min,cikin haka ne na shagala sai ji na yi na yi baya.“Kar ki bi ta nan...” yayi saurin faɗa sai dai tuni na ɗora ƙafata ɗaya wacce nake jin kamar a garwashin wuta take.Tsabar azaba ban san lokacin da na fasa ihu ba,kaina ya juya daga nan ban sake sanin abin da ya faru ba.
“Ayodele keee ?” muryar Momah ta daki kunnena,na ja ajiyar zuciya tare da buɗe idona dakyar da suka min nauyi.
“Lafiya kika kwana a titi? Wato ƙofar gida shi ya fiye miki kan ki kwanta a ciki?” Momah ce ke faɗa rai ɓace.
Kallon wurin da nake na yi,eh a dai ƙofar gidan ne nake zafin rana na haske ni.Dakyar na yunƙura na tashi tsaye,ƙafata ta dama ce na ji ta riƙe “washhh! Wayyooo Momah ” na faɗa hawaye na min shatata.
Abun ka ga uwa tuni ta haɗiye ɓacin ran ta fara taimaka min,dakyar na shiga gida kuka wiwi nake rera wa ita kuma ta na tambayata abubuwan da na yi jiya.Sam ban iya tuna wa ba,to ina ma na ga nutsuwar da zan tuna ɗin.
Jiƙe-jiƙen magani ta yi ta bani na yi wanka,babu laifi na ɗan ji dama musamman da ta saka min maganin massage abokini ta min tausa.Wunin ranar dai na dawo ƴar lelen Momah kamar can farko,duk fushin da take da ni ta janye.
“Allah sa dai ba jan magana ki ka je ki ka sake yi ba! Na sha faɗa miki ba komai ne mutum yake magana ba,haka ba kullum ya zama dole sai ka yi taimako ba.Amma ba ki ji,kunnen ƙashi ne da ke ! Duba ta dalilin ki inda mu ka dawo,da ace kin zauna ɗam da duk hakan ba ta faru ba”
Sama-sama nake jin furucinta don tuni na lula duniyar tunani,wanda ba na komai ba ne sai na mutumen nan mai suna André duk abubuwan da suka faru kuma suka dawo min daram a kwanya sai dai ban san ya aka yi na tsinci kaina ƙofar gida ba.
Na ja a jiyar zuciya ‘ta yi yu kuma mafarki ne na yi’ na faɗa a zuci bisanin na lalubo wayata,na kunnata saƙonnin Fatimah da kiranta ne barkatai na yi ta cin karo da su.
Kiranta na yi,har sai da ta yi ajiyar zuciya wacce nake kyautata zato ta murna ce.
“Wallahi duk kin tashi hankalina,kin kashe waya na je gidan ku kuma kun tashi har wasu sun shiga” cewar Fatimah.
“Yi haƙuri ƙawata tashin ne ya zo cikin wani yanayi,ya aiki kuma ku na ta zuwa?”
“Ina ta dai zuwa! A'isha yau wajen kwana nawa rabonta da aiki,kin san kuwa Dr Jaleel ya karɓi lambar ki wurina”
“Hum! Wasa dai kike,kuma sai kika basa?”
“To ya zan yi?” ta faɗa cikin tausayi,tuni na fahimceta don na daɗe da sanin Fatimah na mugun son Dr Jaleel.
“Oh! Na gane yanzu haka abokinsa ya tambaye shi,ban faɗa miki ba wani ya rage min hanya kwanaki har ya ce na burge shi wai”
Fatimah ta saki ranta,ta ce “wai ne ma? Don Allah Ayodele ki yarda ki fara soyayya a yi mutum kamar jikar almutsutsai”
Shiru na yi ,tunanina ya koma duniyar da na je jiya sai na ce mata kawai “Fatimah zan sake kiran ki” ƙittt! Na kashe kiran.
So nake na tantance shin wai mafarki na yi ko kuwa gaske ne,ina ta tunanin hanyar da zan bi na gaskata cikin ɗaga murya na ce “Lassey!”
Ji kake kwacaaaa Momah ta saki kwandon kwanoni da ta gama wanke wa,dama da gangan na yi don na ga réaction ɗinta.
Da sauri kuma ta shiga kwashe su jikinta har rawa yake,na kuma furta “Lassey fa?” sai na yi tamkar waya nake,ina ankare da Momah a wannan karon ma sai da ta zabura.Na saki murmushi na ce “to Allah kyauta sai an jima”
Kamar kullum wuraren ƙarfe takwas na dare na fito ƙofar gida na yi zaune,unguwar tsit take ko tsuntsu babu.
Wani mutum na ga ya bi ya wuce ta gaban ya nufi wani ɗan gangare,na bi bayansa da kallo kawai ina mamakinsa don yau kusan sau uku kenan da ina ganinsa.
Zuciyata ce ta raya min na bi bayansa,kamar aikaka haka na miƙe har da haɗa wa da gudu na take masa baya.Mun yi tafiya mai ƴar nisa bisanin na tsaya,domin ya kai wurin da ke da tsananin duhu ba zan iya shiga ba.
Idona ne ya sauka ga allon sanarwa mai ɗauke da sunan MAƘABARTA,gabana ya bada ras! ‘Ko shakka babu irin mutanen nan ne masu haƙo kabari don yi aikin asiri ko tsafi’ na faɗa a zuci ina mai ƙara ɗan yin gaba ina ɗigirgire ko Allah ya sa na hango wani abu.Daga bayana na ji an dafa kafaɗa,da mugun sauri na juyo muka haɗa ido a take hanjin cikina suka hautsana.....
[28/04 07:43] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU*
Page 9
A lokacin da na juyo na fuskance shi,a sa'ilin ne kuma na tantance fuskarsa duk da ƙarancin haske da ke wurin.Fuskarsa baƙa ƙirin ce mai ɗauke da ƙwalayen idanuwa babu komai sai gurbinsu da ya bai wa jini damar gangaro wa kan lamutsatsun kumatunsa.
Zuciyata ta fara rawa,hankalina ya tashi farashin tsorona ya ninku ainun ina ta ƙoƙarin cira ƙafata sai dai bai bani damar ba domin kuwa tamkar an dasa ni haka nake a tsaye ƙiƙam.
“Mi bil'adama yake a duniyarmu?” ita ce tambayarsa.
Gabana ya ƙara bada wani sautin rasss,tsabar firgici ban san lokacin da na furta “Ayodele yau kin ɗebo ruwan dafa kan ki”
“Ayodele? Ayodele?” ya maimaita sunan har sau biyu cike da mamaki,bisanin ya ci gaba da cewa “ƴar sarki Lassey?” A daidai wannan gaɓa samaniya ta ɗauki wani irin rugugi da kuma wata irin walƙiya.
Da sauri na lumshe ido jin saukar ruwan sama,wanda suka zame min tamkar wankewar tsoron da ya aure ni.Ji na nake kamar ina kan gajiyar izzata wacce nake juya gawa tare da yin magana da su ba tare da na ji tsoro ba.
Na ji saukar hannunsa akan kafaɗa a karo na biyu,“barka da zuwa duniyar ababen bauta,haƙiƙa ƙarfin ruhinki da nacinsa ya jawo ki izuwa nan.Zo ki yi ziyara gun dangin kakannin ki”
Na ware idona,a yanzu kam ban san mi ya shige ni ba sam ba na jin tsoronsa haka fuskarsa ma ba na ganin muninta.
Tamkar raƙumi da akala ya yi min jagora izuwa tsakiyar maƙabartar wacce take maƙil da kaburbura.
Wasu sanaye ya shiga ambato dukkanninsu babu ɗaya na musulmi,kamar almara sai na fara ganinsu su na fito wa daga cikin kabarinsu su na yin zaune.
Gabatar min da su ya fara ɗai baya ɗayan har aka kawo kan wani tsoho ya nuna min shi da hannu ya ce “kin ga wannan shi ne kakan ki Sarki Octbar,shi ya haifi mahaifin ki Sarki Lassey,waccan kuma da kike gani Yayar baban ki ce sunanta Déborah bayan ta sauka daga mulki mahaifin ki ya hau.Je ki gare su na san za su baki saƙo ,bayan nan sai na kai ki gun ababen bauta”
Gun wanda ya kira da Kakana na je na yi tsayi,hannuna ya kama bai yi magana ba sai jimƙe shi kawai da yayi.Tamkar yadda ake turan abu a xender haka na fara jin sabbin abubuwa na ratsa jijiyoyin hannuna su na shiga magudanar jinina wanda don dole na lumshe ido.
Ya na sake min hannu ya shige ƙarƙashin ƙasa,“ungo wannan zoben ki saka shi,na san komai daren daɗewa za ki je Victoria Falls duk da mahaifiyar ki ba ta so.In kin je ki gaishe min da ƙanena ” Déborah ta faɗa ta na saka min wani tsobe a yatsana manuniya na hagun.
“Mu je” na ji muryarsa, “André kar ka kaita ko ina ka mayar da ita duniya,a halin yanzu akwai tazara mai ƙarfi ita da karagar mulkinta.In lokaci yayi ababen bauta su za su neme ta da kansu,amma mi zai hana ka nuna mata ababen tarihin shahararrun matsafa da kuma yadda suke wanzar da tsafin?”
Sai da ya dube ni da kyau bisanin ya jinjina kansa , Déborah ta ɓace ma ganina a kuma daidai wannan lokaci na tsinci kaina cikin wani hatsabibin daji.Na fara waige-waige,wani irin “wuhummm! Zummm!” nake jin ma'adanar sautina na zuƙo min ai kuwa na toshe kunne,ashe hakan shi ake kiran ainahin ga wofi wai harare cikin duhu don hakan da na yi bai canza zane ba.
“Haƙuri za ki yi da sannu za ki saba”cewar André ,bisanin ya shiga nuna min wasu itatuwa wanda suka fi ɗaukar hankalina su ne wanda suke jere su uku an yi masu ado na penti masu nuni da kalolin tsafi da asiri (mai son ƙarin bayani ya nemi littafina na ƳAN ƘUNGIYAR ASIRI)
Mun yi yawo sosai sai bayanin abubuwa yake min,cikin haka ne na shagala sai ji na yi na yi baya.“Kar ki bi ta nan...” yayi saurin faɗa sai dai tuni na ɗora ƙafata ɗaya wacce nake jin kamar a garwashin wuta take.Tsabar azaba ban san lokacin da na fasa ihu ba,kaina ya juya daga nan ban sake sanin abin da ya faru ba.
“Ayodele keee ?” muryar Momah ta daki kunnena,na ja ajiyar zuciya tare da buɗe idona dakyar da suka min nauyi.
“Lafiya kika kwana a titi? Wato ƙofar gida shi ya fiye miki kan ki kwanta a ciki?” Momah ce ke faɗa rai ɓace.
Kallon wurin da nake na yi,eh a dai ƙofar gidan ne nake zafin rana na haske ni.Dakyar na yunƙura na tashi tsaye,ƙafata ta dama ce na ji ta riƙe “washhh! Wayyooo Momah ” na faɗa hawaye na min shatata.
Abun ka ga uwa tuni ta haɗiye ɓacin ran ta fara taimaka min,dakyar na shiga gida kuka wiwi nake rera wa ita kuma ta na tambayata abubuwan da na yi jiya.Sam ban iya tuna wa ba,to ina ma na ga nutsuwar da zan tuna ɗin.
Jiƙe-jiƙen magani ta yi ta bani na yi wanka,babu laifi na ɗan ji dama musamman da ta saka min maganin massage abokini ta min tausa.Wunin ranar dai na dawo ƴar lelen Momah kamar can farko,duk fushin da take da ni ta janye.
“Allah sa dai ba jan magana ki ka je ki ka sake yi ba! Na sha faɗa miki ba komai ne mutum yake magana ba,haka ba kullum ya zama dole sai ka yi taimako ba.Amma ba ki ji,kunnen ƙashi ne da ke ! Duba ta dalilin ki inda mu ka dawo,da ace kin zauna ɗam da duk hakan ba ta faru ba”
Sama-sama nake jin furucinta don tuni na lula duniyar tunani,wanda ba na komai ba ne sai na mutumen nan mai suna André duk abubuwan da suka faru kuma suka dawo min daram a kwanya sai dai ban san ya aka yi na tsinci kaina ƙofar gida ba.
Na ja a jiyar zuciya ‘ta yi yu kuma mafarki ne na yi’ na faɗa a zuci bisanin na lalubo wayata,na kunnata saƙonnin Fatimah da kiranta ne barkatai na yi ta cin karo da su.
Kiranta na yi,har sai da ta yi ajiyar zuciya wacce nake kyautata zato ta murna ce.
“Wallahi duk kin tashi hankalina,kin kashe waya na je gidan ku kuma kun tashi har wasu sun shiga” cewar Fatimah.
“Yi haƙuri ƙawata tashin ne ya zo cikin wani yanayi,ya aiki kuma ku na ta zuwa?”
“Ina ta dai zuwa! A'isha yau wajen kwana nawa rabonta da aiki,kin san kuwa Dr Jaleel ya karɓi lambar ki wurina”
“Hum! Wasa dai kike,kuma sai kika basa?”
“To ya zan yi?” ta faɗa cikin tausayi,tuni na fahimceta don na daɗe da sanin Fatimah na mugun son Dr Jaleel.
“Oh! Na gane yanzu haka abokinsa ya tambaye shi,ban faɗa miki ba wani ya rage min hanya kwanaki har ya ce na burge shi wai”
Fatimah ta saki ranta,ta ce “wai ne ma? Don Allah Ayodele ki yarda ki fara soyayya a yi mutum kamar jikar almutsutsai”
Shiru na yi ,tunanina ya koma duniyar da na je jiya sai na ce mata kawai “Fatimah zan sake kiran ki” ƙittt! Na kashe kiran.
So nake na tantance shin wai mafarki na yi ko kuwa gaske ne,ina ta tunanin hanyar da zan bi na gaskata cikin ɗaga murya na ce “Lassey!”
Ji kake kwacaaaa Momah ta saki kwandon kwanoni da ta gama wanke wa,dama da gangan na yi don na ga réaction ɗinta.
Da sauri kuma ta shiga kwashe su jikinta har rawa yake,na kuma furta “Lassey fa?” sai na yi tamkar waya nake,ina ankare da Momah a wannan karon ma sai da ta zabura.Na saki murmushi na ce “to Allah kyauta sai an jima”