Sashe 1
Farautar Mayu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
[19/04 15:19] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU*
Ƙirƙiraren labari ne,ban yi shi don cin mutumci kowa ba.Duk wanda ya zo daidai da rayuwarsa to akasi aka samu.
1
#ƘASAR COTE D'IVOIRE
#Babbar asibitin Abengourou
A tsorace nake ƙara tushe kunnuwana ko zan samu sa'ar toshe ma'adanar sautina da ke zuƙo min wata murya mai cike da tashin hankali.Sai dai yaudarar kaina nake,domin kuwa toshe kunnen da na yi hakan bai canza zane ba .Na kai hannu da niyyar ɗaukar pilow ko shi Allah zai sa na dace,hasken ɗakin ne ya ɗauke ɗif wanda ya yi sanadiyar tsayawar na'urar da ke kore zafi.
Ƙaiƙayi na fara ji yayin da sauro da zafi suka ce salama alaikum,shegiyar muryar nan mai shegen naci sai ƙara ƙaimi take wurin roƙon abin da ban san mi take so ba “ku cece ni ! Ku cece ni don Allah babu kowa ne?”
Na ja tsuki bisanin na lalubo wayata na kunna fitila,duk abokan aikina baccinsu kawai suke a gajiye.Na miƙe tare da nufar ƙofa,na murɗa handle na fito ,ga mamakina ko ina na asibitin akwai hasken wuta sai ɗakinmu da kuma wani ɗakin da ke can gabashi wanda akwai ƴar tazara tsakani.
Haka kawai na ji zuciyata na tunzura ni kan na je na duba tako ɗaya ,biyu,ina daɗa matsawa ina kuma daɗa jin sautin muryar nan mai neman taimako har na isa bakin ƙofar daidai nan hasken ɗakin ya dawo.Na kutsa kai,sai na tarar da nurse biyu da wani Dr a tsaye kan wata matashiyar budurwa ,gefe kuma wata jemamiyar tsohuwa ce zaune ta na kaɗa ƙafa.
Duk kallonsu ya dawo kaina,ni ma su nake kallo ɗin.
“Ayodele mi kike yi a nan? Babu aiki ne ɓangaren ku?” Dr ya tambaye ni,na buɗa baki da niyyar yin magana na tsinkayo wata murya kuma na ce min “Ayodele please ki taimaka min ban mutu ba!”
Inda sautin ya fito na duba,sai yanzu na lura da idon budurwar rufe suke ruf kamar mai yin bacci.Da mamaki nake tambayar kaina ‘dama mai bacci ya na iya yin magana?’
“Ta rasu ne! Ƙoƙarin cire duk abubuwan da ke jikinta ne muke amma sun ƙi fita” Dr ya katse min tunani.
“Amma yanzun nan fa ta min magana akan na taimaketa ba ta mutu ba” na faɗa .
Duk kallon mamaki suka bi ni da shi,hakan yasa na ci gaba da cewa “tun ɗazu fa ita ta hana ni bacci kururuwar ta ce ta tashe ni”
“Ayodeleee?” Dr ya kira ni da wani sauti,bisanin ya tambayi nurse ɗin “ku tun ɗazu da muke nan kun ji kururuwar ne?” duk kai suka girgiza alamun a'a.
Sai ya maido kallonsa gare ni “to kin ji ta yiyu kunnuwanki ne ba su jiye miki daidai ba”
“Mi sunanta?” ita ce tambayar da na yi,“Emeka” ɗaya daga cikin nurse ɗin ta ban amsa.
A hankali na fara taka ƙafata sai dai kafin na isa ga Emekar tsohuwar nan ta taso tare da tsaya wa a gabana “ina za ki je? Mi za ki yi?” ta jero min tambayoyi haɗi da jifata da wani mugun kallo mai ratsa ɓargo da tsoka don sam bai da daɗi.
Dakyar na fizgo numfashi tare da jarumtar kallonta cikin tsakiyar ido ,kawai sai na ga mugun razani a nata idon tare kuma da saurin ja ta bani wuri ba tare da na san dalilin yin haka ba.
Kai ga Emeka na yi tsaye bisanin na kai hannu kan fuskarta na ce “Emeka ?”
“Ayodele ta fa mutu,ya kike yi wa matatta magana kamar zautatta?” Dr ya tari numfashina.Ba tare da na dube shi ba na ce “ba ta mutu ba Dr ! Doguwar suma aka sa ta”
“Wa ya sa ta doguwar suma? Nan fa asibiti ce kuma mun san aikinmu ”
“Dr ita wacce ta saka ta suman ta san kan ta! Ina iyayenta suke?” na tambaya.
“Daga ita sai Kakarta suka zo,kuma ga ta can ta fita” cewar nurse.
Na ɗago kaina sai na ga tuni tsohuwar nan ba ta nan,wato abin da na fahimta ita ce Kakar Emeka.
“Ayodele ki taimaka ki damƙa ni ga iyayena Kakata ba ta sona shi ne take son kashe ni,ta ɓoye ruhina cikin asusun ƙarfe ta lashi takobi ba za ta fiddo shi ba har abada” shiru na yi ina sauraren esprit ɗin Emeka da ke yi min magana ba tare da ni kaina na san shi ne ba.
“Dr yanzu ma ba ga shi ta na yin magana ba?”
“Mtsw! Ayodele fita! Fita na ce !” Dr ya yi min wata muguwar tsawa.
Tako ɗaya na yi na tsaya,cikin fushi ya kuma cewa “kenan ba za ki fita ɗin ba?”
Murya a raunane na ce “ba ka ga ta riƙe min hannu ba ne?”
Duk ido suka waro Dr har da ɗora hannu a kai ya ce “wai Ayodele haukata ni kike son yi? Ku kun ga ta riƙe ta?” ya tambayi nurse suka girgiza kai.
Da mamaki nake kallonsu bisanin na mayar da dubana ga Emeka wacce ta riƙe ni gam ta na girgiza kai idonta na shatatar da hawaye.
“Ke kaɗai ke jin abin da nake cewa da kuma ganin abin da nake don Allah kar ki biye su” cewar Emeka .
Cikin jin haushi Dr ya fizgo hannuna da niyyar fitar da ni da ƙarfin tsiya sai dai sam ya kasa sakamakon ɗayan hannun da ke riƙe da Emeka .
“Dr ni fa na fara jin tsoro! Ina ga fa gaskiya ne! Dubi yadda hannunta ke jone kamar a rinƙe shi ɗin kuma ....kuma gadon kamar ya na motsa wa” nurse ta faɗa.
Dr ya sake min hannu,ya ce “ba zan yi mamaki ba don Abeno cike take da ƴaƴan matsafa da Mayu....” bai rufe bakinsa ba Emeka ta fara shaƙuwa,da sauri duk suka nufeta tare da saita na'urar aiki a kanta.
Ni kuwa ganin numfashinta ya dawo kawai sai na sulale na koma can ɓangaren mu.Kasa bacci na yi sai zaune da na yi na rabka uban tagumi ina tunanin abin da ya faru.Gadon bayana ne ya fara yin ƙaiƙayi,tare kuma da wata irin tsira wa tamkar ana nitsa wasu abubuwa gefe da gefen kafaɗuna.
Dishi-dishi idona ya fara,ban san ya aka yi ba na tsinci kaina a wata duniya wacce na fi kyautata zaton ta mafarki ce.
Wani ƙaton gida mai ɗauke da ɗakuna kashi-kashi,ruhina ya sallama.Babu wanda ya amsa min haka ba wanda ya ɗago ya dube ni sai tsohuwa wacce tun farkon shigowata na ji yaran gidan na ambaton sunanta da “Yaba”
Mugun kallon nan mai cike da hassada,ƙyashi haɗi da baƙin ciki ta jefo min bisanin ta miƙe tsaye ta zo gare ni.“Mi kike so kuma yanzu?”
“Abin da kika ɓoye!” na bata amsa.
“Maganar ahali ce wannan bai shafe ki ba,kin dai yi naki ikon don haka ki....” ban bari ta dire ba na tari numfashinta da “ki bani cikin lumana ko kuma na ƙwata ta ƙarfin tsiya! Yin haka kuma babba asara ce gare ki domin duk abin da kika ɓoye zan fito da su ne”
Tsoro ne na gani shimfiɗe ƙarara a fuskar Yaba,bisanin ta yi gaba ni kuma na take mata baya har cikin ɗakinta na laka wanda aka yi ma rufin kara.
Ƙarƙashin gado ta duƙa ta fito da wani asusun ƙarfe tare da miƙo min shi,ban ɗauki lokaci ba wurin buɗe shi.Baƙin hayaƙi ya fito kamar fitar iska ya tashi sama,guntun ƙyallen atamfa na gani sai na ɗauke shi bisanin na aje asusun na fito.
Daidai nan kuma na farka daga baccina,na dafe gefen goshina da yake sara min bisanin na buɗe idona taram .Da sauri na tashi ganin Emeka a tsaye ta na min murmushi.
“Na gode sosai Ayodele,kin ceci rayuwata!” ta faɗa tare da ƙoƙarin karɓa wani abu daga hannuna da nake jin na jimƙe ba tare da na san mine ne ba sai da na kai dubana sai na ga ƙiren atamfar da na yi mafarki ne.
Emeka ta ci gaba da cewa “wannan zanen ankon bikina ce,Inna Yaba ta yi amfani da shi don kashe ni saboda kawai zan auri bare wanda ba cikin danginmu ba.Na gode!” ta na gama faɗar haka ta fice ta bar ni sake da baki ina tunanin kar dai ace mafarkin da na yi gaskiya ne? ??????
[19/04 15:23] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU*
2
Har aka fara kiran asallatu ban rumtsa ba,ina ta saƙa da warwara don gano ainahin abin da ke faruwa da ni sai dai ga banza wai an tsikari kakkausa.
Ƙarfe biyar na asubahi abokan aikina suka tashi don gabatar da sallah.Har suka ida ina nan zaune ina reto da ƙafafuna, A'ishah ta dube ni cike da kulawa ta ce “Ayodele lafiyar ki kuwa?”
“Ƙalau nake!” na bata amsa.
“Mi ya samu fuskar ki duk ta yi ja?” ta sake tambayata,ban bata amsa ba sai wata nauyayyar ajiyar zuciya da na sauke.
Fatima da ke jan casbi kusa da ita ta ce “ƙila mafarkin da ta saba yi ne yau ma ya sake zuwar mata”
Na ɗan harareta na ce “don ban da aikin yi sai mafarkin ɓoyayyen masoyi ko?” duk suka yi dariya bisanin A'ishah ta ce “Ya kamata dai ki tashi ki wanke fuskar ki tun da ba sallah za ki yi ba”
Na dube ta na ce “lokacin da nake tawa ibadar ki na ina ne?”
Ta taɓe baki ta ce “ibadar da kike yi marar alƙibila? Ke fa kan ki ba ki san wane ne kike bauta ma ba”
“Ubangiji nake bauta! Kuma na yi imani da shi,kamar yadda kuke bautar naku da ba ku taɓa gani ba” na bata amsa.
Fatima ta ce “don Allah ku bar zancen Addini! Mu je mu ida aikinmu mu kama gabanmu”
Hakan kuwa aka yi,bayan na wanke fuskata mu ka shiga fara duba maras lafiya ƙarfe tara na buga wa duk mu ka sauka daga aiki.
Ƙirƙiraren labari ne,ban yi shi don cin mutumci kowa ba.Duk wanda ya zo daidai da rayuwarsa to akasi aka samu.
1
#ƘASAR COTE D'IVOIRE
#Babbar asibitin Abengourou
A tsorace nake ƙara tushe kunnuwana ko zan samu sa'ar toshe ma'adanar sautina da ke zuƙo min wata murya mai cike da tashin hankali.Sai dai yaudarar kaina nake,domin kuwa toshe kunnen da na yi hakan bai canza zane ba .Na kai hannu da niyyar ɗaukar pilow ko shi Allah zai sa na dace,hasken ɗakin ne ya ɗauke ɗif wanda ya yi sanadiyar tsayawar na'urar da ke kore zafi.
Ƙaiƙayi na fara ji yayin da sauro da zafi suka ce salama alaikum,shegiyar muryar nan mai shegen naci sai ƙara ƙaimi take wurin roƙon abin da ban san mi take so ba “ku cece ni ! Ku cece ni don Allah babu kowa ne?”
Na ja tsuki bisanin na lalubo wayata na kunna fitila,duk abokan aikina baccinsu kawai suke a gajiye.Na miƙe tare da nufar ƙofa,na murɗa handle na fito ,ga mamakina ko ina na asibitin akwai hasken wuta sai ɗakinmu da kuma wani ɗakin da ke can gabashi wanda akwai ƴar tazara tsakani.
Haka kawai na ji zuciyata na tunzura ni kan na je na duba tako ɗaya ,biyu,ina daɗa matsawa ina kuma daɗa jin sautin muryar nan mai neman taimako har na isa bakin ƙofar daidai nan hasken ɗakin ya dawo.Na kutsa kai,sai na tarar da nurse biyu da wani Dr a tsaye kan wata matashiyar budurwa ,gefe kuma wata jemamiyar tsohuwa ce zaune ta na kaɗa ƙafa.
Duk kallonsu ya dawo kaina,ni ma su nake kallo ɗin.
“Ayodele mi kike yi a nan? Babu aiki ne ɓangaren ku?” Dr ya tambaye ni,na buɗa baki da niyyar yin magana na tsinkayo wata murya kuma na ce min “Ayodele please ki taimaka min ban mutu ba!”
Inda sautin ya fito na duba,sai yanzu na lura da idon budurwar rufe suke ruf kamar mai yin bacci.Da mamaki nake tambayar kaina ‘dama mai bacci ya na iya yin magana?’
“Ta rasu ne! Ƙoƙarin cire duk abubuwan da ke jikinta ne muke amma sun ƙi fita” Dr ya katse min tunani.
“Amma yanzun nan fa ta min magana akan na taimaketa ba ta mutu ba” na faɗa .
Duk kallon mamaki suka bi ni da shi,hakan yasa na ci gaba da cewa “tun ɗazu fa ita ta hana ni bacci kururuwar ta ce ta tashe ni”
“Ayodeleee?” Dr ya kira ni da wani sauti,bisanin ya tambayi nurse ɗin “ku tun ɗazu da muke nan kun ji kururuwar ne?” duk kai suka girgiza alamun a'a.
Sai ya maido kallonsa gare ni “to kin ji ta yiyu kunnuwanki ne ba su jiye miki daidai ba”
“Mi sunanta?” ita ce tambayar da na yi,“Emeka” ɗaya daga cikin nurse ɗin ta ban amsa.
A hankali na fara taka ƙafata sai dai kafin na isa ga Emekar tsohuwar nan ta taso tare da tsaya wa a gabana “ina za ki je? Mi za ki yi?” ta jero min tambayoyi haɗi da jifata da wani mugun kallo mai ratsa ɓargo da tsoka don sam bai da daɗi.
Dakyar na fizgo numfashi tare da jarumtar kallonta cikin tsakiyar ido ,kawai sai na ga mugun razani a nata idon tare kuma da saurin ja ta bani wuri ba tare da na san dalilin yin haka ba.
Kai ga Emeka na yi tsaye bisanin na kai hannu kan fuskarta na ce “Emeka ?”
“Ayodele ta fa mutu,ya kike yi wa matatta magana kamar zautatta?” Dr ya tari numfashina.Ba tare da na dube shi ba na ce “ba ta mutu ba Dr ! Doguwar suma aka sa ta”
“Wa ya sa ta doguwar suma? Nan fa asibiti ce kuma mun san aikinmu ”
“Dr ita wacce ta saka ta suman ta san kan ta! Ina iyayenta suke?” na tambaya.
“Daga ita sai Kakarta suka zo,kuma ga ta can ta fita” cewar nurse.
Na ɗago kaina sai na ga tuni tsohuwar nan ba ta nan,wato abin da na fahimta ita ce Kakar Emeka.
“Ayodele ki taimaka ki damƙa ni ga iyayena Kakata ba ta sona shi ne take son kashe ni,ta ɓoye ruhina cikin asusun ƙarfe ta lashi takobi ba za ta fiddo shi ba har abada” shiru na yi ina sauraren esprit ɗin Emeka da ke yi min magana ba tare da ni kaina na san shi ne ba.
“Dr yanzu ma ba ga shi ta na yin magana ba?”
“Mtsw! Ayodele fita! Fita na ce !” Dr ya yi min wata muguwar tsawa.
Tako ɗaya na yi na tsaya,cikin fushi ya kuma cewa “kenan ba za ki fita ɗin ba?”
Murya a raunane na ce “ba ka ga ta riƙe min hannu ba ne?”
Duk ido suka waro Dr har da ɗora hannu a kai ya ce “wai Ayodele haukata ni kike son yi? Ku kun ga ta riƙe ta?” ya tambayi nurse suka girgiza kai.
Da mamaki nake kallonsu bisanin na mayar da dubana ga Emeka wacce ta riƙe ni gam ta na girgiza kai idonta na shatatar da hawaye.
“Ke kaɗai ke jin abin da nake cewa da kuma ganin abin da nake don Allah kar ki biye su” cewar Emeka .
Cikin jin haushi Dr ya fizgo hannuna da niyyar fitar da ni da ƙarfin tsiya sai dai sam ya kasa sakamakon ɗayan hannun da ke riƙe da Emeka .
“Dr ni fa na fara jin tsoro! Ina ga fa gaskiya ne! Dubi yadda hannunta ke jone kamar a rinƙe shi ɗin kuma ....kuma gadon kamar ya na motsa wa” nurse ta faɗa.
Dr ya sake min hannu,ya ce “ba zan yi mamaki ba don Abeno cike take da ƴaƴan matsafa da Mayu....” bai rufe bakinsa ba Emeka ta fara shaƙuwa,da sauri duk suka nufeta tare da saita na'urar aiki a kanta.
Ni kuwa ganin numfashinta ya dawo kawai sai na sulale na koma can ɓangaren mu.Kasa bacci na yi sai zaune da na yi na rabka uban tagumi ina tunanin abin da ya faru.Gadon bayana ne ya fara yin ƙaiƙayi,tare kuma da wata irin tsira wa tamkar ana nitsa wasu abubuwa gefe da gefen kafaɗuna.
Dishi-dishi idona ya fara,ban san ya aka yi ba na tsinci kaina a wata duniya wacce na fi kyautata zaton ta mafarki ce.
Wani ƙaton gida mai ɗauke da ɗakuna kashi-kashi,ruhina ya sallama.Babu wanda ya amsa min haka ba wanda ya ɗago ya dube ni sai tsohuwa wacce tun farkon shigowata na ji yaran gidan na ambaton sunanta da “Yaba”
Mugun kallon nan mai cike da hassada,ƙyashi haɗi da baƙin ciki ta jefo min bisanin ta miƙe tsaye ta zo gare ni.“Mi kike so kuma yanzu?”
“Abin da kika ɓoye!” na bata amsa.
“Maganar ahali ce wannan bai shafe ki ba,kin dai yi naki ikon don haka ki....” ban bari ta dire ba na tari numfashinta da “ki bani cikin lumana ko kuma na ƙwata ta ƙarfin tsiya! Yin haka kuma babba asara ce gare ki domin duk abin da kika ɓoye zan fito da su ne”
Tsoro ne na gani shimfiɗe ƙarara a fuskar Yaba,bisanin ta yi gaba ni kuma na take mata baya har cikin ɗakinta na laka wanda aka yi ma rufin kara.
Ƙarƙashin gado ta duƙa ta fito da wani asusun ƙarfe tare da miƙo min shi,ban ɗauki lokaci ba wurin buɗe shi.Baƙin hayaƙi ya fito kamar fitar iska ya tashi sama,guntun ƙyallen atamfa na gani sai na ɗauke shi bisanin na aje asusun na fito.
Daidai nan kuma na farka daga baccina,na dafe gefen goshina da yake sara min bisanin na buɗe idona taram .Da sauri na tashi ganin Emeka a tsaye ta na min murmushi.
“Na gode sosai Ayodele,kin ceci rayuwata!” ta faɗa tare da ƙoƙarin karɓa wani abu daga hannuna da nake jin na jimƙe ba tare da na san mine ne ba sai da na kai dubana sai na ga ƙiren atamfar da na yi mafarki ne.
Emeka ta ci gaba da cewa “wannan zanen ankon bikina ce,Inna Yaba ta yi amfani da shi don kashe ni saboda kawai zan auri bare wanda ba cikin danginmu ba.Na gode!” ta na gama faɗar haka ta fice ta bar ni sake da baki ina tunanin kar dai ace mafarkin da na yi gaskiya ne? ??????
[19/04 15:23] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU*
2
Har aka fara kiran asallatu ban rumtsa ba,ina ta saƙa da warwara don gano ainahin abin da ke faruwa da ni sai dai ga banza wai an tsikari kakkausa.
Ƙarfe biyar na asubahi abokan aikina suka tashi don gabatar da sallah.Har suka ida ina nan zaune ina reto da ƙafafuna, A'ishah ta dube ni cike da kulawa ta ce “Ayodele lafiyar ki kuwa?”
“Ƙalau nake!” na bata amsa.
“Mi ya samu fuskar ki duk ta yi ja?” ta sake tambayata,ban bata amsa ba sai wata nauyayyar ajiyar zuciya da na sauke.
Fatima da ke jan casbi kusa da ita ta ce “ƙila mafarkin da ta saba yi ne yau ma ya sake zuwar mata”
Na ɗan harareta na ce “don ban da aikin yi sai mafarkin ɓoyayyen masoyi ko?” duk suka yi dariya bisanin A'ishah ta ce “Ya kamata dai ki tashi ki wanke fuskar ki tun da ba sallah za ki yi ba”
Na dube ta na ce “lokacin da nake tawa ibadar ki na ina ne?”
Ta taɓe baki ta ce “ibadar da kike yi marar alƙibila? Ke fa kan ki ba ki san wane ne kike bauta ma ba”
“Ubangiji nake bauta! Kuma na yi imani da shi,kamar yadda kuke bautar naku da ba ku taɓa gani ba” na bata amsa.
Fatima ta ce “don Allah ku bar zancen Addini! Mu je mu ida aikinmu mu kama gabanmu”
Hakan kuwa aka yi,bayan na wanke fuskata mu ka shiga fara duba maras lafiya ƙarfe tara na buga wa duk mu ka sauka daga aiki.