Sashe 28
Facala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kukan muklees da Su'ada ta jiyo a d'aki yasa ta shige da sauri,tana fad'in "Yauwa Babana sarkin kuka an farka da kukan kenan."
Khairiyya dai cirewa Nusrat kayan tai gaba d'aya, ta barta daga ita sai base da d'an pant,dake daman zafi ake sosai a lokacin.
Bayan Su'ada ta d'auko muklees ta zauna kusa da Khairiyyan tana fad'in "Uwar masifa ko gaisawa ba muyi ba fa."
Y'ar dariya Khairiyyan tai kafin ta gaida ta,tana tsokanar Muklees "Su Abbanmu sarkin kuka sarkin tsotso."
Harararta Su'ada tai da fad'in"Abban ake cewa sarkin kuka ko?"
Cikin dariya Khairiyya tace "To ai ba k'arya nai ba,jifa daga farkawa daga bacci ya cika gari da kuka,yasin yaron nan badan sunan Abbanmu gareshi ba bazan had'a jam'iyya dashi ba."
"To karki had'a mana,ni ina had'e da Abuna,kin fi son ki ganshi salo salo kamar y'arku,ah Allah ya kiyaye, Abbana namijin duniya ne me k'arfin sojoji."
Khairiyya na dariya ta d'ora Nusrat akan cinyarta tana fad'in "Ai Wallahi yarinyata bata da makusa, d'abiun ta kalar na mata,jan aji da nutsuwa ne yasa bata hayaniya tun tana jinjira, komai nata cikin class take,amma wannan Abban ai kalar garada ne."
Ta kai k'arshen zancen da dariya sosai.
Yatsina Fuska Su'ada tai tana kallon kayan da aka cirewa Nusrat d'in tace "Wai don wulak'ancinku kawai don ta d'an goga mata maik'o shine kuka cire kayan? Yasin baki da kara fa."
D'age gira Khairiyya tai da watsa hannu alamar ko a jikinta tace "To akan me zan barta da kaya me datti a jiki? Ah haba wai baki da labarin y'ata me tsada ce ne?"
Mik'ewa Su'ada tai tana dire muklees a kan cafet,ta wuce kitchen, don bata dad'e da dawowa daga makaranta ba,don ma yara exam's suke da wuri suke tashi
Girkin data d'ora taje ta duba,sannan ta dawo suka d'ora hira.
Sallamar Baby ce tasa su tsayawa da hirar suna amsa mata,da fara'arta ta k'araso tana fad'in "Yanzun nan ina shigowa Islam tace min Nusrat tazo."
Tsugunnawa tai tana kamo hannun yarinyar,tana gaida Khairiyya, sannan ta dauketa zasu fita Muklees yasa kuka yana mik'awa Babyn hannu.
Tafa hannu Su'ada tai da fad'in "Eh lalle Baby,sabida kinga Nusrat shine zaki wulak'anta min uba,to ai zata tafi ta barmu da ke ne."
Dariya Babyn tai tana jutowa ta d'auki muklees d'in a d'aya hannunta.
bayan Sun fita Khairiyya tace "Allah sarki Baby,Wallahi sam ba tai halin Uwarta ba,yarinyar na birgeni."
Gyad'a kai Su'ada tai tace "Ita kam halin Babanta tai,ba ruwanta,rayuwar ta komai da sauk'i take yinsa."
Daga wannan hirar suka koma hirar bikin Jiddah, Wanda ya rage wata biyu.
******
Baby dai na can d'akinsu tana ta fama da su Muklees, musamman Nusrat da take ta hannun damanta,sai ina naka sa ina naka aje take da yarinyar.
*********K'arfe daya da rabi Khaleelee ya dawo gida don yin shirin sallar jummaa,dake su masallacin murtala suke bi,kuma sai k'arfe biyu ake salla a masallacin.
A tsakar gida ya tarda Baby ta na goye da Muklees, tana bawa Nusrat abinci a baki,cikin mirmishi yake amsa sannu da zuwan da yaran ke masa.
Rik'o hannun Nusrat d'in ya yi yana fad'in "Mamana yau an waiwayomu kenan, ke da wa kuka zo?"
Cikin gwarancinta tace "Aunty Khairiyya ne."
Gyad'a kai ya yi yana mik'awa Islam hannu su ka tafa,yace "Maman mama me aka ci ne baki ke maik'o
"
Girgiza kai tai cikin dariya tace "Abinci muka ci fa me dad'i."
Yana y'ar dariya ya wuce ciki.
A falo ya same su suna cin abunci,Khairiyya ta gaisheshi ya amsa yana tsokanarta don Bayan Khaleelee cikin y'an gidan yafi wasa da Khairiyya.
Kad'an ya d'an zauna yana tambayarta gida dasu mama, sannan ya wuce d'aki.
Bin bayansa Su'ada tai zuwa d'akin, yana k'ok'arin rage kayan jikinsa yace "Madam a had'a min ruwa,ji nake kamar ban tab'a wanka ba,gaskiya yau ana zafi sosai."
Taimaka mishi tai ya cire kayan jikinsa zuwa jallabiya.sannu ta fito ta had'a mishi ruwan wanka.
Sai wajan k'arfe uku Khaleelee ya dawo gidan daga masallaci.
Khairiyya na d'aya d'aki tana bacci, yayin da Su'ada ke falo tana marking exam's d'in d'alibai, Muklees ma baccin yake sai Nusrat a gefenta tana mata hirarsu ta yara.
Zama ya yi kan kujera yana amsa sannu da zuwan Su'ada, idonsa naga Nusrat,sosai yake kallon yarinyar yana ganin kullum k'ara girma take,dukda yana wata guda ko giye bai ganta ba,amma duk sanda zai ganta sai yaga tai tsayi.
Yana wannan tunanin har Su'ada ta kawo mishi abinci.bayan ya sauko k'asa inda zai ci abincin yace "Mamana zo mu ci abincin ."
Girgiza Kai tai alamun ta k'oshi, mirmishi kan fuskarsa yace " Su'ada yarinyar nan ta kusa kamoki a tsayi fa."
Dariya Su'ada tai kafin tace "Tunda tai gadon tsayi ai in ma ta fini tsayin ba damuwa bace."
D'agata yai cas ya d'ora ta kan cinyarsa,wani k'aunar yarinyar yake ji na ratsa b'argo da jijiyarsa,tabbas kara da kawaici ne kawai ba za su barshi yace a dawo mai da y'arsa gida ba.ya San yanda ake kula da ita a can ko gidan ma sai haka,to amma fa shima ya na buk'atarta kusa da shi.
Wasa take tayi da gaban rigarsa ,yayin da idanuwansa ke tsaye a kanta,mirmishi yak'i barin fuskarsa,ko yaushe in yana tare da yarinyar sai ya riski kansa cikin farin ciki.
Su'ada idanuwanta a kansa ta san sarai tunanin da yake,ko yaushe bakinsa kan maganar Nusrat yake,tasan kara yake mata kawai,don kafin ta haihu yasha fad'a mata shi fa a rayuwa bai tab'a iya yin kyautar d'a, yanda yake da son y'ay'a ba zai rink'a barin d'ansa yayi nisa da shi ba ko na sati guda.to amma ga shi yau tsawon shekara guda tun daga yaye iyayen ta sun rik'e Nusrat,kuma ko ita akan kanta tana jin k'aunar kasancewa da yarinyar tare da ita,amma ba zata iya cewa zata karb'eta ba in ba su suka dawo da ita ba.
*******Ana kiran Sallar la'asar Khaleelee ya mik'e da Nusrat a jikinsa yana fad'in "Mamana bari naje salla."
Mak'ale kafad'a ta yi tana k'ara shegewa jikinsa.
Da yai zaton wasa ne abun,amma da ya fara k'ok'arin sauketa k'asa sai ta k'ara rik'eshi cikin b'ata fuska tace"Zanje fa."
Komawa ya yi ya zauna a kujera yana y'ar dariya yace"Zauna, in naje masallaci na dawo zan d'aukeki muje yawo."
Kuka ta fara yi sosai,abunda ya sa Khairiyya fitowa daga d'aki da sauri don cikin bacci ta jiyo kukanta.
"Me ya faru take wannan kukan?"
Su'ada dariya tace "wai masallaci zata bishi, kullum kuyi ta cewa y'ar Ku bata rigima to gashi tayi mun gani."
B'ata fuska Khairiyya tai kafin tace "wallahi ba ta rigima,in kinji Ku kanta da dalili,shi yasa da naji kukan na tashi da sauri."
Jin an fara tada sallar ya sa da sauri Khaleelee ya mik'e da ajiye ta kan kujera ya shige ban d'aki don d'aura alwala.
Sosai fa Nusrat take kuka,ita dole zata bi Abbanta.
Khairiyya ta d'auketa tana rarrashinta,ita kuwa Su'ada tashi tai don yin salla ta barsu wajan.
Har khaleelee ya dawo a salla tana kuka,hakan ya sa yace Khairiyya tasa mata kaya yaje da ita shagonsa,in ta fito sai ta tsaya ta karb'eta.
Jakarta ta bud'e ta d'auko mata wata y'ar doguwar riga Mara hannu.
Nan da nan tai mata y'ar kwalliya ta shafeta da farar powder sabida zafin da ake,sannan ta canja mata Pampers.
Yana d'aukan ta ta fara dariyar murna,shima dariyar ya yi,yana fad'in "Yau dai Mamana ta zama Muklees sarkin rigima."
Su'ada tace"Ah daman da kukanta,kawai tana dad'ewa ne batai ba,ba Muklees ne kad'ai akoke ba."
Fita yayi sab'e da ita yana dariya yace "Khairiyya sai kin fito."
Ta amsa mishi da to.
A tsakar gida Sakeena taga Khaleelee d'auke da Nusrat ta kalleta da sabuwar kwalliyar sa akai mata,ta had'iye wani yawu kafin tace "Nusrat kukan me take ne? Naji ihunta ina salla."
Khaleelee yana sa kai zai fita yace"Rigima take wai in fita da ita."
Daga haka ya fice.
Ita kuma ta tab'e baki cikin ranta take cewa 'To in banda ma abu yarinya da gidan ubanta amma an barta gidan kakanni,sabida son abun duniya da kwad'ayi kawai.'
Ba Wanda ya jita balle ya bata amsa,ita kad'ai take ta nunk'ufurcinta kamar y'arta.
***
Shi kuwa Khaleelee tunda yaje da Nusrat shago yaran shagon keta fad'in "kai masha Allah, wai haka ta girma."
Sosai ta ware dashi a shagon tana ta mai gwaranci.
Wani kanti Dan gefen shagonsu ya shiga yayi mata siyaugar biscuit da alawowi.ta sha kad'an bacci ya d'auketa. Ya kwantar da ita a cinyarsa yana d'an pitting bayanta.
Sai wajan k'arfe shida da mintina Khairiyya ra tsaya a adaidaita tanaiwa Khaleelee magana.
Tasowa yayi ya kawo mata Nusrat d'in yana fad'in "Khairi Wannan yarinyar taki yau ta had'a ni da aiki,kinga da zuwanmu fa tai bacci."
Dariya Khairiyya tai bayan ta gyara mata zama a jikinta tace"Um a bani abata,duk kunsa tai kuka da yawa daga zuwanmu gidanku."
Dariya yai lokacin da yake bata ledar da yayiwa Nusrat d'in siyayya,sannan ya d'aga mata hannu yana cewa ta gaida mama.
*****
Bayan sallar magriba a gudansu Su'ada, duk suna zaune falo don cin abincin dare,Mama ta dubi Khairiyya tana cewa "Wai ya akai Nuarat tai miki bacci a hanya ne yau?"
Gyad'a kai Khairiyya tai tana cewa"Kuka ta sha,shine kuma sai tai bacci."
"Wane irin kuka kuma?abunda ba cinikinta ba."
Cewar mama.
Nan Khairiyya ta basu labarin sanadin kukan.
Mama tace "Ai da kin barta ta kwana biyu,ko zuwa jibi sai a d'auko ta."
Zare ido Khairiyya tai da fad'in "Tab' d'in, haka kawai da ga nan suce sun rik'e ta."
Da mamaki maman ke kallonta tace "Ah to in sun raketa ma ba y'ar su bace, ko daman kunyi da su sun ce miki kyauta su ka bamu?"
Turo baki Khairiyya tai,don zancen bai mata ba,Jiddah dai kam sai dariya take,mamy me bin Khairiyya tace "A'a wallahi mama,ba mai d'auke mana ita,sai da ta shak'u da mu,muma muka shak'u da ita,sannan sai su d'auke ta,tab' d'in, ai Wallahi nasan Abba ma ba zai yarda ba."
Khairiyya dai cirewa Nusrat kayan tai gaba d'aya, ta barta daga ita sai base da d'an pant,dake daman zafi ake sosai a lokacin.
Bayan Su'ada ta d'auko muklees ta zauna kusa da Khairiyyan tana fad'in "Uwar masifa ko gaisawa ba muyi ba fa."
Y'ar dariya Khairiyyan tai kafin ta gaida ta,tana tsokanar Muklees "Su Abbanmu sarkin kuka sarkin tsotso."
Harararta Su'ada tai da fad'in"Abban ake cewa sarkin kuka ko?"
Cikin dariya Khairiyya tace "To ai ba k'arya nai ba,jifa daga farkawa daga bacci ya cika gari da kuka,yasin yaron nan badan sunan Abbanmu gareshi ba bazan had'a jam'iyya dashi ba."
"To karki had'a mana,ni ina had'e da Abuna,kin fi son ki ganshi salo salo kamar y'arku,ah Allah ya kiyaye, Abbana namijin duniya ne me k'arfin sojoji."
Khairiyya na dariya ta d'ora Nusrat akan cinyarta tana fad'in "Ai Wallahi yarinyata bata da makusa, d'abiun ta kalar na mata,jan aji da nutsuwa ne yasa bata hayaniya tun tana jinjira, komai nata cikin class take,amma wannan Abban ai kalar garada ne."
Ta kai k'arshen zancen da dariya sosai.
Yatsina Fuska Su'ada tai tana kallon kayan da aka cirewa Nusrat d'in tace "Wai don wulak'ancinku kawai don ta d'an goga mata maik'o shine kuka cire kayan? Yasin baki da kara fa."
D'age gira Khairiyya tai da watsa hannu alamar ko a jikinta tace "To akan me zan barta da kaya me datti a jiki? Ah haba wai baki da labarin y'ata me tsada ce ne?"
Mik'ewa Su'ada tai tana dire muklees a kan cafet,ta wuce kitchen, don bata dad'e da dawowa daga makaranta ba,don ma yara exam's suke da wuri suke tashi
Girkin data d'ora taje ta duba,sannan ta dawo suka d'ora hira.
Sallamar Baby ce tasa su tsayawa da hirar suna amsa mata,da fara'arta ta k'araso tana fad'in "Yanzun nan ina shigowa Islam tace min Nusrat tazo."
Tsugunnawa tai tana kamo hannun yarinyar,tana gaida Khairiyya, sannan ta dauketa zasu fita Muklees yasa kuka yana mik'awa Babyn hannu.
Tafa hannu Su'ada tai da fad'in "Eh lalle Baby,sabida kinga Nusrat shine zaki wulak'anta min uba,to ai zata tafi ta barmu da ke ne."
Dariya Babyn tai tana jutowa ta d'auki muklees d'in a d'aya hannunta.
bayan Sun fita Khairiyya tace "Allah sarki Baby,Wallahi sam ba tai halin Uwarta ba,yarinyar na birgeni."
Gyad'a kai Su'ada tai tace "Ita kam halin Babanta tai,ba ruwanta,rayuwar ta komai da sauk'i take yinsa."
Daga wannan hirar suka koma hirar bikin Jiddah, Wanda ya rage wata biyu.
******
Baby dai na can d'akinsu tana ta fama da su Muklees, musamman Nusrat da take ta hannun damanta,sai ina naka sa ina naka aje take da yarinyar.
*********K'arfe daya da rabi Khaleelee ya dawo gida don yin shirin sallar jummaa,dake su masallacin murtala suke bi,kuma sai k'arfe biyu ake salla a masallacin.
A tsakar gida ya tarda Baby ta na goye da Muklees, tana bawa Nusrat abinci a baki,cikin mirmishi yake amsa sannu da zuwan da yaran ke masa.
Rik'o hannun Nusrat d'in ya yi yana fad'in "Mamana yau an waiwayomu kenan, ke da wa kuka zo?"
Cikin gwarancinta tace "Aunty Khairiyya ne."
Gyad'a kai ya yi yana mik'awa Islam hannu su ka tafa,yace "Maman mama me aka ci ne baki ke maik'o
"
Girgiza kai tai cikin dariya tace "Abinci muka ci fa me dad'i."
Yana y'ar dariya ya wuce ciki.
A falo ya same su suna cin abunci,Khairiyya ta gaisheshi ya amsa yana tsokanarta don Bayan Khaleelee cikin y'an gidan yafi wasa da Khairiyya.
Kad'an ya d'an zauna yana tambayarta gida dasu mama, sannan ya wuce d'aki.
Bin bayansa Su'ada tai zuwa d'akin, yana k'ok'arin rage kayan jikinsa yace "Madam a had'a min ruwa,ji nake kamar ban tab'a wanka ba,gaskiya yau ana zafi sosai."
Taimaka mishi tai ya cire kayan jikinsa zuwa jallabiya.sannu ta fito ta had'a mishi ruwan wanka.
Sai wajan k'arfe uku Khaleelee ya dawo gidan daga masallaci.
Khairiyya na d'aya d'aki tana bacci, yayin da Su'ada ke falo tana marking exam's d'in d'alibai, Muklees ma baccin yake sai Nusrat a gefenta tana mata hirarsu ta yara.
Zama ya yi kan kujera yana amsa sannu da zuwan Su'ada, idonsa naga Nusrat,sosai yake kallon yarinyar yana ganin kullum k'ara girma take,dukda yana wata guda ko giye bai ganta ba,amma duk sanda zai ganta sai yaga tai tsayi.
Yana wannan tunanin har Su'ada ta kawo mishi abinci.bayan ya sauko k'asa inda zai ci abincin yace "Mamana zo mu ci abincin ."
Girgiza Kai tai alamun ta k'oshi, mirmishi kan fuskarsa yace " Su'ada yarinyar nan ta kusa kamoki a tsayi fa."
Dariya Su'ada tai kafin tace "Tunda tai gadon tsayi ai in ma ta fini tsayin ba damuwa bace."
D'agata yai cas ya d'ora ta kan cinyarsa,wani k'aunar yarinyar yake ji na ratsa b'argo da jijiyarsa,tabbas kara da kawaici ne kawai ba za su barshi yace a dawo mai da y'arsa gida ba.ya San yanda ake kula da ita a can ko gidan ma sai haka,to amma fa shima ya na buk'atarta kusa da shi.
Wasa take tayi da gaban rigarsa ,yayin da idanuwansa ke tsaye a kanta,mirmishi yak'i barin fuskarsa,ko yaushe in yana tare da yarinyar sai ya riski kansa cikin farin ciki.
Su'ada idanuwanta a kansa ta san sarai tunanin da yake,ko yaushe bakinsa kan maganar Nusrat yake,tasan kara yake mata kawai,don kafin ta haihu yasha fad'a mata shi fa a rayuwa bai tab'a iya yin kyautar d'a, yanda yake da son y'ay'a ba zai rink'a barin d'ansa yayi nisa da shi ba ko na sati guda.to amma ga shi yau tsawon shekara guda tun daga yaye iyayen ta sun rik'e Nusrat,kuma ko ita akan kanta tana jin k'aunar kasancewa da yarinyar tare da ita,amma ba zata iya cewa zata karb'eta ba in ba su suka dawo da ita ba.
*******Ana kiran Sallar la'asar Khaleelee ya mik'e da Nusrat a jikinsa yana fad'in "Mamana bari naje salla."
Mak'ale kafad'a ta yi tana k'ara shegewa jikinsa.
Da yai zaton wasa ne abun,amma da ya fara k'ok'arin sauketa k'asa sai ta k'ara rik'eshi cikin b'ata fuska tace"Zanje fa."
Komawa ya yi ya zauna a kujera yana y'ar dariya yace"Zauna, in naje masallaci na dawo zan d'aukeki muje yawo."
Kuka ta fara yi sosai,abunda ya sa Khairiyya fitowa daga d'aki da sauri don cikin bacci ta jiyo kukanta.
"Me ya faru take wannan kukan?"
Su'ada dariya tace "wai masallaci zata bishi, kullum kuyi ta cewa y'ar Ku bata rigima to gashi tayi mun gani."
B'ata fuska Khairiyya tai kafin tace "wallahi ba ta rigima,in kinji Ku kanta da dalili,shi yasa da naji kukan na tashi da sauri."
Jin an fara tada sallar ya sa da sauri Khaleelee ya mik'e da ajiye ta kan kujera ya shige ban d'aki don d'aura alwala.
Sosai fa Nusrat take kuka,ita dole zata bi Abbanta.
Khairiyya ta d'auketa tana rarrashinta,ita kuwa Su'ada tashi tai don yin salla ta barsu wajan.
Har khaleelee ya dawo a salla tana kuka,hakan ya sa yace Khairiyya tasa mata kaya yaje da ita shagonsa,in ta fito sai ta tsaya ta karb'eta.
Jakarta ta bud'e ta d'auko mata wata y'ar doguwar riga Mara hannu.
Nan da nan tai mata y'ar kwalliya ta shafeta da farar powder sabida zafin da ake,sannan ta canja mata Pampers.
Yana d'aukan ta ta fara dariyar murna,shima dariyar ya yi,yana fad'in "Yau dai Mamana ta zama Muklees sarkin rigima."
Su'ada tace"Ah daman da kukanta,kawai tana dad'ewa ne batai ba,ba Muklees ne kad'ai akoke ba."
Fita yayi sab'e da ita yana dariya yace "Khairiyya sai kin fito."
Ta amsa mishi da to.
A tsakar gida Sakeena taga Khaleelee d'auke da Nusrat ta kalleta da sabuwar kwalliyar sa akai mata,ta had'iye wani yawu kafin tace "Nusrat kukan me take ne? Naji ihunta ina salla."
Khaleelee yana sa kai zai fita yace"Rigima take wai in fita da ita."
Daga haka ya fice.
Ita kuma ta tab'e baki cikin ranta take cewa 'To in banda ma abu yarinya da gidan ubanta amma an barta gidan kakanni,sabida son abun duniya da kwad'ayi kawai.'
Ba Wanda ya jita balle ya bata amsa,ita kad'ai take ta nunk'ufurcinta kamar y'arta.
***
Shi kuwa Khaleelee tunda yaje da Nusrat shago yaran shagon keta fad'in "kai masha Allah, wai haka ta girma."
Sosai ta ware dashi a shagon tana ta mai gwaranci.
Wani kanti Dan gefen shagonsu ya shiga yayi mata siyaugar biscuit da alawowi.ta sha kad'an bacci ya d'auketa. Ya kwantar da ita a cinyarsa yana d'an pitting bayanta.
Sai wajan k'arfe shida da mintina Khairiyya ra tsaya a adaidaita tanaiwa Khaleelee magana.
Tasowa yayi ya kawo mata Nusrat d'in yana fad'in "Khairi Wannan yarinyar taki yau ta had'a ni da aiki,kinga da zuwanmu fa tai bacci."
Dariya Khairiyya tai bayan ta gyara mata zama a jikinta tace"Um a bani abata,duk kunsa tai kuka da yawa daga zuwanmu gidanku."
Dariya yai lokacin da yake bata ledar da yayiwa Nusrat d'in siyayya,sannan ya d'aga mata hannu yana cewa ta gaida mama.
*****
Bayan sallar magriba a gudansu Su'ada, duk suna zaune falo don cin abincin dare,Mama ta dubi Khairiyya tana cewa "Wai ya akai Nuarat tai miki bacci a hanya ne yau?"
Gyad'a kai Khairiyya tai tana cewa"Kuka ta sha,shine kuma sai tai bacci."
"Wane irin kuka kuma?abunda ba cinikinta ba."
Cewar mama.
Nan Khairiyya ta basu labarin sanadin kukan.
Mama tace "Ai da kin barta ta kwana biyu,ko zuwa jibi sai a d'auko ta."
Zare ido Khairiyya tai da fad'in "Tab' d'in, haka kawai da ga nan suce sun rik'e ta."
Da mamaki maman ke kallonta tace "Ah to in sun raketa ma ba y'ar su bace, ko daman kunyi da su sun ce miki kyauta su ka bamu?"
Turo baki Khairiyya tai,don zancen bai mata ba,Jiddah dai kam sai dariya take,mamy me bin Khairiyya tace "A'a wallahi mama,ba mai d'auke mana ita,sai da ta shak'u da mu,muma muka shak'u da ita,sannan sai su d'auke ta,tab' d'in, ai Wallahi nasan Abba ma ba zai yarda ba."