Sashe 24
Facala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kauda kai gefe tai tana d'an dariya tace "Wannan kallon kamar za'a siyeni ."
Lumshe ido yai ya bud'e yana y'ar dariyar shima ya bata amsa da "Hhhmmmm siya kuma na nawa? An siya an biya har an jujjuya an sami ribar farko gata a kwance."
Mik'ewa tai tana saka doguwar rigar data d'auko mara nauyi kuma bata da Babban hannu,yana tsaye yana kallo ta gama sawa sannan ya k'araso cikin d'akin sosai yana k'arasawa ga bakin gadon yanawa Nusrat wasa da wak'a. "Mamana tafi ta kowa, Mamana sarkin kuka,amma kukan ma da dalili,Mamana y'ar albarka,Mamana Ummyn Abba."
Juyowa tai da mamaki tana kallonasa kafin tace "yaushe ka fara wak'a?"
Dariya yai bayan ya zauna sosai ya d'auki Nusrat Sannan yace "Tun ranar da na zama Abba."
Jijjiga kai tai da d'an mirmishi tace "Ba ruwana, Allah yasa wani ya jika kanaiwa y'ar fari wak'a."
Sosai maganar ta bashi dariya,sai da yai mai isarsa sannan yace"Ke in bakiyi ni bani waje,ko a gaban Baba zan mata wak'a da rawa."
Zaro ido tai da fad'in "La' ni kam ba ruwana Wallahi, ni ka fita ma kar aga kazo ka dad'e a d'akin ayi wani tunanin."
Bai kara tanka mata ba ya ci gaba da yiwa yarinyarsa wasa harda kwanciya kan gadon, ita kam Su'ada data gaji da magiyar ya fita yak'i sai ra fito ta bar mai d'akin. A falo a tadda Aunty Bulkisu na ta sharewa su kam su Innaro na tsakar gida.tace Aunty sannunku da aiki,da kun huta ma da safe ai kwayi."
"A'a k'ara mu rage yanzu, kuma shara ma ai ba'a barta ta kwana ba,kina ganin fa yanda duk wajan ya jagale,ki koma d'aki don moping zan yi."
"To sannunku da aiki" ta fad'a tana komawa d'akin.
Jan stool tai ta zauna bakin gadon tana kallonsa na d'an lokaci sannan ta lumshe ido. Shima kallontan yai ya kauda kai da fad'in "da ganin Wannan kallon na kewa ta ne."
Turo baki tai kamar zatai kuka tace "Ni bance ba,gaskiya ka bari,kawai don na kalleka sai ya zama abun fassara."
Ajiye Nusrat yai ya taso zuwa Inda take,d'an rank'wafowa yai saitin fuskarta yana magana can k'asa "Ko baki fad'a ba yarinya na gani cikin idonki, kuma duk abunda ido ya nuna gaskiya ne."
Yana fad'i ya mik'ar da ita tsaye tare da rungumeta,maimakon ta tureshi yanda take mai tunda akai haihuwar sai yaga sab'anin haka,don lif tai a k'irjinsa tana sauke tagwagen ajiyar zuciya.
Shafa bayanta ya ke a hankali yana jin wani bala'in bukatarta na taso mai,idonsa a lumshe yake ta sansana gashin kanta dayasha gyara yana bada k'amshi.
Sun dad'e a haka,maganganun su Innaro da sukaji a falon yasa su sakin juna a d'an hanzarce,Innaro da bata San Khaleelee yana wannan d'akin ba don tasan bai shigowa yana can dayan d'akin, ta turo k'ofa da sallama,ganin Khaleelee tsaye Su'ada zaune kan stool a gabansa yasa da sauri ta juya.
Shima da saurin ya d'auki Nusrat ya biyo bayanta,a d'an kunyace yace "Inna sannunku,ya gajiyar taro data aiki?.
Cikin kulawa ta amsa mai da " Alhamdulillah. "
Dayan d'akin da ya zama makwancinsa yanzu ya shige,bayan ya ajiye Babyn a gado ya cire kayan jikinsa tare da kwanciya ya d'ora ta a cikinsa yana d'an shafa bayanta don bacci take.
A d'aki kam cikin hikima Innaro ke k'ara jawa Su'ada kunne kan kame jikinta daga Miji,a dabara take ta bata labarin rayuwar su ta da,yanda mace ke gujewa miji a duk sanda take jego har sai tai arba'in ko dama da haka ma.duk da bata bayyana zancen akan Su'adan ba amma ita tasan da ita take,sabida yanayin data riskesu d'azu duk wanda ya gansu yasan da magana.
********Washe garin suna y'an uwan Su'ada suka gyara nama suka soyeshi,bayan sun gama suka rarraba shi kamar yanda akeyi,kowa dake da hakki aka fidda mishi rabonsa.
A ranar su Aunty Bilkisu duk suka tafi,gida ya koma daga Su'ada sai Innaro.
********Jego me tsafta Su'ada keyi da Babyn ta,ba zaka taba shigowa wajanta ka sami wani abu na k'i ba,kullum cikin ado take da k'amshi, haka ma Nusrat, Baby kam ta zama y'ar raino,data dawo makaranta take yada zango taita fama da goyo.
Bayan Su'ada tai shawara da Khaleelee ta had'a kud'ad'an data samu na barka dubu 700 tacewa mai tana son siyawa Nusrat d'an kunne,bai k'i ta tata ba amma yace tasa dubu hamsin a account d'inta, dubu ashirin kuma tasai mata k'arami,a gaba in ta k'ara girma sai tasai mata babba. ba gaddama ta yarda da shawararsa,ta aikawa mama kud'in aka siyowa Nusrat d'an k'aramin d'an kunne.
*******A yanzu kam Sakeena sai dai ace Masha Allah, don tunda akai haihuwar nan bata nuna wani halinta ba,ta nutsu tai komai kamar yanda ya kamata,duk da dai abubuwa da yawa a lokacin sun sosa ranta,yanda akai komai kamar sunan wata y'ar attajirai.
Su'ada a ranta take fad'in Ashe duk mugun halin FACALA tana da rana,ita kam taga ranar FACALA a lokacin da haihuwa tazo mata,don Sakeena ta taimaka mata sosai,har addu'a Su'ada keyi Allah yasa Sakeena ta gyara halinta kenan, zasu zauna kamar yanda sauran facaloli je zama da junansu.
*Taku ce*
*Y'ar mutan Ja'oji*🙋
[2/24, 12:03 AM] LAYUZA KABIR: 👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
_*page*_*41-42*
A sannu kwanaki suke ja,yau ya rage kwana uku Su'ada tai arba'in,suna ta shirye shiryen zuwa gida suyi kwana biyu sannan su zagaya dangi,zuwa Yanzu kam Nusrat kamarta da mamanta k'ara fitowa take sosai,har rashin k'iba na Su'ada ne,sai tsayi fa Masha Allah ta d'auko Khaleelee don kana d'aukanta zaka tabbatar da doguwar yarinya ce ita,sab'anin Su'ada da bata da tsayi bata da k'iba.
A iya tsakankanin Khaleelee ya bud'ewa Su'ada wuta ko yaushe fad'a mata yake hak'urinsa ya k'are amma ita kam ta kafe mai sai Innaro ta bar gidan zata iya kula dashi,don tasan yanda kullum Innaro ke fad'a Mata tayi taka tsantsan da shigewa namiji a Lokacin da take jego dukda ta sami tsarki amma taki yarda dashi.
Ranar da sukai arba'in ta zaga dangin Khaleelee duk da suke kusa tai musu yawon arba'in, washe gari kuwa suka wuce gidansu Wanda a ranar Innaro tai sallama dasu gaba d'aya.
Sun sami kwana biyu a gida suna zaga dangi, ranar da suka kwana biyun da dare yazo ya dauketa.
Ta shirya mai tsaf don itama tai kewarsa,don haka batai sanya ba wajan sa hannu bibbiyu ta amshi mijinta.
************
Lokacin da Nusrat ta shiga wata biyu dai dai Su'ada ta koma bakin aikinta,a Lokacin kuma hidima tai mata yawa,amma haka take tsara komai cikin lokutanta.bata shiga hakkin mijinta dana yarta sabida aiki.wannan yasa kullum Khaleelee ke k'ara bata kwarin gwiwa kuma yake taimaka mata da dukka ayyukan gida.
To tsakanin Sakeena da Su'ada ba yabo ba fallasa, zaman ya dawo irin na farko,don lokuta da
dama Su'ada tana ganin Abu sai dai ta kauda kai,musamman kan yanda Baby Ke kulafacin d'aukan Nusrat, wani lokaci tana ji za taita mata fad'a kan yawon goyon da takewa Nusrat d'in wai k'irjinta zai bud'e, sosai ran Su'ada ke soyuwa amma sai ta danne,wani lokaci har sai tayi kamar zata hana yarinyar d'aukan ta amma sai ta fasa,don yanda baby ke nacin Nusrat d'in ba magana.
Wata ranar Asabar da safe Sakeena na tsakar gida tana aiki, tacewa Baby ta kawo mata robar magi a falo,Baby ta amsa amma bata kawo ba har wajan mintina biyu,Sakeena ta k'ara magana,sannan ta fito tana gyara goyon Nusrat da ke bayanta, cikin fishi Sakeena ta kawo mata duka da fad'in "Kina goyon k'anwar uwarki dole nayi magana ki share ai, ta bud'e baki zatai magana ta k'ara kai mata bugu,tai baya da sauri hakan yasa kan Nusrat buguwa a bango,karar data tsanyara yasa Su'ada dake tsakar gidanta tana aiki sannan tana jin duk abunda su keyi ta fito da sauri,da azama ta k'arasa ga Baby wadda duk ta gigice tana ta jijjiga yarinya tace " Aunty Wallahi ban sani ba,mama ce za ta dakeni nai baya shine na bugeta."
D'an mirmishi Su'ada tai bayan ta kwance ta a bayanta tace "Karki damu,ai nasan da ganganci ba zaki bigeta ba Baby."
Wajanta ta shige zuciyarta na mata k'una,bayan ta rarrashi yarinyar tai shiru sannan ta sauke ajiyar zuciya tana shafa mata kai,a ranta take mamakin wai meye dalilin da yasa Sakeena tsangwamar Baby don tana d'awainiya da Nusrat,tabbas tasan sarai da Sakeena nada iko da tuni ta hana Baby jigilar d'aukan yarinyar. Amma ya zama dole ta d'au mataki,duk nacin Baby zata daina bata Nusrat tunda uwarta bata son hakan. "
******
Da Rana Khaleelee ya dawo cin abinci ya kula sam Su'ada bata da walwala, don haka ya ajiye cokalin da ya d'ebo abincin ya zuba mata ido,kanta da ke k'asa ta d'ago don taji alamun kallona ta yake,d'an mirmishi tai tana kauda kai gefe,bai d'auke idonsa a kanta ba haka bai ce mata uffan ba,gajiya tai don kanta tace "Wai wannan kallonfa?"
Janye plat d'in abincin yai daga tsakiyarsu tare da rik'o hannunta ya d'an matsa cikin nashi.
Sanyaya murya yai sosai ya fara magana"meye matsalarki? Na hango damuwa tare dake."
Sosai tai k'ok'arin wadata fuskarta da fara'a kafin tace"Ba abunda kW damuna, kawai ban jin dad'in yanayin ne Yau. "
Cikin kallon ban yarda dake ba ya k'ara fad'in "Damuwar dake kan fuskar ki tafi k'arfin ace rashin jin dad'in jiki ne ya saki haka,ki fad'a matsalar ki Su'ada, ko akwai wanda yafi cancanta da jin matsalar ki sama da mijinki?*
Girgiza kai tai cikin sanyi tace " Kasan me? Wallahi Nusrat ce ta buge d'azu,kukan da tai da yawa shi yasa duk zuciyata tamin rashin dad'i. "
Zaro ido yai da fad'in "Wane irin bigewa?garin yaya hakan ta faru?"
D'an motsa hannunta dake cikin nasa tayi kafin tace "tsautsayi,a bayana take nazo shiga kitchen na bugeta,ta bugu sosai ,tai kuka da yawa,shi Yasa duk jikina ya mutu ."
Tashi yai a hankali zuwa kujerar da yarinyar ke kwance tana bacci ya d'aukota tare da zama yana dudduba fuskarta zuwa jikinta.d'agowa yai yana kallon Su'ada da d'an mirmishi yace "Da sauk'i ai,ki kwantar da hankalinki kinji."
Gyad'a kai nai nima ina d'an mirmishin.
Lumshe ido yai ya bud'e yana y'ar dariyar shima ya bata amsa da "Hhhmmmm siya kuma na nawa? An siya an biya har an jujjuya an sami ribar farko gata a kwance."
Mik'ewa tai tana saka doguwar rigar data d'auko mara nauyi kuma bata da Babban hannu,yana tsaye yana kallo ta gama sawa sannan ya k'araso cikin d'akin sosai yana k'arasawa ga bakin gadon yanawa Nusrat wasa da wak'a. "Mamana tafi ta kowa, Mamana sarkin kuka,amma kukan ma da dalili,Mamana y'ar albarka,Mamana Ummyn Abba."
Juyowa tai da mamaki tana kallonasa kafin tace "yaushe ka fara wak'a?"
Dariya yai bayan ya zauna sosai ya d'auki Nusrat Sannan yace "Tun ranar da na zama Abba."
Jijjiga kai tai da d'an mirmishi tace "Ba ruwana, Allah yasa wani ya jika kanaiwa y'ar fari wak'a."
Sosai maganar ta bashi dariya,sai da yai mai isarsa sannan yace"Ke in bakiyi ni bani waje,ko a gaban Baba zan mata wak'a da rawa."
Zaro ido tai da fad'in "La' ni kam ba ruwana Wallahi, ni ka fita ma kar aga kazo ka dad'e a d'akin ayi wani tunanin."
Bai kara tanka mata ba ya ci gaba da yiwa yarinyarsa wasa harda kwanciya kan gadon, ita kam Su'ada data gaji da magiyar ya fita yak'i sai ra fito ta bar mai d'akin. A falo a tadda Aunty Bulkisu na ta sharewa su kam su Innaro na tsakar gida.tace Aunty sannunku da aiki,da kun huta ma da safe ai kwayi."
"A'a k'ara mu rage yanzu, kuma shara ma ai ba'a barta ta kwana ba,kina ganin fa yanda duk wajan ya jagale,ki koma d'aki don moping zan yi."
"To sannunku da aiki" ta fad'a tana komawa d'akin.
Jan stool tai ta zauna bakin gadon tana kallonsa na d'an lokaci sannan ta lumshe ido. Shima kallontan yai ya kauda kai da fad'in "da ganin Wannan kallon na kewa ta ne."
Turo baki tai kamar zatai kuka tace "Ni bance ba,gaskiya ka bari,kawai don na kalleka sai ya zama abun fassara."
Ajiye Nusrat yai ya taso zuwa Inda take,d'an rank'wafowa yai saitin fuskarta yana magana can k'asa "Ko baki fad'a ba yarinya na gani cikin idonki, kuma duk abunda ido ya nuna gaskiya ne."
Yana fad'i ya mik'ar da ita tsaye tare da rungumeta,maimakon ta tureshi yanda take mai tunda akai haihuwar sai yaga sab'anin haka,don lif tai a k'irjinsa tana sauke tagwagen ajiyar zuciya.
Shafa bayanta ya ke a hankali yana jin wani bala'in bukatarta na taso mai,idonsa a lumshe yake ta sansana gashin kanta dayasha gyara yana bada k'amshi.
Sun dad'e a haka,maganganun su Innaro da sukaji a falon yasa su sakin juna a d'an hanzarce,Innaro da bata San Khaleelee yana wannan d'akin ba don tasan bai shigowa yana can dayan d'akin, ta turo k'ofa da sallama,ganin Khaleelee tsaye Su'ada zaune kan stool a gabansa yasa da sauri ta juya.
Shima da saurin ya d'auki Nusrat ya biyo bayanta,a d'an kunyace yace "Inna sannunku,ya gajiyar taro data aiki?.
Cikin kulawa ta amsa mai da " Alhamdulillah. "
Dayan d'akin da ya zama makwancinsa yanzu ya shige,bayan ya ajiye Babyn a gado ya cire kayan jikinsa tare da kwanciya ya d'ora ta a cikinsa yana d'an shafa bayanta don bacci take.
A d'aki kam cikin hikima Innaro ke k'ara jawa Su'ada kunne kan kame jikinta daga Miji,a dabara take ta bata labarin rayuwar su ta da,yanda mace ke gujewa miji a duk sanda take jego har sai tai arba'in ko dama da haka ma.duk da bata bayyana zancen akan Su'adan ba amma ita tasan da ita take,sabida yanayin data riskesu d'azu duk wanda ya gansu yasan da magana.
********Washe garin suna y'an uwan Su'ada suka gyara nama suka soyeshi,bayan sun gama suka rarraba shi kamar yanda akeyi,kowa dake da hakki aka fidda mishi rabonsa.
A ranar su Aunty Bilkisu duk suka tafi,gida ya koma daga Su'ada sai Innaro.
********Jego me tsafta Su'ada keyi da Babyn ta,ba zaka taba shigowa wajanta ka sami wani abu na k'i ba,kullum cikin ado take da k'amshi, haka ma Nusrat, Baby kam ta zama y'ar raino,data dawo makaranta take yada zango taita fama da goyo.
Bayan Su'ada tai shawara da Khaleelee ta had'a kud'ad'an data samu na barka dubu 700 tacewa mai tana son siyawa Nusrat d'an kunne,bai k'i ta tata ba amma yace tasa dubu hamsin a account d'inta, dubu ashirin kuma tasai mata k'arami,a gaba in ta k'ara girma sai tasai mata babba. ba gaddama ta yarda da shawararsa,ta aikawa mama kud'in aka siyowa Nusrat d'an k'aramin d'an kunne.
*******A yanzu kam Sakeena sai dai ace Masha Allah, don tunda akai haihuwar nan bata nuna wani halinta ba,ta nutsu tai komai kamar yanda ya kamata,duk da dai abubuwa da yawa a lokacin sun sosa ranta,yanda akai komai kamar sunan wata y'ar attajirai.
Su'ada a ranta take fad'in Ashe duk mugun halin FACALA tana da rana,ita kam taga ranar FACALA a lokacin da haihuwa tazo mata,don Sakeena ta taimaka mata sosai,har addu'a Su'ada keyi Allah yasa Sakeena ta gyara halinta kenan, zasu zauna kamar yanda sauran facaloli je zama da junansu.
*Taku ce*
*Y'ar mutan Ja'oji*🙋
[2/24, 12:03 AM] LAYUZA KABIR: 👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
_*page*_*41-42*
A sannu kwanaki suke ja,yau ya rage kwana uku Su'ada tai arba'in,suna ta shirye shiryen zuwa gida suyi kwana biyu sannan su zagaya dangi,zuwa Yanzu kam Nusrat kamarta da mamanta k'ara fitowa take sosai,har rashin k'iba na Su'ada ne,sai tsayi fa Masha Allah ta d'auko Khaleelee don kana d'aukanta zaka tabbatar da doguwar yarinya ce ita,sab'anin Su'ada da bata da tsayi bata da k'iba.
A iya tsakankanin Khaleelee ya bud'ewa Su'ada wuta ko yaushe fad'a mata yake hak'urinsa ya k'are amma ita kam ta kafe mai sai Innaro ta bar gidan zata iya kula dashi,don tasan yanda kullum Innaro ke fad'a Mata tayi taka tsantsan da shigewa namiji a Lokacin da take jego dukda ta sami tsarki amma taki yarda dashi.
Ranar da sukai arba'in ta zaga dangin Khaleelee duk da suke kusa tai musu yawon arba'in, washe gari kuwa suka wuce gidansu Wanda a ranar Innaro tai sallama dasu gaba d'aya.
Sun sami kwana biyu a gida suna zaga dangi, ranar da suka kwana biyun da dare yazo ya dauketa.
Ta shirya mai tsaf don itama tai kewarsa,don haka batai sanya ba wajan sa hannu bibbiyu ta amshi mijinta.
************
Lokacin da Nusrat ta shiga wata biyu dai dai Su'ada ta koma bakin aikinta,a Lokacin kuma hidima tai mata yawa,amma haka take tsara komai cikin lokutanta.bata shiga hakkin mijinta dana yarta sabida aiki.wannan yasa kullum Khaleelee ke k'ara bata kwarin gwiwa kuma yake taimaka mata da dukka ayyukan gida.
To tsakanin Sakeena da Su'ada ba yabo ba fallasa, zaman ya dawo irin na farko,don lokuta da
dama Su'ada tana ganin Abu sai dai ta kauda kai,musamman kan yanda Baby Ke kulafacin d'aukan Nusrat, wani lokaci tana ji za taita mata fad'a kan yawon goyon da takewa Nusrat d'in wai k'irjinta zai bud'e, sosai ran Su'ada ke soyuwa amma sai ta danne,wani lokaci har sai tayi kamar zata hana yarinyar d'aukan ta amma sai ta fasa,don yanda baby ke nacin Nusrat d'in ba magana.
Wata ranar Asabar da safe Sakeena na tsakar gida tana aiki, tacewa Baby ta kawo mata robar magi a falo,Baby ta amsa amma bata kawo ba har wajan mintina biyu,Sakeena ta k'ara magana,sannan ta fito tana gyara goyon Nusrat da ke bayanta, cikin fishi Sakeena ta kawo mata duka da fad'in "Kina goyon k'anwar uwarki dole nayi magana ki share ai, ta bud'e baki zatai magana ta k'ara kai mata bugu,tai baya da sauri hakan yasa kan Nusrat buguwa a bango,karar data tsanyara yasa Su'ada dake tsakar gidanta tana aiki sannan tana jin duk abunda su keyi ta fito da sauri,da azama ta k'arasa ga Baby wadda duk ta gigice tana ta jijjiga yarinya tace " Aunty Wallahi ban sani ba,mama ce za ta dakeni nai baya shine na bugeta."
D'an mirmishi Su'ada tai bayan ta kwance ta a bayanta tace "Karki damu,ai nasan da ganganci ba zaki bigeta ba Baby."
Wajanta ta shige zuciyarta na mata k'una,bayan ta rarrashi yarinyar tai shiru sannan ta sauke ajiyar zuciya tana shafa mata kai,a ranta take mamakin wai meye dalilin da yasa Sakeena tsangwamar Baby don tana d'awainiya da Nusrat,tabbas tasan sarai da Sakeena nada iko da tuni ta hana Baby jigilar d'aukan yarinyar. Amma ya zama dole ta d'au mataki,duk nacin Baby zata daina bata Nusrat tunda uwarta bata son hakan. "
******
Da Rana Khaleelee ya dawo cin abinci ya kula sam Su'ada bata da walwala, don haka ya ajiye cokalin da ya d'ebo abincin ya zuba mata ido,kanta da ke k'asa ta d'ago don taji alamun kallona ta yake,d'an mirmishi tai tana kauda kai gefe,bai d'auke idonsa a kanta ba haka bai ce mata uffan ba,gajiya tai don kanta tace "Wai wannan kallonfa?"
Janye plat d'in abincin yai daga tsakiyarsu tare da rik'o hannunta ya d'an matsa cikin nashi.
Sanyaya murya yai sosai ya fara magana"meye matsalarki? Na hango damuwa tare dake."
Sosai tai k'ok'arin wadata fuskarta da fara'a kafin tace"Ba abunda kW damuna, kawai ban jin dad'in yanayin ne Yau. "
Cikin kallon ban yarda dake ba ya k'ara fad'in "Damuwar dake kan fuskar ki tafi k'arfin ace rashin jin dad'in jiki ne ya saki haka,ki fad'a matsalar ki Su'ada, ko akwai wanda yafi cancanta da jin matsalar ki sama da mijinki?*
Girgiza kai tai cikin sanyi tace " Kasan me? Wallahi Nusrat ce ta buge d'azu,kukan da tai da yawa shi yasa duk zuciyata tamin rashin dad'i. "
Zaro ido yai da fad'in "Wane irin bigewa?garin yaya hakan ta faru?"
D'an motsa hannunta dake cikin nasa tayi kafin tace "tsautsayi,a bayana take nazo shiga kitchen na bugeta,ta bugu sosai ,tai kuka da yawa,shi Yasa duk jikina ya mutu ."
Tashi yai a hankali zuwa kujerar da yarinyar ke kwance tana bacci ya d'aukota tare da zama yana dudduba fuskarta zuwa jikinta.d'agowa yai yana kallon Su'ada da d'an mirmishi yace "Da sauk'i ai,ki kwantar da hankalinki kinji."
Gyad'a kai nai nima ina d'an mirmishin.