Sashe 13
Facala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hankakinsa ba ga abincin sa yace " Sa Hijab d'inki ki je ki kai mai."
D'aki ta koma ta d'aura zani sannan ta saka katon hijab ta fito,binta yai da kallo harta fita a falon.
A tsakar gida ta same shi ya na cin sauran abincin da ta kaiwa Baba,cikin fara'a ya d'ago ya na fad'in "Aunty na barka da gida ."
"Sannu da dawowa, ga abincin ka harka fara cin wani,amma wannan taliya ne fa."
"Wallahi kinga yunwa na ke ji ,kuma Maman Abba bata k'arasa ba kawai na d'auko sauran na Babah,amma kawo taliyar ma duk zata shiga ai,kin san cikina na maza ne ba kalar na angonki ba."
Ya k'arasa da tsokana,
Dariya tai ta ajiye mai kulan ta na fad'in "Ba ruwana ai ya na jiyo ka."
Sakeena ta saki wani tsaki tana fifita wuta.
Juyowa tai ta kalleta har za tai magana taga ta wani d'aure fuska,don haka bata tanka ba ta juya ta koma wajanta.
Bayan sallar Magriba Su'ada na kwance jikin Ibrahim ya kamo kunnanta yana magana k'asa k'asa " Ke ce kika bada damar a kunna ice a gidan nan ko?"
Rik'e hannun da ya kama mata kunnan tai cikin kukan shagwab'a tace "Wayyo Allah, Abbana mamana,kun kawo ni za'a cire muku kunne na."
Sosai maganar ta bashi dariya yace "Yanzu wannan kunnan ai nawa ne,ko na cire ni zan yi kuka, amma kin San me?"
"Um um sai ka fad'a."
"Ban san inga ana kunna ice a gidan nan tun asali,sabida matar gidan tana da rauni wajan gyarawa,in ta kunna ice sai ki ga duk gidan ya fita hayyacinsa, don haka ma shi kansa Yaya Muktar ya hana,sai gawayi ta ke amfani da shi,to d'azu da nazo naga ta kunna ice nace ga gawayi me yasa ta kunna ice ,shine tace wai ya k'i kamawa sai kika ce ta kunna icen kawai."
Gyara kwanciya tai a jikinsa tans wasa da gashin da ke kwance a Hannayensa,
Cikin sanyin murya tace " Ka kan wani abu ne? Gawayin da take amfani da shi bai ci,ya sha ruwa kuma lokaci na ta k'urewa ba ta d'ora girki ba,shi ne Abba ya ke ce mata ga sauran icen biki ta d'iba,to sai na ga ta nuna ko za kai fad'a ne ni kuma na ce mata me ne ai lalura ce don ta kunnna ice kamawa tai."
Shafa kanta ya ke cikin wani salo ya fara magana " Su'ada wlh Maman Abba ba ta kulawa da gidan nan,sai ta Kai yamma ba tai wanke wanke ba,shara kuwa ba batunta,sai kwana biyu ake yi,sai dai in an b'ata waje a tattare iya gun,ga yara dole gida ya rink'a buk'atar gyara kullum,Wannan dalilin yasa na d'auke sharar gidan nan ta dawo kaina,kin ga band'akinmu ba d'aya ba amma haka nake wanke namu na wanke na su, wanke wanke ma don Baby ta kawo girma ne ake yinsa a kan kari,to kinga shekarar ta takwas yarinyar amma ita ke wanke wanke safe da yamma,wani lokaci da safe ina jinta ta ba kuka tana wanke wanke sabida ga makaranta ga aiki,wankan yara wahla ya ke mata,na sha kama yaran nan nai musu wanka,in naga su na yawo da datti,Maman Abba ta na da son kiji da k'iywa,ni kuma na tsani kazanta,duk rashin son maganata ba na shiru in naga k'azanta ,to in kin jini da ita k'azanta na gani,ban so ban so wlh."
Juyi Su'ada tai a jikinsa Wanda ta san dole zai tsirga mai,da sauri ya Tsantsameta ya na fad'in "Kan kujera fa mu ke sai kin fad'o ko?"
Mik'a ta k'ara yi sannan tace "To in na fad'o ai laifinka ne.
Kasan me? Maman Abba mace ce,kuma duk mace ta na buk'atar uziri cikin rayuwar ta,maybe abubuwa ne su kai mata yawa,ga yara ga aikin gida,amma Yanzu tunda yaranta sun fara girma za ka ga komai ya dai daita,k'azanta ba ta dad'i ko kad'an amma wani ta zame mai jiki."
Kiran Sallar isha'i ya sa su ka mik'e don yin salla.
Bayan sun dawo daga masallaci ya shiga yiwa Babs sai da safe,zai mik'e yace ya zauna.bayan gyaran murya ya fara magana "Ibrahima daman batu ne kan abinci,ka ga tun zuwan matarka gidan nan ta samin kwano itama,ga ba wajan Sakeena, to abincin ya na min yawa,kuma duk wadda ban ci nata ba zata ji ba dad'i, kaga d'azu ban ci na Sakeena ba sabida na k'oshi a lokacin da ta kawo,nace yaran su cinye,to hakan bai mata dad'i ba har ta kaiwa mijinta k'orafi, d'azu da magriba ta ke min zancan, don haka shima na fad'a mai ko wacce ta rink'a kawo min abinci sau d'aya, wata da rana wata da dare,kaga hakan zai fi ko?"
Jinjina kai ya yi da cewa "Hakan yayi Baba, amma ita Su'ada sai ta rink'a kawo ma na dare,sabida kaga tana koyarwa kuma da safe ne,yanzu ma hutu su ka bata,kafin ta dawo ta d'ora girki lokaci zai rink'a k'urewa,amma na daren ta na gida."
Gyad'a kai Baba yai da fad'in "Hakan ya yi,Allah ta yai muku albarka ya hore muku abinda za ku kula da iyalenku."
"Ameen Ameen Baba,Allah ya tashemu lafiya."
Sai da dafe ya yi mai ya fito.
Sai da su ka zo kwanciya ya kewa Su'ada maganar da su kai da Baba,ita kam mamaki ne ya cika ta,amma sai ta basar kawai tace "To ai ba damuwa,duk d'aya ne."
********
Da safe Baba ya na jiran abun karyawa har wajan goma Sakeena ba ta kawo mishi ba,ya saba tun wajan takwas take kawo mishi,tunda mijinta da wuri ya ke fita tare da yara ya saukesu a makaranta,to yau har yaran su ka fita shiru,har ya koma baccin safe ya tashi ba labari, bai ce komai ba ya shirya ya fita k'ofar gida, a nan ya samu yara masu wucewa da abun siyarwa ya sai kunun gyad'a ya sha.
Su'ada kam daman ita na rana da dare ta ke bashi,to kuma yanzu ance sau d'aya, ba ta san Baba bai karya ba balle ta aiko mai.
Ibrahim ya gama shirin sa zai tafi shago, ta rako shi kamar yanda ta saba,d'akin Baba su ka shiga don gaisheshi, sai su ka samu bai ciki,bakin soro ta rakoshi su kai sallama ya tafi.
ganin Sakeena ba ta tsakar gida ya sa Su'ada tsayawa k'ofar d'aki tana gaisheta, a dak'ile ta amsa mata,Islam ta d'aga labule ta na mata surutu,ta tsaya ta na tsokanar yarinyar,ta rik'e hannunta su ka wuce wajanta, ba ta bi ta kan uwar ba.
Tsawon kwana uku Su'ada ta ga Sakeena ta canja mata sosai,abun na bata mamaki,ita dai ta san ba abunda tai mata amma sai cin magani take.
Ganin haka ya sa ta tsantsame jikinta,don duk kirkin Su'ada ba ta d'aukan wulakanci sam.
B'angaran Baba kuwa kwana uku ya na fama da yunwar safe,ba wanda ya kula cikin yaransa,dalili Jabir daman da safe ya ke fita school,Yaya Muktar ma tun bayan sallar asuba in ya shiga su ka gaisa to sai yara sun yi shirin boko ya ke fitowa su tafi tare,to anan ma in ya shiga mai sallama ba dad'ewa ya ke ba,shima Ibrahim in su ka gaisa bayan dawowa daga sallar asuba to sai goma in zai fita ya ke k'ara shiga wajansa.
Hak'uri kawaici irin na mutanan da ya sa cikin kwana ukun Baba bai magantu ba,sai dai kullum in hantsi ya d'aga ya fita k'ofar gida ya zauna,in masu kunu sun zo wucewa ya siya ya sha. Ganin da yai yunwa na neman mai illa ya sa yau yai magana,lokacin da Ibrahim ya zo mai Sallama zai fita ya tsaida shi.
"Ibrahima in babu takura ka cewa me d'akinka ta sa kwanan safe da ni,ita Sakeena sai ta rink'a kawo min na rana kawai."
"To Baba ba damuwa,na ranar ma don ka k'i ne wallahi."
"A'a a yi hakan kawai,na safe da na daran ma Allah ya yi albarka ya bud'a muku."
"Ameen Baba, Allah ya k'ara lafiya ya k'ara nisan kwana."
Nan yai mai sallama ya tafi.
*******
Da dare ya sanar da Su'ada ta rink'a girkin safe da Baba,ta amsa da to, ba ta k'ara cewa komai ba,cikin ranta ta ke nazarin al'umuran da ke faruwa,tabbas in haka zaman gidan zai rink'a tafiya ba zai dad'i ba.
*Taku ce*
*y'ar mutan Ja'oji*🙋
[2/24, 12:05 AM] LAYUZA KABIR: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
_Allah ya k'ara maka lafiya my Grandfather, Allah ya tashi kafad'arka ya sauk'ak'a maka_🙏🙏🙏
_*page*_ *23-24*
Washe gari kam Su'ada da wuri ta had'a abincin karyawa, kunun tsamiya ta dama kasancewar ta san Baba ya na sonshi,sannan ta d'an nik'a wakenta a blander tai mai lafiyayyiyar alala wadda ta ji kifi da k'wai, da yawa ta zuba mishi kunun a flask,sannan alalan ma ta zuba mishi da yawa.
Bayan sun yi wanka kafin su zauna karyawa Ibrahim ya kai mishi.
Sakeena na tsakar gida ta ga ya wuce da abinci ya kaiwa Babah,tsaki ta ja tana fad'i cikin ranta '' Aikin banza sabon sanabe,za a gaji a bari tunda mu ma muka saki''
Bai kula da yanayin fuskarta ba,gaidata kawai yai ya wuce.
Ita kam zuciyarta fal k'unci taita k'ananun maganganunta.
Tun daga ranar sai ya zamana ko yaushe da wuri Su'ada ke tashi tai abin karyawa sabida Babah,ko da su ba lokacin zasu karya ba.
Sosai Babah ke sa mata albarka dare da rana,wanda hakan ke sa taji dad'i kuma yake k'ara mata karsashi wajan yi mai hidima.
************
Lokacin hutun da Su'ada ta d'auka na aure ya cika, don haka wannan satin tai shirin komawa bakin aikinta.
Sassafe ranar Monday tai shirinta,bayan ta gama abincin karyawa Khaleelee ya kaiwa Baba nashi,ita kam a tsatstsaye ma ta sha ruwan tea.
Kamar yanda ya tsara kullum shi zai rink'a kaita, don haka tare su ka fito,Ta tsaya k'ofar d'akin Sakeena ta gaisheta,sannan tai mata sallama.
Bata san ina zata ba,ta dai amsa mata da "To sai kin dawo".
D'akin Babah ta shiga su ka gaisa ta fad'a mai ta koma aiki,yai mata addu'a sosai,cikin jin dad'i take amsawa, fito su ka wuce.
Har cikin makarantar ya sauketa,su kai sallama.
D'aki ta koma ta d'aura zani sannan ta saka katon hijab ta fito,binta yai da kallo harta fita a falon.
A tsakar gida ta same shi ya na cin sauran abincin da ta kaiwa Baba,cikin fara'a ya d'ago ya na fad'in "Aunty na barka da gida ."
"Sannu da dawowa, ga abincin ka harka fara cin wani,amma wannan taliya ne fa."
"Wallahi kinga yunwa na ke ji ,kuma Maman Abba bata k'arasa ba kawai na d'auko sauran na Babah,amma kawo taliyar ma duk zata shiga ai,kin san cikina na maza ne ba kalar na angonki ba."
Ya k'arasa da tsokana,
Dariya tai ta ajiye mai kulan ta na fad'in "Ba ruwana ai ya na jiyo ka."
Sakeena ta saki wani tsaki tana fifita wuta.
Juyowa tai ta kalleta har za tai magana taga ta wani d'aure fuska,don haka bata tanka ba ta juya ta koma wajanta.
Bayan sallar Magriba Su'ada na kwance jikin Ibrahim ya kamo kunnanta yana magana k'asa k'asa " Ke ce kika bada damar a kunna ice a gidan nan ko?"
Rik'e hannun da ya kama mata kunnan tai cikin kukan shagwab'a tace "Wayyo Allah, Abbana mamana,kun kawo ni za'a cire muku kunne na."
Sosai maganar ta bashi dariya yace "Yanzu wannan kunnan ai nawa ne,ko na cire ni zan yi kuka, amma kin San me?"
"Um um sai ka fad'a."
"Ban san inga ana kunna ice a gidan nan tun asali,sabida matar gidan tana da rauni wajan gyarawa,in ta kunna ice sai ki ga duk gidan ya fita hayyacinsa, don haka ma shi kansa Yaya Muktar ya hana,sai gawayi ta ke amfani da shi,to d'azu da nazo naga ta kunna ice nace ga gawayi me yasa ta kunna ice ,shine tace wai ya k'i kamawa sai kika ce ta kunna icen kawai."
Gyara kwanciya tai a jikinsa tans wasa da gashin da ke kwance a Hannayensa,
Cikin sanyin murya tace " Ka kan wani abu ne? Gawayin da take amfani da shi bai ci,ya sha ruwa kuma lokaci na ta k'urewa ba ta d'ora girki ba,shi ne Abba ya ke ce mata ga sauran icen biki ta d'iba,to sai na ga ta nuna ko za kai fad'a ne ni kuma na ce mata me ne ai lalura ce don ta kunnna ice kamawa tai."
Shafa kanta ya ke cikin wani salo ya fara magana " Su'ada wlh Maman Abba ba ta kulawa da gidan nan,sai ta Kai yamma ba tai wanke wanke ba,shara kuwa ba batunta,sai kwana biyu ake yi,sai dai in an b'ata waje a tattare iya gun,ga yara dole gida ya rink'a buk'atar gyara kullum,Wannan dalilin yasa na d'auke sharar gidan nan ta dawo kaina,kin ga band'akinmu ba d'aya ba amma haka nake wanke namu na wanke na su, wanke wanke ma don Baby ta kawo girma ne ake yinsa a kan kari,to kinga shekarar ta takwas yarinyar amma ita ke wanke wanke safe da yamma,wani lokaci da safe ina jinta ta ba kuka tana wanke wanke sabida ga makaranta ga aiki,wankan yara wahla ya ke mata,na sha kama yaran nan nai musu wanka,in naga su na yawo da datti,Maman Abba ta na da son kiji da k'iywa,ni kuma na tsani kazanta,duk rashin son maganata ba na shiru in naga k'azanta ,to in kin jini da ita k'azanta na gani,ban so ban so wlh."
Juyi Su'ada tai a jikinsa Wanda ta san dole zai tsirga mai,da sauri ya Tsantsameta ya na fad'in "Kan kujera fa mu ke sai kin fad'o ko?"
Mik'a ta k'ara yi sannan tace "To in na fad'o ai laifinka ne.
Kasan me? Maman Abba mace ce,kuma duk mace ta na buk'atar uziri cikin rayuwar ta,maybe abubuwa ne su kai mata yawa,ga yara ga aikin gida,amma Yanzu tunda yaranta sun fara girma za ka ga komai ya dai daita,k'azanta ba ta dad'i ko kad'an amma wani ta zame mai jiki."
Kiran Sallar isha'i ya sa su ka mik'e don yin salla.
Bayan sun dawo daga masallaci ya shiga yiwa Babs sai da safe,zai mik'e yace ya zauna.bayan gyaran murya ya fara magana "Ibrahima daman batu ne kan abinci,ka ga tun zuwan matarka gidan nan ta samin kwano itama,ga ba wajan Sakeena, to abincin ya na min yawa,kuma duk wadda ban ci nata ba zata ji ba dad'i, kaga d'azu ban ci na Sakeena ba sabida na k'oshi a lokacin da ta kawo,nace yaran su cinye,to hakan bai mata dad'i ba har ta kaiwa mijinta k'orafi, d'azu da magriba ta ke min zancan, don haka shima na fad'a mai ko wacce ta rink'a kawo min abinci sau d'aya, wata da rana wata da dare,kaga hakan zai fi ko?"
Jinjina kai ya yi da cewa "Hakan yayi Baba, amma ita Su'ada sai ta rink'a kawo ma na dare,sabida kaga tana koyarwa kuma da safe ne,yanzu ma hutu su ka bata,kafin ta dawo ta d'ora girki lokaci zai rink'a k'urewa,amma na daren ta na gida."
Gyad'a kai Baba yai da fad'in "Hakan ya yi,Allah ta yai muku albarka ya hore muku abinda za ku kula da iyalenku."
"Ameen Ameen Baba,Allah ya tashemu lafiya."
Sai da dafe ya yi mai ya fito.
Sai da su ka zo kwanciya ya kewa Su'ada maganar da su kai da Baba,ita kam mamaki ne ya cika ta,amma sai ta basar kawai tace "To ai ba damuwa,duk d'aya ne."
********
Da safe Baba ya na jiran abun karyawa har wajan goma Sakeena ba ta kawo mishi ba,ya saba tun wajan takwas take kawo mishi,tunda mijinta da wuri ya ke fita tare da yara ya saukesu a makaranta,to yau har yaran su ka fita shiru,har ya koma baccin safe ya tashi ba labari, bai ce komai ba ya shirya ya fita k'ofar gida, a nan ya samu yara masu wucewa da abun siyarwa ya sai kunun gyad'a ya sha.
Su'ada kam daman ita na rana da dare ta ke bashi,to kuma yanzu ance sau d'aya, ba ta san Baba bai karya ba balle ta aiko mai.
Ibrahim ya gama shirin sa zai tafi shago, ta rako shi kamar yanda ta saba,d'akin Baba su ka shiga don gaisheshi, sai su ka samu bai ciki,bakin soro ta rakoshi su kai sallama ya tafi.
ganin Sakeena ba ta tsakar gida ya sa Su'ada tsayawa k'ofar d'aki tana gaisheta, a dak'ile ta amsa mata,Islam ta d'aga labule ta na mata surutu,ta tsaya ta na tsokanar yarinyar,ta rik'e hannunta su ka wuce wajanta, ba ta bi ta kan uwar ba.
Tsawon kwana uku Su'ada ta ga Sakeena ta canja mata sosai,abun na bata mamaki,ita dai ta san ba abunda tai mata amma sai cin magani take.
Ganin haka ya sa ta tsantsame jikinta,don duk kirkin Su'ada ba ta d'aukan wulakanci sam.
B'angaran Baba kuwa kwana uku ya na fama da yunwar safe,ba wanda ya kula cikin yaransa,dalili Jabir daman da safe ya ke fita school,Yaya Muktar ma tun bayan sallar asuba in ya shiga su ka gaisa to sai yara sun yi shirin boko ya ke fitowa su tafi tare,to anan ma in ya shiga mai sallama ba dad'ewa ya ke ba,shima Ibrahim in su ka gaisa bayan dawowa daga sallar asuba to sai goma in zai fita ya ke k'ara shiga wajansa.
Hak'uri kawaici irin na mutanan da ya sa cikin kwana ukun Baba bai magantu ba,sai dai kullum in hantsi ya d'aga ya fita k'ofar gida ya zauna,in masu kunu sun zo wucewa ya siya ya sha. Ganin da yai yunwa na neman mai illa ya sa yau yai magana,lokacin da Ibrahim ya zo mai Sallama zai fita ya tsaida shi.
"Ibrahima in babu takura ka cewa me d'akinka ta sa kwanan safe da ni,ita Sakeena sai ta rink'a kawo min na rana kawai."
"To Baba ba damuwa,na ranar ma don ka k'i ne wallahi."
"A'a a yi hakan kawai,na safe da na daran ma Allah ya yi albarka ya bud'a muku."
"Ameen Baba, Allah ya k'ara lafiya ya k'ara nisan kwana."
Nan yai mai sallama ya tafi.
*******
Da dare ya sanar da Su'ada ta rink'a girkin safe da Baba,ta amsa da to, ba ta k'ara cewa komai ba,cikin ranta ta ke nazarin al'umuran da ke faruwa,tabbas in haka zaman gidan zai rink'a tafiya ba zai dad'i ba.
*Taku ce*
*y'ar mutan Ja'oji*🙋
[2/24, 12:05 AM] LAYUZA KABIR: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
_Allah ya k'ara maka lafiya my Grandfather, Allah ya tashi kafad'arka ya sauk'ak'a maka_🙏🙏🙏
_*page*_ *23-24*
Washe gari kam Su'ada da wuri ta had'a abincin karyawa, kunun tsamiya ta dama kasancewar ta san Baba ya na sonshi,sannan ta d'an nik'a wakenta a blander tai mai lafiyayyiyar alala wadda ta ji kifi da k'wai, da yawa ta zuba mishi kunun a flask,sannan alalan ma ta zuba mishi da yawa.
Bayan sun yi wanka kafin su zauna karyawa Ibrahim ya kai mishi.
Sakeena na tsakar gida ta ga ya wuce da abinci ya kaiwa Babah,tsaki ta ja tana fad'i cikin ranta '' Aikin banza sabon sanabe,za a gaji a bari tunda mu ma muka saki''
Bai kula da yanayin fuskarta ba,gaidata kawai yai ya wuce.
Ita kam zuciyarta fal k'unci taita k'ananun maganganunta.
Tun daga ranar sai ya zamana ko yaushe da wuri Su'ada ke tashi tai abin karyawa sabida Babah,ko da su ba lokacin zasu karya ba.
Sosai Babah ke sa mata albarka dare da rana,wanda hakan ke sa taji dad'i kuma yake k'ara mata karsashi wajan yi mai hidima.
************
Lokacin hutun da Su'ada ta d'auka na aure ya cika, don haka wannan satin tai shirin komawa bakin aikinta.
Sassafe ranar Monday tai shirinta,bayan ta gama abincin karyawa Khaleelee ya kaiwa Baba nashi,ita kam a tsatstsaye ma ta sha ruwan tea.
Kamar yanda ya tsara kullum shi zai rink'a kaita, don haka tare su ka fito,Ta tsaya k'ofar d'akin Sakeena ta gaisheta,sannan tai mata sallama.
Bata san ina zata ba,ta dai amsa mata da "To sai kin dawo".
D'akin Babah ta shiga su ka gaisa ta fad'a mai ta koma aiki,yai mata addu'a sosai,cikin jin dad'i take amsawa, fito su ka wuce.
Har cikin makarantar ya sauketa,su kai sallama.