Sashe 16
Facala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
D'an lumshe ido tai tana k'ara matsa hannunsa e cikin nata tace "Me yasa zan kiraka kana wajan sana'arka na tashi hankalinka, na fita na bata hak'uri bata jiba don haka na barta, tun d'azu nake fatan Allah ya dawo da Baba ko Yaya Muktar d'in, sai kuma ga ka Allah ya kawoka,matsalar nan abun dubawa ce my Choice, wani sashin Maman Abba tana da gaskiya,kawai yanda zata kai kokenta ne bata iya ba,a k'aidar musulunci daman Abba da Faruk bai dace su na kwana cikin su Baby ba,in ba da wata babbar lalura ba,kawai rashin iya magana ne yasa ba za'a fahimceta ba."
Lumshe idanuwansa yai yana d'an cizon lips d'in sa yace " Su'ada ba wannan dalilin ne yasa Sakeena take wannan borin ba,kishi ke damunta, tun lokacin da Baba yace ya bar mana gidan nan ni da yaya Muktar kuma ya kasafta ya bawa kowa rabonsa take bori,borin kuma taga duk d'akunan da take wadak'arta dasu sun shigo rabona,taga na ware sashi na na keb'ence shi,tun sannan taga gidan ya tsuke mata ta shiga masifar d'akuna biyu sun mata kad'an da y'ay'anta, wannan dalilin yasa nace Abba ya rink'a kwana tare da Jabeer tunda ni na bar d'akin, to bayan wannan me Sakeena ke nema kuma Su'ada? "
Tsam tai da ranta tana nazari can tace "D'aki d'aya take so a k'ara mata."
"To wane d'akin za'a bata? Na Baba ko na Jabeer?"
Ajiyar zuciya ta sauke kafin tace " Na Jabeer take hari,da akwai shago a k'ofar gida da ya koma ya bar Mata."
Zamewa kawai yai ya kwanta bai k'ara magana ba.
Ganin haka yasa Su'ada ta tashi ta ci gaba da ayyukanta.
Jabeer kam yana k'ofar gida zaune shi kad'ai sai huci yake,a lokacin su Baba su ka dawo daga d'aurin Auran da su ka je, ganin Jabeer d'in dafe da kai fuska d'aure tamau yasa Baba saurin tambayar sa me ya faru. Cikin k'unar rai ya juyewa Baban komai har fad'an da Ibrahim yai ta mai kuma akan gaskiyarsa.
Shiru Baba yayi na d'an lokaci sannan yace " Tashi muje ciki."
D'akin Baban su ka shiga,bayan ya rage kayan jikinsa ya dubeshi da kyau yace "Jabeer! abunda kai Sam baka kyauta ba,shin ka manta Sakeena matsayin uwa take gareka,shekaru goma sha fa tana rainonka,sauyin halin da tai bashi zai sa kuma Ku sauya ba,duk rashin mutuncin mutum karka manta alkairin da ya tab'a yi maka, kishin matar k'anin miji (FACALA) ke cin Sakeena, kuma ba akanta aka fara ba,sai dai kuma shi kishin jahilci ne,ba wani dalili da zaisa kai kishin matar da baku had'a miji da ita ba,a da can mata sun maida kishin FACALA abun yi,har sai kaga wata macen bata kishin kishiyarta kamar yanda take na FACALA, amma a yanzu da ilimi ya wadata wayewa tai yawa duk an zubar da wannan abun,sai dai dai daikun mata ne irin Sakeena basu gane hakan ba,abunda nake jan hankalinka Kai tai mata uziri karka bari wannan halin yasa ta zama abokiyar fadanka,sannan kamar yanda kowa ya sani wannan gida a da can ne yake nawa,yanzu kuwa ya zama mallakin Ibrahima da Muktar don haka matansu nada iko dashi, ni da kai duk cin arzik'i muke na d'an lokaci, kwanaki kad'an su ka rage min a duniyar,yayin da kai kuma lokaci na zuwa kaima za kai auranka ka zauna a naka gidan, don haka yanzu kana ji ko,ka had'a kayanka tsaf ka dawo d'akin nan muyi zamanmu mu biyu,daman d'akin yamin girma ai,kaga ko cikin dare ka rink'a taimakona in ciwo ya tayar min."
Tofa Baba ya gama kulle Jabeer, banda tsananin biyayyarsu da mahaifnsu ba abunda zai sa bai musawa Baba ba,amma ba yanda ya iya,haka ya amsa ya tashi ya fice.
Ibrahim ya fito sallar azahar Baba yake sanar dashi shawarar daya yanke ta dawowar Jabeer d'akin sa,bai so amma bai nuna ba yacewa Baba Allah yasa hakan yafi alkairi, nan ya zage ya taimakawa Jabeer d'in su ka kwashe duk kayan su ka dawo dashi d'akin Baba, gefe duk ya jera kayansa,sai dai gado bazai samu waje ba duk da k'arami ne,Baba yace ba komai nashi ya ishesu su biyun ai,yace ya bar gadon a d'akin su Abban sai su rink'a kwana,habawa bak'in ciki kamar ya kashe Jabeer ya kasa dannewa har Baban ya gane ya sassauta murya da fad'in " Ashe ba zaka iya yiwa y'ay'an d'an uwanka hidima ba? Shin me Sunana da faruku da zasu rink'a kwana a d'akin akan gadonka shi kakewa bak'in ciki,ko ba ran Muktar Kai me rik'e mai y'ay'a ne don haka karka sa b'acin ran uwarsu a ranka har ya shafesu,kayi mu'amala dasu kamar y'ay'an cikinka kaji ko?"
Gyad'a kai kawai yayi yaci gaba da jera kayansa,da yawan wasu abubuwan dole ya barsu a d'akin don ba wajan ajiyar su.
05/12/2019
*TAKU CE*
*Y'AR MUTAN JA'OJI*🙋
[2/24, 12:05 AM] LAYUZA KABIR: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
*Sadaukarwar gareku D'alibai masu albarka*
*'Daliban makarantar Intisharul Qur'anil Kareem*
*Da 'Daliban Nusratul Aulad Islamiyya*
*Allah yai muku albarka ya sawa iliminku albarka,ya sa musulunci yai alfahari da ku,Al'umma su amfana da ku*🙏🙏 *Kuna cikin raina ina sonku sosai duk da irin charger min k'wak'walwa da Ku ke*😕
_*page*_*27-28*
Bayan sallar la'asar Baba ya tako har tsakar gidan ya samu Sakeena bakin murhu,cikin fara'a ya fara yiwa yaran wasa yana tsokanar su, daga nan ya kalleta ba wata damuwa tare dashi yace "Sakeena ki had'owa me sunana duk kayansa da Faruku ki dawo musu dashi wancan d'aki na Jabeer, shi ya koma dakina da zama har sanda Allah zai raba zaman, ga gado nan da yar durowar kaya nace ya bar musu asa musu kayansu ciki."
Ya juya yana duban Abba yace "Sulaimanu daga yau wancan d'akin ne naku kaji ko?"
Gyad'a kai Abba yayi kawai don yaji abun banbarakwai a kansa.
Daga haka Baba ya koma d'akinsa.
Tofa maimakon murna sai jikin Sakeena yai sanyi k'alau,sai ta fara tunanin Allah yasa dai ba wani abun aka fad'awa Baban ba,don ko bata d'akin za'ai bata hanyar Baba taso abun ya biyo ba,taso Muktar ne da kansa ya shiga maganar ya 'kwatar mata y'ancinta,ita yanzu ma bata san ya za tai dashi ba.
Jikinta a mace har dare, lokacin dawowar yaya Muktar yai nan cikinta ya k'ara d'urar ruwa.
Bayan ya gama cin abinci yai wanka ya fita sallar isha'i, anan Baba yace mai "muje dakina ina son magana da kai."
Bai bud'e mai abunda ke faruwa ba kawai ca yai mai "Muktar sabida lalura da yanayin rayuwa nace Jabeer ya dawo d'akin nan mu rink'a kwana tare,kaga da yawa ciwo cikin dare Ke kamani,kuma na samu abokin d'ebe kewa ma. d'akin sa kuma nace ya barwa me sunana da Faruk su rink'a kwana a ciki."
Tsam Yaya Muktar yai da ransa,ko ba'a fad'a mishi komai ba to yaji a jikinsa kamar a kwai wata a k'asa, don haka ya kalli Baba ya na tausasa murya yace "Baba Allah ya sa dai ba wani abu ne ya faru ba?"
Cikin kauda zancen Baba yace "A'a ba abunda ya faru,je ka abunka."
Kawai shi Yaya Muktar sai ya ji zuciyarsa ta kasa nutsuwa, don haka ya na barin d'akin Baba sai ya fito k'ofar gida,wayar Ibrahim ya kira yace don Allah ya fito waje ya sameshi za suyi magana.
Shi kam Khaleelee har ya cire kayansa ma ya maida ya fito,a kan dakali ya samu yaya zaune,bayan ya zauna gefensa,Yaya Muktar ya zuba mishi ido na d'an lokaci, can yace "Ibrahim kaji hukuncin da Baba ya yanke kan Jabeer ya barwa su Abba d'akinsa ?"
Gyad'a kai yai yana fad'in "Eh haka yace, wai ko don ciwonsa wani sa'in in ya tayar mai cikin dare ga mutum kusa dashi."
Yanayin amsar da Ibrahim ya bawa shi Sam bata gamsar dashi ba,mik'ewa yai yana fad'in "Allah ya kyauta."
Daga haka ya bashi hannu su kai musabaha yace "mu koma ciki Allah ya tashemu lafiya."
Shi kam Ibrahim ba dan Baba ya kwab'eshi da kar ya sanar da Muktar fad'an da Sakeena tai da Jabeer akan d'akin ba tabbas da ya sanar dashi komai,amma ya san bai da wannan damar,haka ya koma wajan sa yana cire zancen a ransa.
Yaya Muktar baiwa Sakeena maganar ba har sai da su ka zo bacci,har ta kwanta ya bubbuga k'afarta ta tashi zaune,zuba mata ido yai yana nazartarta don ya ga kamar a tsorace ta tashi.mutstsika ido ta fara yi ganin ya kafeta da ido, can dai da taga yak'i magana sai tai fuaka tace "Me ya faru wai?"
Cikin d'aure fuska yace mata "Ke zan tambaya me ya faru? maza ke nake jira fad'a min me ya faru kan batun d'akin Jabeer da ki ka 'kwallafa rai a kansa,shin wane rashin albarka ki kai har d'akin ya zama mallakar y'ay'anki?"
Cikin tsoro da kuma rashin kunya a sashi d'aya tace "Me kuwa ya faru,ni ba ruwana, Me d'akin ne ya min rashin kunya ni kuma na taka masa burki,na nuna masa ni ba Sa'arsa bace, to ni daga haka ban san me kuma ya faru ba."
Eh lalle zarginsa ya zama gaskiya, nan fa Ya Muktar ya sata gaba da masifa in da yake shiga ba nan yake fita ba,yaci mutuncinta tas kuma ya ja mata kunne kan sanin me take yi don wata rana za tai abunda za tai danasani.
To Sakeena dai baki ya mutu, sai muzuran k'arya take tana turo baki,shi kam ya juya mata baya ya kwanta.
Tsawon kwanaki uku duk Sakeena ta rasa me ke mata dad'i, ga d'aki dai an bar mata yara suna kwana a ciki,to amma miji yak'i sakar mata fuska sam,ga Jabeer da kullum ya shigo gidan zai tai mata muzurai,don k'ala bata had'a shi da ita yanzu,abincinta ma ya bar ci,duk wani kayan ta da ya ke amfani dasu ya daina,a gabanta zai wuce wajan Su'ada yace "Auntyna don Allah ban aran abu kaza."
To ita Sakeena hakan ne bata so,tab'a ana fifita Su'ada ko ana huld'a da ita.
Lumshe idanuwansa yai yana d'an cizon lips d'in sa yace " Su'ada ba wannan dalilin ne yasa Sakeena take wannan borin ba,kishi ke damunta, tun lokacin da Baba yace ya bar mana gidan nan ni da yaya Muktar kuma ya kasafta ya bawa kowa rabonsa take bori,borin kuma taga duk d'akunan da take wadak'arta dasu sun shigo rabona,taga na ware sashi na na keb'ence shi,tun sannan taga gidan ya tsuke mata ta shiga masifar d'akuna biyu sun mata kad'an da y'ay'anta, wannan dalilin yasa nace Abba ya rink'a kwana tare da Jabeer tunda ni na bar d'akin, to bayan wannan me Sakeena ke nema kuma Su'ada? "
Tsam tai da ranta tana nazari can tace "D'aki d'aya take so a k'ara mata."
"To wane d'akin za'a bata? Na Baba ko na Jabeer?"
Ajiyar zuciya ta sauke kafin tace " Na Jabeer take hari,da akwai shago a k'ofar gida da ya koma ya bar Mata."
Zamewa kawai yai ya kwanta bai k'ara magana ba.
Ganin haka yasa Su'ada ta tashi ta ci gaba da ayyukanta.
Jabeer kam yana k'ofar gida zaune shi kad'ai sai huci yake,a lokacin su Baba su ka dawo daga d'aurin Auran da su ka je, ganin Jabeer d'in dafe da kai fuska d'aure tamau yasa Baba saurin tambayar sa me ya faru. Cikin k'unar rai ya juyewa Baban komai har fad'an da Ibrahim yai ta mai kuma akan gaskiyarsa.
Shiru Baba yayi na d'an lokaci sannan yace " Tashi muje ciki."
D'akin Baban su ka shiga,bayan ya rage kayan jikinsa ya dubeshi da kyau yace "Jabeer! abunda kai Sam baka kyauta ba,shin ka manta Sakeena matsayin uwa take gareka,shekaru goma sha fa tana rainonka,sauyin halin da tai bashi zai sa kuma Ku sauya ba,duk rashin mutuncin mutum karka manta alkairin da ya tab'a yi maka, kishin matar k'anin miji (FACALA) ke cin Sakeena, kuma ba akanta aka fara ba,sai dai kuma shi kishin jahilci ne,ba wani dalili da zaisa kai kishin matar da baku had'a miji da ita ba,a da can mata sun maida kishin FACALA abun yi,har sai kaga wata macen bata kishin kishiyarta kamar yanda take na FACALA, amma a yanzu da ilimi ya wadata wayewa tai yawa duk an zubar da wannan abun,sai dai dai daikun mata ne irin Sakeena basu gane hakan ba,abunda nake jan hankalinka Kai tai mata uziri karka bari wannan halin yasa ta zama abokiyar fadanka,sannan kamar yanda kowa ya sani wannan gida a da can ne yake nawa,yanzu kuwa ya zama mallakin Ibrahima da Muktar don haka matansu nada iko dashi, ni da kai duk cin arzik'i muke na d'an lokaci, kwanaki kad'an su ka rage min a duniyar,yayin da kai kuma lokaci na zuwa kaima za kai auranka ka zauna a naka gidan, don haka yanzu kana ji ko,ka had'a kayanka tsaf ka dawo d'akin nan muyi zamanmu mu biyu,daman d'akin yamin girma ai,kaga ko cikin dare ka rink'a taimakona in ciwo ya tayar min."
Tofa Baba ya gama kulle Jabeer, banda tsananin biyayyarsu da mahaifnsu ba abunda zai sa bai musawa Baba ba,amma ba yanda ya iya,haka ya amsa ya tashi ya fice.
Ibrahim ya fito sallar azahar Baba yake sanar dashi shawarar daya yanke ta dawowar Jabeer d'akin sa,bai so amma bai nuna ba yacewa Baba Allah yasa hakan yafi alkairi, nan ya zage ya taimakawa Jabeer d'in su ka kwashe duk kayan su ka dawo dashi d'akin Baba, gefe duk ya jera kayansa,sai dai gado bazai samu waje ba duk da k'arami ne,Baba yace ba komai nashi ya ishesu su biyun ai,yace ya bar gadon a d'akin su Abban sai su rink'a kwana,habawa bak'in ciki kamar ya kashe Jabeer ya kasa dannewa har Baban ya gane ya sassauta murya da fad'in " Ashe ba zaka iya yiwa y'ay'an d'an uwanka hidima ba? Shin me Sunana da faruku da zasu rink'a kwana a d'akin akan gadonka shi kakewa bak'in ciki,ko ba ran Muktar Kai me rik'e mai y'ay'a ne don haka karka sa b'acin ran uwarsu a ranka har ya shafesu,kayi mu'amala dasu kamar y'ay'an cikinka kaji ko?"
Gyad'a kai kawai yayi yaci gaba da jera kayansa,da yawan wasu abubuwan dole ya barsu a d'akin don ba wajan ajiyar su.
05/12/2019
*TAKU CE*
*Y'AR MUTAN JA'OJI*🙋
[2/24, 12:05 AM] LAYUZA KABIR: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
*Sadaukarwar gareku D'alibai masu albarka*
*'Daliban makarantar Intisharul Qur'anil Kareem*
*Da 'Daliban Nusratul Aulad Islamiyya*
*Allah yai muku albarka ya sawa iliminku albarka,ya sa musulunci yai alfahari da ku,Al'umma su amfana da ku*🙏🙏 *Kuna cikin raina ina sonku sosai duk da irin charger min k'wak'walwa da Ku ke*😕
_*page*_*27-28*
Bayan sallar la'asar Baba ya tako har tsakar gidan ya samu Sakeena bakin murhu,cikin fara'a ya fara yiwa yaran wasa yana tsokanar su, daga nan ya kalleta ba wata damuwa tare dashi yace "Sakeena ki had'owa me sunana duk kayansa da Faruku ki dawo musu dashi wancan d'aki na Jabeer, shi ya koma dakina da zama har sanda Allah zai raba zaman, ga gado nan da yar durowar kaya nace ya bar musu asa musu kayansu ciki."
Ya juya yana duban Abba yace "Sulaimanu daga yau wancan d'akin ne naku kaji ko?"
Gyad'a kai Abba yayi kawai don yaji abun banbarakwai a kansa.
Daga haka Baba ya koma d'akinsa.
Tofa maimakon murna sai jikin Sakeena yai sanyi k'alau,sai ta fara tunanin Allah yasa dai ba wani abun aka fad'awa Baban ba,don ko bata d'akin za'ai bata hanyar Baba taso abun ya biyo ba,taso Muktar ne da kansa ya shiga maganar ya 'kwatar mata y'ancinta,ita yanzu ma bata san ya za tai dashi ba.
Jikinta a mace har dare, lokacin dawowar yaya Muktar yai nan cikinta ya k'ara d'urar ruwa.
Bayan ya gama cin abinci yai wanka ya fita sallar isha'i, anan Baba yace mai "muje dakina ina son magana da kai."
Bai bud'e mai abunda ke faruwa ba kawai ca yai mai "Muktar sabida lalura da yanayin rayuwa nace Jabeer ya dawo d'akin nan mu rink'a kwana tare,kaga da yawa ciwo cikin dare Ke kamani,kuma na samu abokin d'ebe kewa ma. d'akin sa kuma nace ya barwa me sunana da Faruk su rink'a kwana a ciki."
Tsam Yaya Muktar yai da ransa,ko ba'a fad'a mishi komai ba to yaji a jikinsa kamar a kwai wata a k'asa, don haka ya kalli Baba ya na tausasa murya yace "Baba Allah ya sa dai ba wani abu ne ya faru ba?"
Cikin kauda zancen Baba yace "A'a ba abunda ya faru,je ka abunka."
Kawai shi Yaya Muktar sai ya ji zuciyarsa ta kasa nutsuwa, don haka ya na barin d'akin Baba sai ya fito k'ofar gida,wayar Ibrahim ya kira yace don Allah ya fito waje ya sameshi za suyi magana.
Shi kam Khaleelee har ya cire kayansa ma ya maida ya fito,a kan dakali ya samu yaya zaune,bayan ya zauna gefensa,Yaya Muktar ya zuba mishi ido na d'an lokaci, can yace "Ibrahim kaji hukuncin da Baba ya yanke kan Jabeer ya barwa su Abba d'akinsa ?"
Gyad'a kai yai yana fad'in "Eh haka yace, wai ko don ciwonsa wani sa'in in ya tayar mai cikin dare ga mutum kusa dashi."
Yanayin amsar da Ibrahim ya bawa shi Sam bata gamsar dashi ba,mik'ewa yai yana fad'in "Allah ya kyauta."
Daga haka ya bashi hannu su kai musabaha yace "mu koma ciki Allah ya tashemu lafiya."
Shi kam Ibrahim ba dan Baba ya kwab'eshi da kar ya sanar da Muktar fad'an da Sakeena tai da Jabeer akan d'akin ba tabbas da ya sanar dashi komai,amma ya san bai da wannan damar,haka ya koma wajan sa yana cire zancen a ransa.
Yaya Muktar baiwa Sakeena maganar ba har sai da su ka zo bacci,har ta kwanta ya bubbuga k'afarta ta tashi zaune,zuba mata ido yai yana nazartarta don ya ga kamar a tsorace ta tashi.mutstsika ido ta fara yi ganin ya kafeta da ido, can dai da taga yak'i magana sai tai fuaka tace "Me ya faru wai?"
Cikin d'aure fuska yace mata "Ke zan tambaya me ya faru? maza ke nake jira fad'a min me ya faru kan batun d'akin Jabeer da ki ka 'kwallafa rai a kansa,shin wane rashin albarka ki kai har d'akin ya zama mallakar y'ay'anki?"
Cikin tsoro da kuma rashin kunya a sashi d'aya tace "Me kuwa ya faru,ni ba ruwana, Me d'akin ne ya min rashin kunya ni kuma na taka masa burki,na nuna masa ni ba Sa'arsa bace, to ni daga haka ban san me kuma ya faru ba."
Eh lalle zarginsa ya zama gaskiya, nan fa Ya Muktar ya sata gaba da masifa in da yake shiga ba nan yake fita ba,yaci mutuncinta tas kuma ya ja mata kunne kan sanin me take yi don wata rana za tai abunda za tai danasani.
To Sakeena dai baki ya mutu, sai muzuran k'arya take tana turo baki,shi kam ya juya mata baya ya kwanta.
Tsawon kwanaki uku duk Sakeena ta rasa me ke mata dad'i, ga d'aki dai an bar mata yara suna kwana a ciki,to amma miji yak'i sakar mata fuska sam,ga Jabeer da kullum ya shigo gidan zai tai mata muzurai,don k'ala bata had'a shi da ita yanzu,abincinta ma ya bar ci,duk wani kayan ta da ya ke amfani dasu ya daina,a gabanta zai wuce wajan Su'ada yace "Auntyna don Allah ban aran abu kaza."
To ita Sakeena hakan ne bata so,tab'a ana fifita Su'ada ko ana huld'a da ita.