Sashe 2
Facala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
To mutumin da ke jawa yaransa kunne kan haka ta ina shi zai fara hakan.
A zahiri maza da yawa ke sonta cikin danginta da jama'ar gari,so na aure kuwa,amma bata tab'a ganin abun birgewa tare da su,ga namiji har namiji dai abun birgewa amma ita in ya zo mata da batun so sai taji duk bai birgeta. Tun tuni tsarin halittar Khaleelee ke birgeta,halayensa da tsaftarsa ke k'ara fizgarta gareshi,da tai tunanin kawai iya birgeta ya ke yi,amma yanzu ta tabbatar mugun sonsa ya hudata ya kama zuciyarta,yanzu dole ta nemawa kanta mafita, d'ayan biyu dole a yi d'aya ko dai ta nisanci Khaleelee ta jawa kanta mutunci da girma,in kuma ba haka ba taci gaba da zuwa shagon Khaleelee tabbas asirin zuciyarta zai bayyana.daga nan kuma girmanta da k'imarta da yake gani kuma su shek'e. Wanne kenan za tayi? Ta tambayi kanta cikin tsananin damuwa, wannan take ta sak'awa da kuncewa har bacci yai gaba da ita.
Amma farka warta da wannan batun ta farka,bayan tai sallar asuba ta shiga kaiwa Allah kukanta kan yai Mata maganin wannan ciwo daya kamata, nan wajan bacci ya k'ara gaba da ita.
Jidda k'anwarta da suke kwana d'aki d'aya ce ta ga har wajan k'arfe bakwai bata tashi ba kuma tace musu tana da exam k'arfe takwas don haka ta fara tashin ta "Aunty Su'ada ki tashi kin makara fa."
Da sauri ta mik'e tana salati tare da kallon ogogo,a hanzarce ta tashi ta wuce band'aki.
Duka a gurguje tai shirin nata data fito ko break bata tsaya tayi ba ta amsa kud'i wajan mamansu ta fice.
Tana tafiya cikin adai daita ji take kamar tai iska ta kai kanta school don duka mintina kad'an suka rage takwas ta cika.
Allah ya taimaketa lokacin data isa ga d'akin jarrabawar a sannan malaman da zasu jiresu suka k'araso don haka kusan a tare suka shiga, babu wata ishshshiyar nutsuwa tare da ita sai data ga ta zauna tsaf an bata question pepper a sannan ta saki ajiyar zuciya tasan ta tsira.
***********
Zaune yake kan dakalin k'ofar gidansu bayan ya gama sharar wajan,cikin ransa yake fad'in 'kwana biyu Su'ada shiru ko wucewarta ban gani ba yau tsahon sati biyu kenan, duk zasu fara exam amma ai in zata wuce ta bakin shaginsu tana d'aga musu hannu, ya dubata online ma bata hawa,duk daman in zata fara exam kashe wayanta take babbar sai dai tabar k'aramar a hannunta'
Ciro wayarsa yai cikin aljihu ya fara nemo number d'inta,ringing d'aya biyu ta d'auka yai mata sallama cikin cool voice d'insa,itama cikin fara'arta ta amsa duk da k'ok'arin ta na danne zakuwar ta na karya gane nishad'in da take ciki, "Malama Su'ada kin b'uya gaba d'aya."
"Hhhmmm bari kawai Khaleelee exam ta binne ni,ban gane komai in ba farar takarda in cikata da bulun Biro ba."
Dariya sosai maganar ta bashi bayan ya gama darawa yace "To Allah ya bada sa'a ya sa a fito da kyakykyawar sakamako."
"Ameen na gode Khaleelee, insha Allah yau zan kawo d'inkunan ankon graduation d'inmu,yanzu da mun fito exam zamu wuce kasuwa mu siyo zan kawo ma guda takwas har dana su K /Mata."
"OK sai kin kawo Regular costumer."
Dariya tai kawai ta kashe wayar.
Wani farin ciki taji ya lullub'eta na jin muryar tasa.
*********
Bayan awa guda su ka fito da ga exam d'in mutum uku suka wakilta zuwa kasuwa cikin su takwas da za suyi ankon kala d'aya, daman tuni sun fiddata a waya kowa ya san kalar da kud'in.
Mudatex suka shiga kai tsaye don a nan suka San zasu same ta bada wahala ba.
Bayan sun siyo sun fito a bakin titi sukai sallama kowa yai hanyar unguwarsu ita kuma ta taho da duk atamfofin kamar yanda su ka shirya Ibrahim zai musu d'inki duka iri d'aya.
_*da yuyuwar nan gaba kad'an ya koma na kud'i*_🥰
*Taku ce*
*Y'ar mutan Ja'oji*🙋
👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
*18/10/2019*
_*page*_ *5-6*
Tunda ta sauka cikin adai daita sahu ya ke binta da kallo,ji yai kamar yayi watanni bai ganta ba, a sannu ta k'araso shagon da ledar kayan,Jabir ya fito ya k'arb'i kayan hannunta. A gajiye ta k'arasa ta zauna da fad'in "Ya Allah."
Cikin kulawa su ka gaisa da jama'ar shagon sannan a hankali ta juya gareshi yana amsa waya mirmishi ya sakar mata ita ma ta maida mai martanin mirmishin tana kauda kai gefe.
Bayan ya gama wayar ya juyo gareta da fadin"hajjaju kin karaso kenan ya exam d'in?"
"Hhhhhmmm gani na karaso Khaleelee amma kamar zan fad'i don gajiya."
"Ayya sannu,ai an kusa dai a huta gaba d'aya ko."
"Eh insha Allah nan da two weeks zamu k'are gaba d'aya."
"To Allah ya nuna mana."
"Ameen ya Allah, ga d'inku nan zuwa gobe zanzo ma awan wanda baka dashi da kudin ma gaba d'aya."
"Ok ba damuwa,ina godiya."
Mik'ewa tai tare da fad'in"na wuce sai goben."
"To Allah ya kaimu,ki gaida Mama da takwara."
"Ok zasu ji insha Allah." Ta fad'a tana fita a shagon.
***********
Da dare suna zaune a falo tare da mamansu kallo suke yayin da rabin hankalin Su'ada yana ga bitar karatun ta wani sashin na zuviyarta kuma na tsinkulin ta da maganar Khaleelee, a hankali ta zame ta kwanta kan kujerar da take zaune,lumshe idanuwa tai tana hasko fuskar Khaleelee d'auke da wannan k'ayataccan mirmishin nashi,ita ma ji tai mirmishin ya sib'ice mata.
Mama da ta juyo za tai mata magana ta ga ta rufe ido tana ta mirmishi ita kad'ai,zuba mata ido tai tana karantar yanayin da take ciki a hankali tace "Su'ada karatun kike ko bacci ko ko tunani."
Da sauri ta bud'e idonta tana d'an yak'e tace "Mama karatu fa tuni na gama dashi,kinga duk in da na duba cikin handout d'in ma sai naga na gama da wajan."
"Ok haka ake so, na ga kin kwanta ne kinata mirmishi ke kad'ai kamar an miki albishir da wani abu,ko akwai wata a k'asa ne bamu sani ba."
Ta k'arasa da d'an dariyar tsokana.
Langab'e kai Su'ada tai da fad'in "Mama meye a k'asa wanda zaku kasa sani,kawai dai tunanin duniya nake."
"Hhhhmmm ko tunanin surukina ake?"
Da sauri ta zaro ido tana fad'in "lah Mama wane suruki kuma,Allah ni dai a'a fa."
Dariya Mama tai da su jiddah ganin yanda ta wani rikice kamar bak'on abu ne a gurinta.
Husna tace "Aunty Su'ada kin san me? Jiya yaya Nazeef ke tambayata wai don Allah ko dai kina yin zance da wani ko dashi ne baki son tsayawa kullum yace zai zo sai ki ce karatu karatu."
Hararar ta Su'ada tai tana tab'e baki tace "ku kuka sani ke da shi,daman na san ke ce abokiyar gumata dashi."
"Aa fa ni tambaya ta kawai yayi na bashi amsa da cewa exam kike maybe in kin gama zaki bashi dama ya rink'a zuwa."
kafin Su'ada tai magana Jidda ta d'auka da fad'in "ke dilla k'yale shi,shi shegen tambaya gareshi kamar ya aje mutane."
Dak'uwa Mama tai Mata da fad'in "Dan gidanku yayan ki ne fa kike mai haka,to wai ma ke yace ya na so ne ko me da kike tada jijiyar wuya haka."
Su'ada ta ce " Mama fa ni wallahi ban sonsa ko kad'an shi kamar bai karatu ba,wallahi da a darkin ma ya ke da zama ban san irin gidahumancin da zai yi ba."
Fulon da ke kusa da Mama ta cillowa Su'ada tare da dak'uwa "Wallahi ku kiyayeni da wannan iya shegen,wai to ma in bi ki bawa masu sonki dama yanzu ba sai yaushe? Eh Su'ada nace sai yaushe? da karatu ya rik'eki mun goya miki baya yanzu kuma meye ya rik'e ki tunda dai karatun nan duka kwanaki ya rage a gama shi."
Sassauta murya ta k'ara yi taci gaba da fad'in " Su'ada ki tsaya ki nutsu cikin tarin samarinki ki fidda wanda ya fi kwanta miki a rai,kinga yanzu saura watanni ki cika shekaru ashirin, gashi saura sati biyu ki gama N.C.E d'inki,kinga aure shi yafi dacewa da ke yanzu,don haka na baki lokaci daga nan har zuwa wata guda ki nutsu ki fidda guda wanda hankalinki ya fi kwanciya dashi kinji."
D'aga kai nai a hankali nace "To mama insha Allah zan fidda."
Tun daga wannan lokacin ban k'ara cewa uffan ba har tsawon lokaci na mik'e zuwa d'aki ina cewa "Mama zan kwanta sai da safe."
"Allah ya tashemu lafiya."
Mama ta amsa Mata.
Tunda ta shiga d'aki ta fad'a gado k'irjinta na wani irin bugawa, rintse ido tai tana fad'i cikin ranta ' Allah ka dafa min Allah karka barni da zab'in raina kai min zab'inka,Allah dukkan abunda zai zama alkairi gareni da rayuwata Allah ka zab'a min shi,kai kasan halin da nake ciki kuma kai zaka min maganinsa."
Juyi take tayi tana rok'on Allah mafita, ba ita tai bacci ba sai k'arfe d'ayan dare.
Da safe haka ta tashi jiki ba k'arfi ta shirya ta tafi school.
Tun daga wannan ranar Abubuwa suka cakud'ewa Su'ada ga karatun exam ga tunanin wa zata zab'a cikin tarin samarinta, ga ciwon son Ibrahim dake k'ara azalzalar zuciyarta, nan da nan ta rame tai fiyau da ita.
**********
Ya rage kwanaki Biyar su zana final Pepper ranar basu da exam da yamma tace Jidda ta shirya ta rakata Wajan Khaleelee ta anso d'inkunan su,don da safe take son tafiya musu dashi school.
Tana sanye da doguwar riga marron colour me adon yello me duhu mayafin da tai Rollin kanta yellow sai plat shoe d'in ta shima yello wayarta kawai ta d'auka ban da jaka, tana tsaye cikin gate tana jiran Jidda ta fito su tafi taji tsayuwar mota a k'ofar gate d'in nasu,bata maida hankali ga gate d'inba don bata tunanin gidan nasu za'a shigo, a sannan Jiddah ta fito tana fad'in " Sorry sis na tsaya d'auko wannan material d'in nawa ne in bawa Khaleelee ya d'inka min na gaji da ajiyarsa a akwati.
Ita dai Su'ada bata amsa mata da komai ba illa sa kai da tai don fita a cikin gidan.
A zahiri maza da yawa ke sonta cikin danginta da jama'ar gari,so na aure kuwa,amma bata tab'a ganin abun birgewa tare da su,ga namiji har namiji dai abun birgewa amma ita in ya zo mata da batun so sai taji duk bai birgeta. Tun tuni tsarin halittar Khaleelee ke birgeta,halayensa da tsaftarsa ke k'ara fizgarta gareshi,da tai tunanin kawai iya birgeta ya ke yi,amma yanzu ta tabbatar mugun sonsa ya hudata ya kama zuciyarta,yanzu dole ta nemawa kanta mafita, d'ayan biyu dole a yi d'aya ko dai ta nisanci Khaleelee ta jawa kanta mutunci da girma,in kuma ba haka ba taci gaba da zuwa shagon Khaleelee tabbas asirin zuciyarta zai bayyana.daga nan kuma girmanta da k'imarta da yake gani kuma su shek'e. Wanne kenan za tayi? Ta tambayi kanta cikin tsananin damuwa, wannan take ta sak'awa da kuncewa har bacci yai gaba da ita.
Amma farka warta da wannan batun ta farka,bayan tai sallar asuba ta shiga kaiwa Allah kukanta kan yai Mata maganin wannan ciwo daya kamata, nan wajan bacci ya k'ara gaba da ita.
Jidda k'anwarta da suke kwana d'aki d'aya ce ta ga har wajan k'arfe bakwai bata tashi ba kuma tace musu tana da exam k'arfe takwas don haka ta fara tashin ta "Aunty Su'ada ki tashi kin makara fa."
Da sauri ta mik'e tana salati tare da kallon ogogo,a hanzarce ta tashi ta wuce band'aki.
Duka a gurguje tai shirin nata data fito ko break bata tsaya tayi ba ta amsa kud'i wajan mamansu ta fice.
Tana tafiya cikin adai daita ji take kamar tai iska ta kai kanta school don duka mintina kad'an suka rage takwas ta cika.
Allah ya taimaketa lokacin data isa ga d'akin jarrabawar a sannan malaman da zasu jiresu suka k'araso don haka kusan a tare suka shiga, babu wata ishshshiyar nutsuwa tare da ita sai data ga ta zauna tsaf an bata question pepper a sannan ta saki ajiyar zuciya tasan ta tsira.
***********
Zaune yake kan dakalin k'ofar gidansu bayan ya gama sharar wajan,cikin ransa yake fad'in 'kwana biyu Su'ada shiru ko wucewarta ban gani ba yau tsahon sati biyu kenan, duk zasu fara exam amma ai in zata wuce ta bakin shaginsu tana d'aga musu hannu, ya dubata online ma bata hawa,duk daman in zata fara exam kashe wayanta take babbar sai dai tabar k'aramar a hannunta'
Ciro wayarsa yai cikin aljihu ya fara nemo number d'inta,ringing d'aya biyu ta d'auka yai mata sallama cikin cool voice d'insa,itama cikin fara'arta ta amsa duk da k'ok'arin ta na danne zakuwar ta na karya gane nishad'in da take ciki, "Malama Su'ada kin b'uya gaba d'aya."
"Hhhmmm bari kawai Khaleelee exam ta binne ni,ban gane komai in ba farar takarda in cikata da bulun Biro ba."
Dariya sosai maganar ta bashi bayan ya gama darawa yace "To Allah ya bada sa'a ya sa a fito da kyakykyawar sakamako."
"Ameen na gode Khaleelee, insha Allah yau zan kawo d'inkunan ankon graduation d'inmu,yanzu da mun fito exam zamu wuce kasuwa mu siyo zan kawo ma guda takwas har dana su K /Mata."
"OK sai kin kawo Regular costumer."
Dariya tai kawai ta kashe wayar.
Wani farin ciki taji ya lullub'eta na jin muryar tasa.
*********
Bayan awa guda su ka fito da ga exam d'in mutum uku suka wakilta zuwa kasuwa cikin su takwas da za suyi ankon kala d'aya, daman tuni sun fiddata a waya kowa ya san kalar da kud'in.
Mudatex suka shiga kai tsaye don a nan suka San zasu same ta bada wahala ba.
Bayan sun siyo sun fito a bakin titi sukai sallama kowa yai hanyar unguwarsu ita kuma ta taho da duk atamfofin kamar yanda su ka shirya Ibrahim zai musu d'inki duka iri d'aya.
_*da yuyuwar nan gaba kad'an ya koma na kud'i*_🥰
*Taku ce*
*Y'ar mutan Ja'oji*🙋
👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
*18/10/2019*
_*page*_ *5-6*
Tunda ta sauka cikin adai daita sahu ya ke binta da kallo,ji yai kamar yayi watanni bai ganta ba, a sannu ta k'araso shagon da ledar kayan,Jabir ya fito ya k'arb'i kayan hannunta. A gajiye ta k'arasa ta zauna da fad'in "Ya Allah."
Cikin kulawa su ka gaisa da jama'ar shagon sannan a hankali ta juya gareshi yana amsa waya mirmishi ya sakar mata ita ma ta maida mai martanin mirmishin tana kauda kai gefe.
Bayan ya gama wayar ya juyo gareta da fadin"hajjaju kin karaso kenan ya exam d'in?"
"Hhhhhmmm gani na karaso Khaleelee amma kamar zan fad'i don gajiya."
"Ayya sannu,ai an kusa dai a huta gaba d'aya ko."
"Eh insha Allah nan da two weeks zamu k'are gaba d'aya."
"To Allah ya nuna mana."
"Ameen ya Allah, ga d'inku nan zuwa gobe zanzo ma awan wanda baka dashi da kudin ma gaba d'aya."
"Ok ba damuwa,ina godiya."
Mik'ewa tai tare da fad'in"na wuce sai goben."
"To Allah ya kaimu,ki gaida Mama da takwara."
"Ok zasu ji insha Allah." Ta fad'a tana fita a shagon.
***********
Da dare suna zaune a falo tare da mamansu kallo suke yayin da rabin hankalin Su'ada yana ga bitar karatun ta wani sashin na zuviyarta kuma na tsinkulin ta da maganar Khaleelee, a hankali ta zame ta kwanta kan kujerar da take zaune,lumshe idanuwa tai tana hasko fuskar Khaleelee d'auke da wannan k'ayataccan mirmishin nashi,ita ma ji tai mirmishin ya sib'ice mata.
Mama da ta juyo za tai mata magana ta ga ta rufe ido tana ta mirmishi ita kad'ai,zuba mata ido tai tana karantar yanayin da take ciki a hankali tace "Su'ada karatun kike ko bacci ko ko tunani."
Da sauri ta bud'e idonta tana d'an yak'e tace "Mama karatu fa tuni na gama dashi,kinga duk in da na duba cikin handout d'in ma sai naga na gama da wajan."
"Ok haka ake so, na ga kin kwanta ne kinata mirmishi ke kad'ai kamar an miki albishir da wani abu,ko akwai wata a k'asa ne bamu sani ba."
Ta k'arasa da d'an dariyar tsokana.
Langab'e kai Su'ada tai da fad'in "Mama meye a k'asa wanda zaku kasa sani,kawai dai tunanin duniya nake."
"Hhhhmmm ko tunanin surukina ake?"
Da sauri ta zaro ido tana fad'in "lah Mama wane suruki kuma,Allah ni dai a'a fa."
Dariya Mama tai da su jiddah ganin yanda ta wani rikice kamar bak'on abu ne a gurinta.
Husna tace "Aunty Su'ada kin san me? Jiya yaya Nazeef ke tambayata wai don Allah ko dai kina yin zance da wani ko dashi ne baki son tsayawa kullum yace zai zo sai ki ce karatu karatu."
Hararar ta Su'ada tai tana tab'e baki tace "ku kuka sani ke da shi,daman na san ke ce abokiyar gumata dashi."
"Aa fa ni tambaya ta kawai yayi na bashi amsa da cewa exam kike maybe in kin gama zaki bashi dama ya rink'a zuwa."
kafin Su'ada tai magana Jidda ta d'auka da fad'in "ke dilla k'yale shi,shi shegen tambaya gareshi kamar ya aje mutane."
Dak'uwa Mama tai Mata da fad'in "Dan gidanku yayan ki ne fa kike mai haka,to wai ma ke yace ya na so ne ko me da kike tada jijiyar wuya haka."
Su'ada ta ce " Mama fa ni wallahi ban sonsa ko kad'an shi kamar bai karatu ba,wallahi da a darkin ma ya ke da zama ban san irin gidahumancin da zai yi ba."
Fulon da ke kusa da Mama ta cillowa Su'ada tare da dak'uwa "Wallahi ku kiyayeni da wannan iya shegen,wai to ma in bi ki bawa masu sonki dama yanzu ba sai yaushe? Eh Su'ada nace sai yaushe? da karatu ya rik'eki mun goya miki baya yanzu kuma meye ya rik'e ki tunda dai karatun nan duka kwanaki ya rage a gama shi."
Sassauta murya ta k'ara yi taci gaba da fad'in " Su'ada ki tsaya ki nutsu cikin tarin samarinki ki fidda wanda ya fi kwanta miki a rai,kinga yanzu saura watanni ki cika shekaru ashirin, gashi saura sati biyu ki gama N.C.E d'inki,kinga aure shi yafi dacewa da ke yanzu,don haka na baki lokaci daga nan har zuwa wata guda ki nutsu ki fidda guda wanda hankalinki ya fi kwanciya dashi kinji."
D'aga kai nai a hankali nace "To mama insha Allah zan fidda."
Tun daga wannan lokacin ban k'ara cewa uffan ba har tsawon lokaci na mik'e zuwa d'aki ina cewa "Mama zan kwanta sai da safe."
"Allah ya tashemu lafiya."
Mama ta amsa Mata.
Tunda ta shiga d'aki ta fad'a gado k'irjinta na wani irin bugawa, rintse ido tai tana fad'i cikin ranta ' Allah ka dafa min Allah karka barni da zab'in raina kai min zab'inka,Allah dukkan abunda zai zama alkairi gareni da rayuwata Allah ka zab'a min shi,kai kasan halin da nake ciki kuma kai zaka min maganinsa."
Juyi take tayi tana rok'on Allah mafita, ba ita tai bacci ba sai k'arfe d'ayan dare.
Da safe haka ta tashi jiki ba k'arfi ta shirya ta tafi school.
Tun daga wannan ranar Abubuwa suka cakud'ewa Su'ada ga karatun exam ga tunanin wa zata zab'a cikin tarin samarinta, ga ciwon son Ibrahim dake k'ara azalzalar zuciyarta, nan da nan ta rame tai fiyau da ita.
**********
Ya rage kwanaki Biyar su zana final Pepper ranar basu da exam da yamma tace Jidda ta shirya ta rakata Wajan Khaleelee ta anso d'inkunan su,don da safe take son tafiya musu dashi school.
Tana sanye da doguwar riga marron colour me adon yello me duhu mayafin da tai Rollin kanta yellow sai plat shoe d'in ta shima yello wayarta kawai ta d'auka ban da jaka, tana tsaye cikin gate tana jiran Jidda ta fito su tafi taji tsayuwar mota a k'ofar gate d'in nasu,bata maida hankali ga gate d'inba don bata tunanin gidan nasu za'a shigo, a sannan Jiddah ta fito tana fad'in " Sorry sis na tsaya d'auko wannan material d'in nawa ne in bawa Khaleelee ya d'inka min na gaji da ajiyarsa a akwati.
Ita dai Su'ada bata amsa mata da komai ba illa sa kai da tai don fita a cikin gidan.