Sashe 26
Facala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
To Alhamdulillah Abban Su'ada yayi rawar gani wajan basu gudunmawa a azumin nan tunda yasan halin da Khaleelee ke ciki,don haka kayan abincin da zasu buk'ata har na tsawon watanni ma ya had'a musu,dai dai da gishi sai da aka had'awa Su'ada cikin kayan abincin,tamkar da gara haka aka had'a musu.
Ba magana fa wajan nuna jin dad'in da Khaleelee yayi,yaje gida yayiwa Abba godiya sosai. Abba yace ba komai ai dole ne ya kula dasu.
Har kayan salla ma sai sa Abba tayiwa Su'ada kala uku, duk da yasan Su'ada ba rasa kaya tai ba,amma shi kayan salla in ka saba duk sanda rashi yasa ba kayi ba sai kaji ba dad'i, don haka ta had'a da y'an uwanta yayi mata.
Ita kuwa Nusrat daman tana can gidan tun yaye basu dawo da ita ba.don shi Abba ma so yake wai su bar musu ita,don yanda take kama da yaran gidan ya b'aci, hakan yasa Abban ke bala'in ji da yarinyar.
Alherin da Su'ada ta saba bata canja ba,satin salla taje kasuwa taiwa su Baby da y'ay'an Zakiyya siyayyar d'an kunne da sarka da dai y'an tarkacen yara mata.
*******
Ba wani d'inkin kirki Khaleelee ya samu ba amma dai yafi babu,da kud'in su kai girkin salla da y'an sauran hidima,babu yanda za'ai dai mutum yace yaga wani rashi a tare dasu,duk kuwa da babu wani kud'i a hannun Khaleeleen.
*******
Sannu sannu cikin Su'ada ya shiga wata tara, kamar yanda edd d'inta ya nuna tsakiyar wayan zata haihu,wannan karon Khaleelee bai mata wata siyayya ba,sabida har zuwa lokacin bai zauna daram a shago ba,duk da an gama musu gyara komai da komai,harma sun koma,to duka keke biyu ne a shagon Wanda Su'ada ta bashi kud'i ya siya sai kuma d'aya da Abbanta ya aiko masa dal a cikin kwalinsa.to ana dai samun abunda ake samu,dashi suke d'an cefane.
Don haka kudinta na watanni biyu na albashi da ta amsa bayan gobar nan shi ta had'a ta bada dubu sittin aka siyo mata rago da tunkiya a k'auyensu dake,Wanda tace a barshi sai ta haihu a kawo.
Sauran kud'in hannunta taje kasuwa tai siyayyar Haihuwa,sabida bata da komai duk ta baiwa Sakeena.
Don haka yanzu haihuwa kawai take jira da fatan sauka lafiya.
*********
Da ikon Allah kuwa tsakiyar wata ta haihu,d'anta namiji, cikin koshin lafiya.
Bayan sun dawo gida daga asibiti mama ta buk'aci Khaleelee daya taimaka ya bar Su'ada ta dawo tai wanka ko na sati uku ne a gida, sabida wannan karon babu me zama da ita Innaro bata da lafiya, sannan k'annanta duk suna makaranta ba cikin hutu ake ba
Babu yanda Khaleelee zai iya don haka ya amince,mama tazo da motarta ta d'auke su.
Sakeena dai tunda akai gobarar nan taji a jikinta, don ta tausayaa Khaleelee matuk'a, to amma a wani sashi na ranta take fad'in 'yanzu dai ba wani rawar kai tunda ba'a da komai,amma bayan d'an lokaci tana ta sa ido taga ta inda Su'ada zata gaza amma babu,komai yanda take a wadace haka take abunta.
Washe garin da akai haihuwar Khaleelee yaje gidan su Su'ada, bayan sun gaisa da Mama ya shiga d'akin da Su'ada take,tana zaune tana cin abinci ya shigo,da mirmishi ta tareshi,amma sai ta hango damuwa kan fuskarta, tsam tai da ranta har ya k'araso kusa da ita ya zauna yana d'aukar jinjirin.
Ji tai abincin ya fita a kanta,don haka ta tureshi gefe tare da maido duka hankakinta ga Khaleeleen.
A sanyaye ta gaisheshi ya amsa yana kirkiro mirmishin da bai kai zuci ba.
Kafeshi tai da ido cikin kallon tuhuma,abunda yasashi sakkowa kusa da ita ya zauna tare da damk'e hannunta cikin nasa,kallon juna suke na d'an lokaci kafin ta d'ora kanta a kafad'arsa.cikin k'aramar murya take mai magana. . . .
[2/24, 12:04 AM] LAYUZA KABIR: 👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
_*page*_*45-46*
Bayan tafiyar Khaleelee Su'ada taje d'akin mama ta sameta tanaiwa Nusrat shirin bacci. Zama tai gefen gadon tana duban mama.
Bayan ta k'arasa sa mata riga ta kwantar da ita gefe sannan ta dawo da hankalinta ga Su'adan "ya akayi ne Su'ada?"
Gyara zama tai tana kallon maman cikin serious voice ta fara magana"Mama daman wata magana mukai da Abban Nusrat yanzu da yazo,kan batun taron suna ne,hidima ta mai yawa,kuma kinsan har yanzu ba wai gama had'a shagon su kai ba,to shine nace mai kawai ba sai anyi taron suna ba."
Cikin girma da nutsuwa mama tace "Na sani Su'ada, na san halin da mijinki yake ciki don haka nace ki dawo gida,ai bazan rasa me zauna miki ba,kawai dai ban son a k'ara mishi nauyi kan wanda yake kansa yanzu,don haka ki kwantar da hankalinki kinji,komai na taron suna za'a yi,kuma zan fad'a mishi karya kashe naira biyar d'insa,yaji ma da gyaran wajan Neman kud'insa, ni da mahaifinki muna dashi Su'ada to in bamu taimaka muku ba meye amfanin samun namu,kuma kema kullum ina k'ara Jan hankalinki,duk abunda zaki samu ki d'auka keda abun karkashin igiyar aure kuke,don haka karki zauna tara kud'i cikin account mijinki yana cikin matsalar kud'i, ki fiddasu ki bashi ya rink'a hidima dasu,basu da wani amfani bayan wannan."
Gyad'a kai Su'ada tai da fad'in "Mama ba kud'i cikin account d'ina duk na fitar dasu na bashi,dasu ne kuma aka bada kud'in ragunan a darki, sannan mukai siyayyar haihuwa,sauran abunda ke hannuna yanzu dubu goma ne,sune daman zan baki ki Siyo ma yaron rigunan fitar suna."
Cikin jin dad'i mama tace "Masha Allah, haka nake sonki dashi Su'ada, ki zama me tausayin mijinki ako wane lokaci, shima zai zama me tausayinki komai runtsi.
****Bayan fitar Su'ada a d'akin, mama ta tashi zuwa d'akin Abba,anan ta zayyane mai duk yanda sukai da Su'ada, jinjina kai yayi,yana fad'in "To yanzu yanda za'ayi kiyi list na duk abunda kike ganin zaku buk'ata sai ki lissafa kud'in ki fad'a min in baku,kuma insha Allah in na koma zan k'ara turo da kud'i ki bawa Ibrahim d'in ya k'arasa gyaran shagon.
Godiya sosai Mama tai mai,shi yasa a duniya take jin tsananin son mijinta,don Abban su Su'ada yana iya juyewa iyalansa duk abunda ke aljihunsa ya tashi ba ko sisi a jikinsa,shi yasa kuwa Allah yake k'ara bud'a mishi harkar samunsa.ko Wannan dawowar da yayi sai da ya k'ara gyara musu gidan,har sabon fenti akai.
Sai da safe Mama take fad'awa Su'ada yanda sukai da Abba,inda sabo Su'ada ta saba da hidima da kyautatawar mahaifinsu garesu,amma wannan karon tana jin nauyi da wata irin ninki k'aunar mahaifan nata a zuciyarta.
Zuwa tai d'aki ta sami Abban yana zaune Nusrat na kan cinyarsa,tanata gwalangwalan d'inta,bayan ta zauna ta gaida Abban,ya amsa cikin kulawa yana tambayarta ya Jinjirin,cikin yanayin da ta saba yiwa Abban nasu magana cikin shagwab'a tace" Abba wannan yaron kuka gareshi, sam bai barinmu barcin dare, Nusrat ta fishi hakuri, ni duk ji ma nake kamar na dakeshi."
"To ai da kin dake shin zai yi shiru da wuri,kinga muma kunnuwanmu sai su huta sa kukan nashi."
Mama dake shigowa d'akin d'auke da jinjirin ta fad'a.
Dariya Su'ada da Abba su kai a tare,sannan Su'ada ta tsaida hankakinta waje guda tana yiwa Abban godiya.
Shi dariya ma abun ya bashi,yace "Su'ada don na muku hidima shikenan kike ta wannan godiyar? Shin kina da wani me yi miki bayan mu iyayenki da kuma mijinki? hakkinki duka yana kanmu da mijinki,kuma Ibrahim yaron kirki ne,kullum k'ara yaba hankalinsa nake,bayan wannan jarabtar data sameshi na san zuwa yanzu da tuni ya gama komai daya rataya a wuyansa,kamar yanda Mamanku ta sanar dani irin namijin k'ok'arin da yayi a wancan karon,to a wannan karon ma tunda munsan babu ne mu iyaye sai mu tallafa ai."
Tsawon lokaci Abba ya d'auka da Su'ada yana mata nasiha da k'ara sanar da ita girman mijinta gareta, har kwalla sai da tai.tana k'ara yiwa iyayenta addu'ar fatan dacewa duniya da lahira.
*********
Yau ma da dare Khaleelee yazo gidan,a waje suka had'u da Abba, bayan sun gaisa cikin girmamawa,Khaleelee ya k'ara k'asa da kansa sannan yace "Abba daman ina son maka maganar sa suna,nai mai hud'uba da sunanka."
Sosai fara'ar Abba ta k'aru,yace "To madalla Allah ya raya mana shi cikin aminci yayi musu albarka."
Cikin jin kunya Yake amsawa sannan ta tashi ya k'asara ciki.
Abba yaji dad'in takwarancin da Khaleelee yai mai,don haka yana shiga d'aki yake sanar da Mama zancen,itama taji dad'i sosai.
****Lokacin da ya shiga d'akin duk su Jidda na ciki,bayan sun gaisa su ka fita su ka basu waje,a kujerar gefen gadon ya zauna yana fad'in "Washhh yau d'inkin ki ya gajiyar dani fa matar tela."
Y'ar dariya tai tana gaidashi tare da tambayarsa gida dasu Baba,yace "To Baba yana can yana fama da jiki sai godiyar Allah."
Cikin tausayawa tace "Allah sarki Baba,don Allah kai mishi sannu in ka koma."
Jinjina Kai yai yana fad'in "mik'o min Abban.ko yau rowarsa ake min."
Kallonsa tai cikin rashin fahimta tace "Abba kuma? Ya za'ai ma rowar abunka."
Bayan ta mik'a mai shi tace "Naji kace Abba."
Gyad'a kai yai yana mirmishi yace "Sunan Abba nasa mai,da fatan yayi miki."
Da fara'a sosai tace "Wayyo, amma naji dad'i fa,Allah ya raya mana shi cikin aminci."
"Amin ya Allah, kin san Yanzu naga Nusrat hannun Khaleelee wai nace tazo ta mak'ale kafad'a,ina ganin fa ta manta ni."
"Ah haba ya za'ai ta mantaka, kawai yanzu ta saba dasu ne,ko nifa bata yarda dani."
Cikin tsokana yace "To ko mu barmusu ita ne?"
Itama cikin tsokanar tace "In zaka iya ba."
"Kiji wai in zan iya,meye don na barwa Mama ita."
D'age gira tai tana y'ar dariya tace "Kasan Abba ma jiya sai da yace wai wannan y'ar ai tasu ce,mu ga namu mun Haifa."
Dariya yai sosai yace " Damu da su duk muna karkashin Su Abba muke."
D'an gyara zama tai kafin ta fara bashi Labarin Abunda Abba yace kan suna da duk abunda suke buk'ata ."
Ba magana fa wajan nuna jin dad'in da Khaleelee yayi,yaje gida yayiwa Abba godiya sosai. Abba yace ba komai ai dole ne ya kula dasu.
Har kayan salla ma sai sa Abba tayiwa Su'ada kala uku, duk da yasan Su'ada ba rasa kaya tai ba,amma shi kayan salla in ka saba duk sanda rashi yasa ba kayi ba sai kaji ba dad'i, don haka ta had'a da y'an uwanta yayi mata.
Ita kuwa Nusrat daman tana can gidan tun yaye basu dawo da ita ba.don shi Abba ma so yake wai su bar musu ita,don yanda take kama da yaran gidan ya b'aci, hakan yasa Abban ke bala'in ji da yarinyar.
Alherin da Su'ada ta saba bata canja ba,satin salla taje kasuwa taiwa su Baby da y'ay'an Zakiyya siyayyar d'an kunne da sarka da dai y'an tarkacen yara mata.
*******
Ba wani d'inkin kirki Khaleelee ya samu ba amma dai yafi babu,da kud'in su kai girkin salla da y'an sauran hidima,babu yanda za'ai dai mutum yace yaga wani rashi a tare dasu,duk kuwa da babu wani kud'i a hannun Khaleeleen.
*******
Sannu sannu cikin Su'ada ya shiga wata tara, kamar yanda edd d'inta ya nuna tsakiyar wayan zata haihu,wannan karon Khaleelee bai mata wata siyayya ba,sabida har zuwa lokacin bai zauna daram a shago ba,duk da an gama musu gyara komai da komai,harma sun koma,to duka keke biyu ne a shagon Wanda Su'ada ta bashi kud'i ya siya sai kuma d'aya da Abbanta ya aiko masa dal a cikin kwalinsa.to ana dai samun abunda ake samu,dashi suke d'an cefane.
Don haka kudinta na watanni biyu na albashi da ta amsa bayan gobar nan shi ta had'a ta bada dubu sittin aka siyo mata rago da tunkiya a k'auyensu dake,Wanda tace a barshi sai ta haihu a kawo.
Sauran kud'in hannunta taje kasuwa tai siyayyar Haihuwa,sabida bata da komai duk ta baiwa Sakeena.
Don haka yanzu haihuwa kawai take jira da fatan sauka lafiya.
*********
Da ikon Allah kuwa tsakiyar wata ta haihu,d'anta namiji, cikin koshin lafiya.
Bayan sun dawo gida daga asibiti mama ta buk'aci Khaleelee daya taimaka ya bar Su'ada ta dawo tai wanka ko na sati uku ne a gida, sabida wannan karon babu me zama da ita Innaro bata da lafiya, sannan k'annanta duk suna makaranta ba cikin hutu ake ba
Babu yanda Khaleelee zai iya don haka ya amince,mama tazo da motarta ta d'auke su.
Sakeena dai tunda akai gobarar nan taji a jikinta, don ta tausayaa Khaleelee matuk'a, to amma a wani sashi na ranta take fad'in 'yanzu dai ba wani rawar kai tunda ba'a da komai,amma bayan d'an lokaci tana ta sa ido taga ta inda Su'ada zata gaza amma babu,komai yanda take a wadace haka take abunta.
Washe garin da akai haihuwar Khaleelee yaje gidan su Su'ada, bayan sun gaisa da Mama ya shiga d'akin da Su'ada take,tana zaune tana cin abinci ya shigo,da mirmishi ta tareshi,amma sai ta hango damuwa kan fuskarta, tsam tai da ranta har ya k'araso kusa da ita ya zauna yana d'aukar jinjirin.
Ji tai abincin ya fita a kanta,don haka ta tureshi gefe tare da maido duka hankakinta ga Khaleeleen.
A sanyaye ta gaisheshi ya amsa yana kirkiro mirmishin da bai kai zuci ba.
Kafeshi tai da ido cikin kallon tuhuma,abunda yasashi sakkowa kusa da ita ya zauna tare da damk'e hannunta cikin nasa,kallon juna suke na d'an lokaci kafin ta d'ora kanta a kafad'arsa.cikin k'aramar murya take mai magana. . . .
[2/24, 12:04 AM] LAYUZA KABIR: 👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
_*page*_*45-46*
Bayan tafiyar Khaleelee Su'ada taje d'akin mama ta sameta tanaiwa Nusrat shirin bacci. Zama tai gefen gadon tana duban mama.
Bayan ta k'arasa sa mata riga ta kwantar da ita gefe sannan ta dawo da hankalinta ga Su'adan "ya akayi ne Su'ada?"
Gyara zama tai tana kallon maman cikin serious voice ta fara magana"Mama daman wata magana mukai da Abban Nusrat yanzu da yazo,kan batun taron suna ne,hidima ta mai yawa,kuma kinsan har yanzu ba wai gama had'a shagon su kai ba,to shine nace mai kawai ba sai anyi taron suna ba."
Cikin girma da nutsuwa mama tace "Na sani Su'ada, na san halin da mijinki yake ciki don haka nace ki dawo gida,ai bazan rasa me zauna miki ba,kawai dai ban son a k'ara mishi nauyi kan wanda yake kansa yanzu,don haka ki kwantar da hankalinki kinji,komai na taron suna za'a yi,kuma zan fad'a mishi karya kashe naira biyar d'insa,yaji ma da gyaran wajan Neman kud'insa, ni da mahaifinki muna dashi Su'ada to in bamu taimaka muku ba meye amfanin samun namu,kuma kema kullum ina k'ara Jan hankalinki,duk abunda zaki samu ki d'auka keda abun karkashin igiyar aure kuke,don haka karki zauna tara kud'i cikin account mijinki yana cikin matsalar kud'i, ki fiddasu ki bashi ya rink'a hidima dasu,basu da wani amfani bayan wannan."
Gyad'a kai Su'ada tai da fad'in "Mama ba kud'i cikin account d'ina duk na fitar dasu na bashi,dasu ne kuma aka bada kud'in ragunan a darki, sannan mukai siyayyar haihuwa,sauran abunda ke hannuna yanzu dubu goma ne,sune daman zan baki ki Siyo ma yaron rigunan fitar suna."
Cikin jin dad'i mama tace "Masha Allah, haka nake sonki dashi Su'ada, ki zama me tausayin mijinki ako wane lokaci, shima zai zama me tausayinki komai runtsi.
****Bayan fitar Su'ada a d'akin, mama ta tashi zuwa d'akin Abba,anan ta zayyane mai duk yanda sukai da Su'ada, jinjina kai yayi,yana fad'in "To yanzu yanda za'ayi kiyi list na duk abunda kike ganin zaku buk'ata sai ki lissafa kud'in ki fad'a min in baku,kuma insha Allah in na koma zan k'ara turo da kud'i ki bawa Ibrahim d'in ya k'arasa gyaran shagon.
Godiya sosai Mama tai mai,shi yasa a duniya take jin tsananin son mijinta,don Abban su Su'ada yana iya juyewa iyalansa duk abunda ke aljihunsa ya tashi ba ko sisi a jikinsa,shi yasa kuwa Allah yake k'ara bud'a mishi harkar samunsa.ko Wannan dawowar da yayi sai da ya k'ara gyara musu gidan,har sabon fenti akai.
Sai da safe Mama take fad'awa Su'ada yanda sukai da Abba,inda sabo Su'ada ta saba da hidima da kyautatawar mahaifinsu garesu,amma wannan karon tana jin nauyi da wata irin ninki k'aunar mahaifan nata a zuciyarta.
Zuwa tai d'aki ta sami Abban yana zaune Nusrat na kan cinyarsa,tanata gwalangwalan d'inta,bayan ta zauna ta gaida Abban,ya amsa cikin kulawa yana tambayarta ya Jinjirin,cikin yanayin da ta saba yiwa Abban nasu magana cikin shagwab'a tace" Abba wannan yaron kuka gareshi, sam bai barinmu barcin dare, Nusrat ta fishi hakuri, ni duk ji ma nake kamar na dakeshi."
"To ai da kin dake shin zai yi shiru da wuri,kinga muma kunnuwanmu sai su huta sa kukan nashi."
Mama dake shigowa d'akin d'auke da jinjirin ta fad'a.
Dariya Su'ada da Abba su kai a tare,sannan Su'ada ta tsaida hankakinta waje guda tana yiwa Abban godiya.
Shi dariya ma abun ya bashi,yace "Su'ada don na muku hidima shikenan kike ta wannan godiyar? Shin kina da wani me yi miki bayan mu iyayenki da kuma mijinki? hakkinki duka yana kanmu da mijinki,kuma Ibrahim yaron kirki ne,kullum k'ara yaba hankalinsa nake,bayan wannan jarabtar data sameshi na san zuwa yanzu da tuni ya gama komai daya rataya a wuyansa,kamar yanda Mamanku ta sanar dani irin namijin k'ok'arin da yayi a wancan karon,to a wannan karon ma tunda munsan babu ne mu iyaye sai mu tallafa ai."
Tsawon lokaci Abba ya d'auka da Su'ada yana mata nasiha da k'ara sanar da ita girman mijinta gareta, har kwalla sai da tai.tana k'ara yiwa iyayenta addu'ar fatan dacewa duniya da lahira.
*********
Yau ma da dare Khaleelee yazo gidan,a waje suka had'u da Abba, bayan sun gaisa cikin girmamawa,Khaleelee ya k'ara k'asa da kansa sannan yace "Abba daman ina son maka maganar sa suna,nai mai hud'uba da sunanka."
Sosai fara'ar Abba ta k'aru,yace "To madalla Allah ya raya mana shi cikin aminci yayi musu albarka."
Cikin jin kunya Yake amsawa sannan ta tashi ya k'asara ciki.
Abba yaji dad'in takwarancin da Khaleelee yai mai,don haka yana shiga d'aki yake sanar da Mama zancen,itama taji dad'i sosai.
****Lokacin da ya shiga d'akin duk su Jidda na ciki,bayan sun gaisa su ka fita su ka basu waje,a kujerar gefen gadon ya zauna yana fad'in "Washhh yau d'inkin ki ya gajiyar dani fa matar tela."
Y'ar dariya tai tana gaidashi tare da tambayarsa gida dasu Baba,yace "To Baba yana can yana fama da jiki sai godiyar Allah."
Cikin tausayawa tace "Allah sarki Baba,don Allah kai mishi sannu in ka koma."
Jinjina Kai yai yana fad'in "mik'o min Abban.ko yau rowarsa ake min."
Kallonsa tai cikin rashin fahimta tace "Abba kuma? Ya za'ai ma rowar abunka."
Bayan ta mik'a mai shi tace "Naji kace Abba."
Gyad'a kai yai yana mirmishi yace "Sunan Abba nasa mai,da fatan yayi miki."
Da fara'a sosai tace "Wayyo, amma naji dad'i fa,Allah ya raya mana shi cikin aminci."
"Amin ya Allah, kin san Yanzu naga Nusrat hannun Khaleelee wai nace tazo ta mak'ale kafad'a,ina ganin fa ta manta ni."
"Ah haba ya za'ai ta mantaka, kawai yanzu ta saba dasu ne,ko nifa bata yarda dani."
Cikin tsokana yace "To ko mu barmusu ita ne?"
Itama cikin tsokanar tace "In zaka iya ba."
"Kiji wai in zan iya,meye don na barwa Mama ita."
D'age gira tai tana y'ar dariya tace "Kasan Abba ma jiya sai da yace wai wannan y'ar ai tasu ce,mu ga namu mun Haifa."
Dariya yai sosai yace " Damu da su duk muna karkashin Su Abba muke."
D'an gyara zama tai kafin ta fara bashi Labarin Abunda Abba yace kan suna da duk abunda suke buk'ata ."