Sashe 18
Facala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
[2/23, 11:56 PM] LAYUZA KABIR: 👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
_*Innalillahi wa'inna ilaihi ra'jiun.Ha'ki'ka dukkan me rai mamaci ne,Wannan aya ta tabbata a kan mahaifin malamina, ina rok'on Allah ya jik'ansa ya gafarta zunubansa ya kyautata makwancinsa,Allah yasa mutuwa hutu ce gareshi*🙏🙏🙏😢
_*page*_*29-30*
A Sannu cikin aminci a ka fad'a cikin watan Ramadana, a lokacin kuma ayyuka sun gama shan kan Khaleelee, duk da yana k'ok'ari wajan ganin ya bawa Su'ada lokacinta don kar ya shiga hak'k'inta,hakan yasa ya tsara lokutansa na dawowa gida. K'arfe goma na safe zai fita,ba zai dawo ba sai gab da shan ruwa,to in yasha ruwa ya d'an huta, da an kira asham in yaje yai salla ya dawo gida zai yo,to duk lokacin nan nata ne,sai wajan sha d'aya na dare zai koma shago,ba zai dawo ba sai yayi sallar asuba.
Sosai su ka tsara abubuwansu don kaucewa shiga shingen Allah, sabida Khaleelee ya saba mata matuk'ar ya na gida to ko yaushe tana jikinsa, shi kanshi ya saba bai so ya ganta nesa dashi,to da Allah ya taimakesu da rana duka yana shago,lokacin da zai dawo kuma kad'an ya rage asha ruwa,kafin yai wanka ya shirya an kira salla,sauran lokutan kuma duk nasu ne,anan suke more soyayyarsu su maida tsinkakken yawu.😝
Da asuba kuwa in ya dawo ya taro gajiya da bacci yana shigowa sai bacci, yana kwance ma take shiryawa ta tafi aiki.
Wai wani aiki sai FACALA wai wannan dawowar ma da yake gida na dare sai da ya zama abun k'orafi a gun Sakeena, sabida rannan ya dawo su Baby sun shigo kallon (dad'in kowa) yace su je bacci zai yi ya kashe kayan kallon,to da su ka je su ka fad'a mata da safe tai ta yada magana.
Su'ada na jinta tana fad'in "Mace me jarabar namiji dai bata wani lasting, ko yaushe miji manne da kai kamar fata, da azuminma ba za'a hak'ura ba Allah dai ya kyauta."
Sosai Abun ya bawa Su'ada dariya tana ayyukanta tana dariya,don ita yanzu abun Sakeena ba kowanne ke damunta ba,duk da ma yanzu an d'an sami sauk'i tun da a Kai case d'in d'aki bata k'ara tado wata ba,sai dai habaici kam Su'ada na shanshi.
Sati guda da d'aukar azumi Abban su Su'ada ya dawo,nan ya aiko mata da k'wai cikin wani dogon farin boket,Su'ada ta kira Abbanta tai ta mai godiya, da Khaleelee ma ya dawo ya gani ya kira waya yai godiya,bayan an sha ruwa Su'ada tai maganar "Khaleelee kaga nace kaga muna da k'wan da ka siyo daman,kuma yanzu ana zafi sosai tunda k'wan da yawa zai iya lalacewa kafin wani lokaci,nace me zai hana mu raba uku a bawa Maman Abba kaso d'aya a aikawa Zakiyya kaso d'aya?'
Idanuwansa da ke lumshe ya bud'e a kanta yana mata kallon shiga rai,sannan a hankali yace " Duk yanda ki kai ya yi my world, komai kika tsara banda ja a kai don duk shawarar da ki ka kawo me kyauce,ki basun Allah yayi miki albarka ya baki babban rabo a duniya da lahira matar rufin asiri."
Cikin farin ciki ta fara godiya "Nima na gode mijin wuce sa'a, ko yaushe 'karfafa min gwiwa ka ke akan duk abunda nazo da shi,ina jin dad'in hakan kuma ina alfahari da kai a kowane lokaci."
Washe gari da safe Su'ada ta raba k'wan ta kawowa Sakeena, kadaran kadahan ta amsa tai godiya, sannan Su'ada tace "Don Allah Maman Abba zan aiki Abba gidan Zakiyya ya kai mata sa'ko in ba inda za ki aikeshi."
"Ba inda zan aikeshi,sai dai kin San dake ya na azumi kuma da gani yana bashi wahla."
Da sauri yaron yace "A'a Mama ni dai zance don Allah, ba wani wuya da azumin ke bani,kuma ai a napep zan je ko Aunty?"
Gyad'a mai kai Su'ada tai da fad'in "Eh zan baka kud'in mota wanda za'a kaika har k'ofar gidan in ma jiranka zai ka kai ka fito Ku dawo duk zan bada."
Bai k'ara bi ta kan uwar ba ya shiga cire kayan jikinsa don sauya wasu.
Ita kam Su'ada komawa tai d'akin ta sami bokiti me murfi zuba k'wan a ciki,da kansa ya biyo ta d'aki ya amsa sak'on.
*Manege plss*🥰
*Taku ce*
*Yar mutan Jaoji*🙋
[2/23, 11:58 PM] LAYUZA KABIR: 👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
_ALLAH KAI MANA MAGANIN DAMUWARMU_🙏🙏🙏
_*page*_*31-32*
Haka aka ci gaba da gudanar da ibadar azumin Ramadan cikin falala ta ubangiji, lokacin da azumi ya raba Su'ada ta shirya zuwa gida yi musu barka da shan ruwa,tun safe ta tafi,sai bayan sallar Isha'i Khaleelee yaje ya d'auko ta,da abinci ta taho don ba girki Zata yi ba,ai kuwa suna zuwa gida yace "Su'ada zuba min abincin nan in ci,na kasa yin bud'e baki gamsashshe duk abunda nasa a bakin sai naji ba d'and'ano,kin gama saba min da girkinki Su'ada, ban jin dad'in wani abinci bayan naki."
Cikin jin dad'in yabon da yake mata tai y'ar dariya tare da fad'in "To shi wannan d'in da za ka ci kasan wa ya dafa ne?"
Shima mirmishi yai da fad'in "Koma ya dafa in dai daga gidanku yake to d'and'anon iri d'aya ne,in Mama ce tai to zaifi ma naki dad'i,tunda gunta ki ka koya,in kuma su Jidda ne su kai to d'and'anon zai zamo d'aya tunda duk gu guda kuka koya."
Tana dariya ta zuba mai,Sannu ta dawo kusa dashi take bashi a baki,a hankali cikin kwantar da murya take mai hira "Khaleelee na,kasan me kuwa? Allah ko yau nima ban wani maida hankali wajan shan ruwa ba,sabida duk sai naji ni wani sakayau, na saba komai tare da kai,daurewa kawai nai fa,amma da kamar na kiraka nace kazo na kasa cin komai."
Kanne ido d'aya yai yana d'age mata gira sannan ya ce "Eh da kin kirani,don a dai dai lokacin nima hakanne tare dani,duk da na san ke fa harda kewan wani abu ya hanaki sakewan."
da sauri ta d'an zaro ido da fad'in
"Kai, kewan me kake so kace?"
Kauda kai yai cikin basarwa yace "Kewan wannan jikin mana,kin saba kina cin abinci ina miki abubuwa,kina mak'alemin a jiki kamar mage."
Turo baki tai tace "A'a ni dai, abunda na san zan dawo na sameshi,kuma yanzuma ka jangwalo kaci gaba da ci da kanka ni kuma in kwanta anan."
Ta fad'a tana zamewa a jikinsa.
Ci gaba yai da cin abincinsa yana k'ara tsokanarta da wai daman haka take so,ita dai bata tanka shi ba tai lamo a jikinsa.
Da k'yar Su'ada ta rok'i Khaleelee ya barta zuwa kasuwa a lokacin da salla ta rage sati guda,K'annanta taiwa siyayya duk da da taje gida ta tadda an gama sai musu komai to amma hakan ba zai hana ta kyautata musu ba,under wear's ta sai musu da kayan kwalliya,sannan ta siyawa k'aninta Khaleelee wasu takalmi masu kyau.
'Ya'yan Zakiyya kuwa da Baby ta sai musu y'an kunne da sark'a sa su Abun hannu,ta siya musu kayan kwalliya,sannan ta had'awa Baby harda jaka,sabida tana jin kullum yanda yarinyar ke nacin Sakeena ta siya Mata jaka duk 'kawayenta an sai musu,amma uwar tai mirsisi da rantsuwar ba zata siya ba,kuma fa badan bata da kud'in ba kawai siyan ne ba niyya kuma alhalin Ubansu ya bada kud'in ai musu siyayya.mutuniyarta Islam kuwa wata riga da wando masu kyau y'an kanti ta siya mata da kayan kitso dasu ribbons masu kyau kalar kayan.
Itama taiwa kanta siyayyar duk abunda take da buk'ata, sannan ta tsaya wajan y'an girki ta had'a duk wani abu da tasan za ta buk'ata da sallar nan.
Lokacin da ta dawo gida bata baiwa kowa abunsa ba,sai da dare data Nunawa mijinta sannan ta fito da na su Baby ta k'wala mata kira,da gudu yarinyar tazo da fad'in "Aunty gani."
Mik'a mata kayan tai tace "Sark'a dasu dan kunne da jaka naki ne,sauran kuma duk na Islam ne."
Ihun murna yarinyar tasa ta fita a guje ko damar godiya bata samu yi mata ba don murna.
Lokacin yaya Muktar na nan ta shiga falo da kayan tana ihun murna,ajiyewa tai a gabansa tana d'aukar jakar tace "Abba kaga Aunty Amarya ce ta siyo min jaka,Wallahi Abba kaga daman kullum sai nacewa Mamanmu ta siya min sai tak'i,gashi Aunty ta siya min,kai wallahi naji dad'i na godewa Allah na godewa Aunty Amarya,Abba sauran kayan na Islam ne."
Ganin yanda duk ta rud'e da murna yasa Abban nasu dariya yace "Kai gaskiya yau Aunty Amarya tasa Maman mamanta cikin farin ciki,To maza koma kice mata an gode don da ganin yanda kike a rude biki ma yi godiya ba."
Juyawa tai da sauri sak'ale da jakarta ta koma taiwa Su'ada godiya.
Islam ma tana murna da aka gwada mata kayan,yace kema je kicewa Aunty an gode.
Bayan fitarta ya kalli Sakeena da take d'an yak'e kadaran kadahan yace "Sakeena je kicewa Su'ada nace na gode ."
D'an tab'e baki tai tace "To godiyar me kaikuma za ka mata,ba ga yaran sun je sun yi ba,kuma nima in ta fito da safe zan mata."
Tsayawa kawai yai yana kallonta da takaici yace "Yanzu mutum yai wa 'ya'anki wannan hidimar amma ki zauna sai da safe zaki gode mata,alhalin kuna gida guda,Tashi don Allah ni ki je ki mata godiya."
Ba dan taso ba ta tashi ta fice.
A turb'une tai sallama hakan ya sa ba suji Sosai ba,ita kuma bata k'ara ba ta sako kai falon a dai dai lokacin da Su'ada ta haye kan ruwan cikin Khaleelee tana k'ok'arin k'wace wayarta da ya d'auka wai zai shiga wani group d'in ta na WathApp da yaga an sa SIRRINMU MATA, sosai su ke kokawa da juna,dariya taci k'arfin Khaleelee wanda yasa take k'ok'arin cin galaba ta k'wace wayar.
Sakeena da ke tsaye tana kallonsu wani k'ululun bak'in ciki ya turnik'eta,wato ma suna jinta su ka k'i amsawa,sabida su na wasan jakai😃🤭,juyawa tai ta bar falon,data koma tacewa Yaya Muktar ai tai mata godiyar.
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
_*Innalillahi wa'inna ilaihi ra'jiun.Ha'ki'ka dukkan me rai mamaci ne,Wannan aya ta tabbata a kan mahaifin malamina, ina rok'on Allah ya jik'ansa ya gafarta zunubansa ya kyautata makwancinsa,Allah yasa mutuwa hutu ce gareshi*🙏🙏🙏😢
_*page*_*29-30*
A Sannu cikin aminci a ka fad'a cikin watan Ramadana, a lokacin kuma ayyuka sun gama shan kan Khaleelee, duk da yana k'ok'ari wajan ganin ya bawa Su'ada lokacinta don kar ya shiga hak'k'inta,hakan yasa ya tsara lokutansa na dawowa gida. K'arfe goma na safe zai fita,ba zai dawo ba sai gab da shan ruwa,to in yasha ruwa ya d'an huta, da an kira asham in yaje yai salla ya dawo gida zai yo,to duk lokacin nan nata ne,sai wajan sha d'aya na dare zai koma shago,ba zai dawo ba sai yayi sallar asuba.
Sosai su ka tsara abubuwansu don kaucewa shiga shingen Allah, sabida Khaleelee ya saba mata matuk'ar ya na gida to ko yaushe tana jikinsa, shi kanshi ya saba bai so ya ganta nesa dashi,to da Allah ya taimakesu da rana duka yana shago,lokacin da zai dawo kuma kad'an ya rage asha ruwa,kafin yai wanka ya shirya an kira salla,sauran lokutan kuma duk nasu ne,anan suke more soyayyarsu su maida tsinkakken yawu.😝
Da asuba kuwa in ya dawo ya taro gajiya da bacci yana shigowa sai bacci, yana kwance ma take shiryawa ta tafi aiki.
Wai wani aiki sai FACALA wai wannan dawowar ma da yake gida na dare sai da ya zama abun k'orafi a gun Sakeena, sabida rannan ya dawo su Baby sun shigo kallon (dad'in kowa) yace su je bacci zai yi ya kashe kayan kallon,to da su ka je su ka fad'a mata da safe tai ta yada magana.
Su'ada na jinta tana fad'in "Mace me jarabar namiji dai bata wani lasting, ko yaushe miji manne da kai kamar fata, da azuminma ba za'a hak'ura ba Allah dai ya kyauta."
Sosai Abun ya bawa Su'ada dariya tana ayyukanta tana dariya,don ita yanzu abun Sakeena ba kowanne ke damunta ba,duk da ma yanzu an d'an sami sauk'i tun da a Kai case d'in d'aki bata k'ara tado wata ba,sai dai habaici kam Su'ada na shanshi.
Sati guda da d'aukar azumi Abban su Su'ada ya dawo,nan ya aiko mata da k'wai cikin wani dogon farin boket,Su'ada ta kira Abbanta tai ta mai godiya, da Khaleelee ma ya dawo ya gani ya kira waya yai godiya,bayan an sha ruwa Su'ada tai maganar "Khaleelee kaga nace kaga muna da k'wan da ka siyo daman,kuma yanzu ana zafi sosai tunda k'wan da yawa zai iya lalacewa kafin wani lokaci,nace me zai hana mu raba uku a bawa Maman Abba kaso d'aya a aikawa Zakiyya kaso d'aya?'
Idanuwansa da ke lumshe ya bud'e a kanta yana mata kallon shiga rai,sannan a hankali yace " Duk yanda ki kai ya yi my world, komai kika tsara banda ja a kai don duk shawarar da ki ka kawo me kyauce,ki basun Allah yayi miki albarka ya baki babban rabo a duniya da lahira matar rufin asiri."
Cikin farin ciki ta fara godiya "Nima na gode mijin wuce sa'a, ko yaushe 'karfafa min gwiwa ka ke akan duk abunda nazo da shi,ina jin dad'in hakan kuma ina alfahari da kai a kowane lokaci."
Washe gari da safe Su'ada ta raba k'wan ta kawowa Sakeena, kadaran kadahan ta amsa tai godiya, sannan Su'ada tace "Don Allah Maman Abba zan aiki Abba gidan Zakiyya ya kai mata sa'ko in ba inda za ki aikeshi."
"Ba inda zan aikeshi,sai dai kin San dake ya na azumi kuma da gani yana bashi wahla."
Da sauri yaron yace "A'a Mama ni dai zance don Allah, ba wani wuya da azumin ke bani,kuma ai a napep zan je ko Aunty?"
Gyad'a mai kai Su'ada tai da fad'in "Eh zan baka kud'in mota wanda za'a kaika har k'ofar gidan in ma jiranka zai ka kai ka fito Ku dawo duk zan bada."
Bai k'ara bi ta kan uwar ba ya shiga cire kayan jikinsa don sauya wasu.
Ita kam Su'ada komawa tai d'akin ta sami bokiti me murfi zuba k'wan a ciki,da kansa ya biyo ta d'aki ya amsa sak'on.
*Manege plss*🥰
*Taku ce*
*Yar mutan Jaoji*🙋
[2/23, 11:58 PM] LAYUZA KABIR: 👭 *FACALA* 👭
*NA*
*LAYUZA KABIR* *ADAM*
👩🏻💻👨🏻💻
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
_ALLAH KAI MANA MAGANIN DAMUWARMU_🙏🙏🙏
_*page*_*31-32*
Haka aka ci gaba da gudanar da ibadar azumin Ramadan cikin falala ta ubangiji, lokacin da azumi ya raba Su'ada ta shirya zuwa gida yi musu barka da shan ruwa,tun safe ta tafi,sai bayan sallar Isha'i Khaleelee yaje ya d'auko ta,da abinci ta taho don ba girki Zata yi ba,ai kuwa suna zuwa gida yace "Su'ada zuba min abincin nan in ci,na kasa yin bud'e baki gamsashshe duk abunda nasa a bakin sai naji ba d'and'ano,kin gama saba min da girkinki Su'ada, ban jin dad'in wani abinci bayan naki."
Cikin jin dad'in yabon da yake mata tai y'ar dariya tare da fad'in "To shi wannan d'in da za ka ci kasan wa ya dafa ne?"
Shima mirmishi yai da fad'in "Koma ya dafa in dai daga gidanku yake to d'and'anon iri d'aya ne,in Mama ce tai to zaifi ma naki dad'i,tunda gunta ki ka koya,in kuma su Jidda ne su kai to d'and'anon zai zamo d'aya tunda duk gu guda kuka koya."
Tana dariya ta zuba mai,Sannu ta dawo kusa dashi take bashi a baki,a hankali cikin kwantar da murya take mai hira "Khaleelee na,kasan me kuwa? Allah ko yau nima ban wani maida hankali wajan shan ruwa ba,sabida duk sai naji ni wani sakayau, na saba komai tare da kai,daurewa kawai nai fa,amma da kamar na kiraka nace kazo na kasa cin komai."
Kanne ido d'aya yai yana d'age mata gira sannan ya ce "Eh da kin kirani,don a dai dai lokacin nima hakanne tare dani,duk da na san ke fa harda kewan wani abu ya hanaki sakewan."
da sauri ta d'an zaro ido da fad'in
"Kai, kewan me kake so kace?"
Kauda kai yai cikin basarwa yace "Kewan wannan jikin mana,kin saba kina cin abinci ina miki abubuwa,kina mak'alemin a jiki kamar mage."
Turo baki tai tace "A'a ni dai, abunda na san zan dawo na sameshi,kuma yanzuma ka jangwalo kaci gaba da ci da kanka ni kuma in kwanta anan."
Ta fad'a tana zamewa a jikinsa.
Ci gaba yai da cin abincinsa yana k'ara tsokanarta da wai daman haka take so,ita dai bata tanka shi ba tai lamo a jikinsa.
Da k'yar Su'ada ta rok'i Khaleelee ya barta zuwa kasuwa a lokacin da salla ta rage sati guda,K'annanta taiwa siyayya duk da da taje gida ta tadda an gama sai musu komai to amma hakan ba zai hana ta kyautata musu ba,under wear's ta sai musu da kayan kwalliya,sannan ta siyawa k'aninta Khaleelee wasu takalmi masu kyau.
'Ya'yan Zakiyya kuwa da Baby ta sai musu y'an kunne da sark'a sa su Abun hannu,ta siya musu kayan kwalliya,sannan ta had'awa Baby harda jaka,sabida tana jin kullum yanda yarinyar ke nacin Sakeena ta siya Mata jaka duk 'kawayenta an sai musu,amma uwar tai mirsisi da rantsuwar ba zata siya ba,kuma fa badan bata da kud'in ba kawai siyan ne ba niyya kuma alhalin Ubansu ya bada kud'in ai musu siyayya.mutuniyarta Islam kuwa wata riga da wando masu kyau y'an kanti ta siya mata da kayan kitso dasu ribbons masu kyau kalar kayan.
Itama taiwa kanta siyayyar duk abunda take da buk'ata, sannan ta tsaya wajan y'an girki ta had'a duk wani abu da tasan za ta buk'ata da sallar nan.
Lokacin da ta dawo gida bata baiwa kowa abunsa ba,sai da dare data Nunawa mijinta sannan ta fito da na su Baby ta k'wala mata kira,da gudu yarinyar tazo da fad'in "Aunty gani."
Mik'a mata kayan tai tace "Sark'a dasu dan kunne da jaka naki ne,sauran kuma duk na Islam ne."
Ihun murna yarinyar tasa ta fita a guje ko damar godiya bata samu yi mata ba don murna.
Lokacin yaya Muktar na nan ta shiga falo da kayan tana ihun murna,ajiyewa tai a gabansa tana d'aukar jakar tace "Abba kaga Aunty Amarya ce ta siyo min jaka,Wallahi Abba kaga daman kullum sai nacewa Mamanmu ta siya min sai tak'i,gashi Aunty ta siya min,kai wallahi naji dad'i na godewa Allah na godewa Aunty Amarya,Abba sauran kayan na Islam ne."
Ganin yanda duk ta rud'e da murna yasa Abban nasu dariya yace "Kai gaskiya yau Aunty Amarya tasa Maman mamanta cikin farin ciki,To maza koma kice mata an gode don da ganin yanda kike a rude biki ma yi godiya ba."
Juyawa tai da sauri sak'ale da jakarta ta koma taiwa Su'ada godiya.
Islam ma tana murna da aka gwada mata kayan,yace kema je kicewa Aunty an gode.
Bayan fitarta ya kalli Sakeena da take d'an yak'e kadaran kadahan yace "Sakeena je kicewa Su'ada nace na gode ."
D'an tab'e baki tai tace "To godiyar me kaikuma za ka mata,ba ga yaran sun je sun yi ba,kuma nima in ta fito da safe zan mata."
Tsayawa kawai yai yana kallonta da takaici yace "Yanzu mutum yai wa 'ya'anki wannan hidimar amma ki zauna sai da safe zaki gode mata,alhalin kuna gida guda,Tashi don Allah ni ki je ki mata godiya."
Ba dan taso ba ta tashi ta fice.
A turb'une tai sallama hakan ya sa ba suji Sosai ba,ita kuma bata k'ara ba ta sako kai falon a dai dai lokacin da Su'ada ta haye kan ruwan cikin Khaleelee tana k'ok'arin k'wace wayarta da ya d'auka wai zai shiga wani group d'in ta na WathApp da yaga an sa SIRRINMU MATA, sosai su ke kokawa da juna,dariya taci k'arfin Khaleelee wanda yasa take k'ok'arin cin galaba ta k'wace wayar.
Sakeena da ke tsaye tana kallonsu wani k'ululun bak'in ciki ya turnik'eta,wato ma suna jinta su ka k'i amsawa,sabida su na wasan jakai😃🤭,juyawa tai ta bar falon,data koma tacewa Yaya Muktar ai tai mata godiyar.