← Book details Zurfin Ciki Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 18

Sashe 17

Zurfin Ciki Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Don
baya son ko kusa hankalinta yatashi, baya son
wani abu yayi musu katsalandan a cikin
daddadan zamansu, don haka ya share bai fada
mata ba.

Da dare alhaji da umma suka je, an
sasanta sannan suka taho da alkawarin cewa
gobe zata dawo dakinta.

Washegari umma ta kira
Abba tace ya share ma bishira daki yau zata
dawo, yace umma nifa gsky dabata hankalina yafi
kwanciya.

Sannan ina ta tunanin yanda zan
tunkari ummi da wannan zancen, umma ta riqe
baki tare da rafka salati, yace ynzun tsoron
ummin ka koma ne?

Yace, a'a umma kin gata
sakankance ynzun hankalinta yakwanta sai kuma
taji nazo mata da zance dawowar bishira?

Tace,
shi kenan nina fada mata.

Awaya ta kira ummi
tafada mata cewa bishira zata dawo, duk datasan
cewa matar mijinta ce dama, amma sai da
gabanta yafadi.

Umma taja mata kunne da cewa
kada taji kada tagani, abba ranar sai kusan sha
biyu zaije gurin aiki.

Don haka yace kannanshi
suje su soma fito da kayan kafin yazo sunzo sun
fada ma ummi, ita ce ta bude musu dakunan don
abba ya canza makulli bayan tafiyar bishira.

Abba
ya shigo tana zaune kan kujera sai tunani take yi
na irin zaman dazasu yi in bishira tadawo.

Yazauna tare dariko hannunta, tunanin me ki ke
yi?

Takalle shi, halin rayuwa nake tunani, yace
yanzun umma ta kira ni jiya sun je gidan su
bishira wai yau zata dawo.

Ummi ta taba baki,
Allah yakawo ta lpy.

Ya ce ni ban soba gsky.

Sbd
ke ummi tadafa kirji, sbd ni?

Ni ya abba, kada
kasa duniya ta zage ni, Tare fa nasameku?

Yace
to ni dai kada kiga kamar da son raina, tace don
Allah ya Abba kabar zancen nan.

Kaje kagyar
mata dakunanta don su kamal bazasu iya ba,
yanufi gurinsu ganin kamar ya damu yasa itama
taje tasa musu hannu don dai ya saki ranshi, sun
gyara tsaf ummi ta goge sannan ta rufe dakin.

Har magriba bishira bata ji an ce za'a maida
taba, sai ta dauki wayar kanwarta ta kira shi wai
yazo don Allah yadauketa.

Tsakanin mata da miji
sai Allah, nan ya tausaya mata yace zaizo, kafin
ya isa sai daya sai mata waya irin dai ta hannun
ummi.

Har cikin gidan ya shiga suka gaisa da
babanta, yayi murna sosai yayi tawa Abba
godiya, tare da ba shi hakuri yace yasan yanda ta
horu zai gata canza da yardar Allah.

Yasa aka
turo ta yayi mata nasiha, sannan ya gargadeta da
cewa inhar ta bari mijinta yakawa kararta zatayi
mamakin abinda zai mata.

Tace, insha Allahu
baza ta kara ba, yakawo kudi yaba Abba, da kyar
ya amsa ita kuma ya bata wasu zannuwa acikin
leda, yace su raba da abokiya zamanta.

Taje tayi
wa hajiya zainu sallama suka tafi, tamkar
baquwa haka ta koma, sai kace basu taba zaman
aure da Abba ba, nauyinsa take ji.

Suna tafe ya
ciro waya ya miqa mata, tasa hannu ta amsa
yace taki ce, tayi ta godiya yace ba komai.

Sallamarsu tasa gaban ummi faduwa, ta dake ta
fito ta amsa, wani kishi ya tasho mata amma
saita danne.

Ta kalli bishira tare dayi mata sannu
dazuwa, ta amsa tana kallon ummi tayi kyau
tagoge daga ka ganta kaga wayayya 'yar gatan
miji.

Ta dauko makullin dakin ta ba bishira, abba
kuma ya nufi dakin ummi.

Bishira ta dinga kallon
yanda abba ya gyara gidan yaja gini ta gefen
ummi yayi mata falo da kicin, sannan tsakar
gidan an gyare shi da tiles.

Haka bandakin su
yagyara shi, nan dai bishira ta shiga dakinta ta
zauna bakin gado tana yi wa allah godiya tare
dayi wa kanta alkawarin har abada bazata ta
kara yin yaji ko ta janyo abinda zaisa mijinta ya
sake ta ba.

Ummi tana kan gado tana karanta
wani littafi yazo ya zauna bakin gadon bata ko
kalle shi ba don haushi take ji.

Sai take ganin
kamar rawar kai yake yi da dawowar bishiran,
kuma tuntuni yana zuwa gurin ta ya boye mata.

Yace madam ina son in yi magana da ku ne ke da
bishira, ummi tace ina jin ka, yace can zaki zo
muje.

Tace, gsky nagaji, kayi maganar da safe.

Yagama gano kishi ne ke damunta, don haka yayi
murmushi yace yanda kikace hakan za'ayi.

Ya
fita kamar minti 30 yasake shigowa ya aje mata
leda tare da cewa saida safe aciki tace Allah
yabamu alheri.

Yana tafiya taje ta banko kofarta,
yau kam bacci ya qi idanun ummi sbd tayi sabon
bacci a haqarqarin Abba.

Dukkan filolinta ta rasa
wanda zai maye mata madadin haqarqarin
mijinta, ynzun yancan da wata tasan yanda yake
wannan rawar jikin ynzun ya manta da batunta.

Tarasa me yake mata dadi, littafin datake
karantawa kuwa sam bata fahimtar abinda ke
ciki.

Hka ta dinga zubda hawaye har nisan dare,
ganin bata da wata mafita, tashi tayi ta bude kofa
lokacin 2 saura taje tayo alwala tazo ta kama
nafila.

Abba jin bude kofarta ne yasa shi leqowa
ta window aranshi yaji tausayinta don yasan bata
iya bacci sai ajikinshi, ita bata san ya leqo ba
don ko hanyar dakin bata ishe ta kallo ba.

Yakalli
bishira wadda bacci yayi gaba da ita ya tausaya
mata sosai yanda tayi tarawar jiki alokacin
auratayyarsu dazun.

Yadauko wayarshi yarubuta
ma ummi sako.

KI KWANTA KIYI BACCI BABY,
TARE DA QISIMA CEWA KINA LAFE
AMAKWANCINKI (WATO JIKINA) INA CIKE DA
KEWAR LEBUNANKI.

Tana sallah taji shigowar
saqo amma bata yi ko marmarin dubawa ba, haka
tai sallah har zuwa lokacin da bacci yasoma
fizgarta.

Tayi adduo'o'i sannan ta kwanta, saida
asubahi ne datayi sallah sannan ta karanta, dan
tsaki taja tare da cewa, Karya kawai, kishi yasa
ta fadin haka don tasan Abba sosai baya boye
mata komai ynzun.

Sai dai abinda yasake qular
da ita da asubahin nan yanda tana fita shi kuma
ya fito wanka, duk da tasan dole wani abu yafaru
tsakaninshi damatarsa, amma sai taga tamkar da
gayya ya tsaya don tafito taganshi.

Tna idar da
sallah ta dora ruwa akicin dinta, tadafa ruwan tea
taje kicin din bishira tadauko flask tazo ta wanke
ta zuba musu ruwan zafi taje kofar bishira tayi
sallama bishiran ce ta bude ummi tamiqa mata
tare da cewa an tashi lpy?

Cikin sakin fuska tace,
lpy lau, nagode.

Ummi ta ce ba komai takoma
dakinta ta kulle kofarta don yau bata da darasin
safe.

Abba ma yau bada wuri zai fita ba, don
haka yadan samu baccin safe sai 8 yayi wanka
ya karya, sannan yanufi dakin ummi.

Kofarta tana
rufe, ya kwankwasa ta share sai can dai dataji
yaqi tafiya sannan tazo tabude.

Takalle shiya yi
kyau cikin kananan kaya, ta kauda kai tare da
cewa, an tashi lpy?

Yace lpy lau, kin karya?

Tace,
um'um sai anjima, zata rufe kofar yace,
makaranta fa?

Tace sai karfe 2 nake da darasi.

Ta maida kofar ta rufe, yayi dan murmushin
takaici sannan yafita.

Kwananshi 2 dakin bishira
yayi niyyar dawowa dakin ummi, don ya kosa
yadawo ya lallasheta bazai iya daukar wannan
shariyar da take mishiba.

Tsakaninta da bishira
lpy lau amma shi sai tana wani share shi. part 33 the end
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:45
Ya shigo da zumudi zai nufi dakinta, tamiqe cikin
fara'a daga wanke-wanken da take yi ta amshi
ledar hannunsa da jakar laptop ta nufi dakin
bishira.

Shida bishira suka bita da kallo, ganin
zata shiga bishira tace ummi yau ai dakinki yake.

Ummi tace injiwa?

Anty bishara ai kullum ke ce
dashi har sai kin rama duk kwanakin da kika
dauka agida.

Kinga kenan kusan wata goma sha
daya kenan.

Abba cikin sauri yace ke
mahaukaciya ce?

Ina ki kasamo wannan fatawar?

Ta kalle shi, sannan tashiga dakin ta ajiye ta fito
taqara kallonshi gurin malamai, yace to ban
yarda ba, don haka zanci gaba dayi muku kwana
bibbiyunku, ummi tace to ni na yafe mata nawa
kwanakin bishira tace nagode ummi.

Haushi ya
cika Abba, amma shi bazai dauki wannan horon
da ummi take shirin yi masa ba.

Yadawo dakin
bishira a fili yafurta kema saina baki haushi zakiyi
dakin sanin wannan furucin.

Sharewa yayi yaci
gaba da kwana dakin bishira tare da nuna kulawa
ga bishiran.

Ummi ta jure duk da duk daren Allah
sai taci kuka ta gode Allah, sannan tashiga zargin
cewa shi ma ya Abban dama can yana son
tarewa dakin bishira, inba haka bame zaisa yayi
saurin yarda kuma yayi ta nuna mata soyayya?

Ganin ummi tana yi tamkar bata damu ba yasa
shi qa rajin haushi, yadawo da yamma suna
zaune kowa A qofarshi.

Ummi tayi kwalliya cikin
qananan kaya, bishira kuma tana sanye da leshi,
karatun littafi bishiran keyi ita kuma ummi tana
yin gyaran qumbunanta.

Bawai suna wata hira
bane amma suna kula juna sosai musamman
bishira tana son su saba da ummi.

Ummin ce
bata cika son fitowa ba, bishira ta tashi ta masa
sannu dazuwa tare da amsar kayan hannunsa
don yanzun tana koyi da ummi gurin kyautatawa,
ummi ta kalle shi sannu dazuwa, ya amsa da
yauwa baby.

Yakalli bishira sweety zanyi wanka,
tace to, takai masa ruwa yashiga dakinta, sai
tazo tace masa takai nan kuma yajanyo bishira
jikinshi.

Ba wai yana da bukata bane, amma don
ya shaqar da ummi sai ya banko kofar, qaran
kofar ne yasa ummi kallon gurin dakin.

Ta duqar
dakai taci gaba da abinda take yi, kusan minti
arba'in suka fito, Abba ya matsawa bishira wai
suyi wanka tare, tace ni bazan iya ba akwai ummi
dama da dare ne inajin kunya.

Kuma kada taga
kamar cin fuska ne, yace kenan don kada ki bata
mata rai ni mijinki bazaki faranta min ba ko?

Dole
ta bishi suka shiga bayi.

Baqin ciki yasa ummi
tashi tashige daki, kuka sosai tayi daga nan bata
fito ba sai magriba, tanayin alwala tarufo kofa,
washegari ma qin bude qofar tayi daga alwalar
asubahi.

Abba yayi ta raba ido ya ganta amma
bata fito ba, yasan fushi take, ya kira wayarta
taqi dagowa yayi mata saqo cewa in zata
makaranta tafito inkuma sai darana ta bude ta
amshi kudin mota.
Chapter 17 · 0% Book details