Sashe 16
Zurfin Ciki Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
To kafin yadawo ma saiga
hajiya zainu da direba tazo gidan su umma tadire
musu 'yar, sannan tashiga gidan umman bashir
tace, in kin haifi danki na halas ne ba shege ba to
kisa shi ya aiko wa 'yata saki.
Umman tace zoko
kiga dan halas ne in yaso kuje ku nemi arne mara
sallah dan uwanta kazami kubashi.
Nan fa zage-
zage ya tashi har su umma dasauran makota
suka shigo.
Dakyar aka tura hajiya ta tafi, tace
kuma saita kira 'yan sanda anzo antafi da umman
bashir.
Alhji qarami ma cewa yayi maza abba
Abba yarubuta takarda ya aika ma bishira.ZURFIN CIKI book 4 part 32
ZURFIN CIKI book 4 part 32
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:37
Shiko alhji babba da umma suka ce a'a abari
qura ta lafa sannan aje.
Koda aka kwana 2 abba
kin bin alhaji yayi sai wani abokinshi alhaji
yasamu suka tafi tare.
Mahaifin bishira yaji
mamaki cewa ba sakinta abba yayi ba.
Kuma bai
san sun maida 'ya ba, tadai ce mishi kunzo kun
amshi 'yarku, to yanzun tunda haka ne kunga
kenan bishira da uwarta basa son takoma gidan
mijinta ko?
Su alhaji suka ce eh, yace to ku sa
shi ya rubuto takardarta ku kawo min, su alhaji
sukace ba za'ayi haka ba.
Yace, to kuje ku barta
zata gane gidan ubanta bananne yadace tazauna
ba.
Sukai godiya suka tafi.
Harta koma gidan
anty farida mahaifinsu yace tadawo nan gidanshi
badashi take takama ba?
Wato ta kashe auranta
zata je ta kashe na yarta dole ta dawo, tsohuwar
dake musu aiki yace ta koma gida tahuta amma
duk wata tazo ta amshi albashinta.
Sannan yace
bishira itace zata dinga wannan aikin duka ita
kadai, lamarin yayi wa bishira tsauri da yawa,
gashi ba fita duk ta rame ta lalace ga tunanin
'yarta.
Muhibba kuwa tana gurin umma, ummi
ma takan daukota sannan ummi tasamu nasarar
rufe bakin umman bashir, ta hanyar yi mata
kyautuka ko me sukace sai ta aika mata.
Tasa
Abba ya canja mata gado don nata ya lallace,
sannan da fati ta haihu tasa Abba ya sai mata
garar abinci, ita kuma tasa zani da rigunan yara.
Nan fa sai ga sahura babu ko kunya tana shima
ummi albarka, ko bashir ne yakawo gulmarsu
ummi sai tace ai ita bata yo halin uwarta ba.
Tafi-tafi ma in ya kawo sai tace ai su umma da
ummi sun gane kuransu.
Haba sahura kodai ki
gane kuranki?
Abba yasoma damun ummi da
batun ciki, wai shifa yana tsoro kada su gaji su
umma, ummi tace su dai yi addu'a sunje asibiti
ba wata matsala, likita yace in rabonsu yazo zasu
haihu.
Da kyar ummi ta shawo kan Abba ya
amince ta zana (JAMB) don ci gaba da karatu,
sannan ta shiga islamiya.
Abba yayi kyau yayi
kiba ya kara gogewa, haka nan ummi duk wanda
yaganta saita birge shi, daka ganta kaga wayayya
wadda mijinta yasan da ita.
Taci nasarar samun
(POLY) saboda bata samu abinda take so don
zuwa (UNIVERSITY) ba, sai dai ba tasha dokoki
kafin ta fara zuwa.
Bayason kawaye baya son
abokai, irin wanda wasu matan keyi sannan
yadinka mata manyan hijabai, kuma banda hawa
acaba, inya samu sarari zai dinga zuwa da kansa
yana daukarta.
Sai kuma gargadi na karshe kuma
da babbar murya, in har ya daina samun kular
datake bashi ta kowane fanni wai saboda karatu,
to kuwa za adaina karatun gaba daya.
Tace,
insha Allah sai abinda yai gaba.
Ya canja mota,
umma tayi ta fada wai tafi son yasai fili yayi dan
gidanshi irin na zamani yace za'azo gurin
ahankali kada ki damu umma.
Bishira ta sulale ta
tafi na'ibawa gidan anty da kukanta wiwi don
Allah ta taimaka mata taba Abba hakuri ya maida
ta, wlh tagane kuskurenta.
Anty tace, nifa bazan
iya kiran Abba ba don kin riga kin bmu kunya, sai
dai in ke ce zaki kira shi ga waya can.
Ta dauko
ta kira, shikuma ganin kiran anty sai yayi parking
yadauko ummi daga makaranta, ya daga sai yaji
muryar bishira.
Cikin kuka tana cewa, don Allah
abba nice, kayi hakuri indawo dakina, wallh zan
canza, yace ok baki riga kin canza din ba, to bari
inkin canza din sai muyi magana.
Yakashe haka
tayi ta kuka tagama anty tabata wasu kayan
sawanta sannan ta tafi.
In lokacin labarai yayi
haka take zuwa ta tasa TV tayi ta kallonshi tana
kuka, kullum kara sonshi take gashi yayi kyau
idanunshi sun qara haske.
Wata ranar jumma'a
wuraran karfe sha daya ta saci jiki tanufi gurin
aikin Abba, yana fitowa dakin daukar labarai
akace wata tana nemanshi.
Baiji wani mamaki ba
don mata kanzo neman shi wasu suce suna
sonshi wasu suce ganinshi kurum zasuyi don
yana birge su.
Yana zuwa sai yaga bishira, nan
take ya daure fuska tamkar bai taba dariya ba,
duk da cewa acan kasan zuciyarshi yatausaya
mata.
Ta tsugunna gwuiwa 2 tana rokonsa, yace
ke tashi kada ki janyo min mutane, jeki zanzo.
Koda ta tafi cikin murna shi ko harkokinsa
yakama.
Shiru-shiru tana saka rai bashi ba
alamarsa.
Nan kuma tashiga daukar waya
kannanta tana kiranshi, harma yadaina dagawa.
Wataran taje tasamu ahmad tana kuka, ahmad
yace taje zai ganshi.
Rannan kuwa har gida
ahmad yiyi sallama da abba yashiga rokon Abba
ya maidota.
Abba yace taje taroqi mahaifiyarsa
dasu umma insun yarda shikenan.
Har gida
ahmad yaje ya fada mata, bata yi sanyi ba tanufi
gurin umman bashir.
Umman tana zaune da
'ya'yanta suna shan farfesun kifin da ummi ta
aiko musu dashi, tana ganin bishira ta hade rai.
Tace, lapiya?
Bishira tace lpy lau umma zuwa
nayi in roqi gafararki.
Tace nime kika min?
Tace
don Allah dai ki yafe ni, ina son indawo dakina
Abba yace sai kin hakura, tace oho, yanzun kin
yarda ina da kima agurinsa?
To bari kiji bazaki
dawo ba, mai baqar rowa kince nimai kwadayi ke
kuma mai rowa ko?
To kin gani wannan ummi ce
ta dafo mana ta nuna mata kular kifi, sanda
kinanan bana cin komai bansan dana yana samu
ko baya samu ba.
Yanzun abin arziki iri-iri
kidawo ki toshemana kofar samu?
Tace, wlh
bazan toshe ba, umman bashir tace dukda haka
dai bazaki dawo ba.
Tayi takuka sannan tafita,
har zata wuce gidan su ummanshi sai ta tuna
kada suyi mata dariya sai tace baridai ta shiga.
Kyakkyawar karba umma tayi mata suka gaisa,
tazauna umma ta kawo mata ruwa ta amsa
tasha.
Muhibba tana ta tsalle tsallenta kan kujera
zuwa jikin umma, umma tace ji hibba ki gaida
mamanki, ga mamakin bishira sai yarinyar ta
kalleta tace.
Umma niba wannan bace ba
momina, momina sun tafi da babana zaya kaita
makaranta.
Umma tace, wannan ma ummarki ce
yarinyar taruga dakin tsohuwa tana cewa, ita ba
ummarta bace.
Bishira ta bita dakallo, yarinyar
tayi bulbul gata cikin shiga mai kyau da tsafta
kanta yaji kitso da 'yan duwatsu.
Saita soma
kuka tana fadin mahaifiyata ta cuce ni, umma
tace a'a kece kika cuci kanki, inbaki dauki
damuwarki kin kai mata ba yaushe zatasan anyi?
To ynzun dai dubi 'yarki tana gudunki sbd bata
sanki ba, ina amfanin wannan?
Tsohuwa tace
kukan wanikeji ta shigo tana kallon bishira cikin
mamaki tace.
'yar nan kece haka?
Ciwo kikayi ko
ko duniya ce ta juya miki baya?
Kai jama'a dubi
yanda kika kare kikayi bikinkirin.
Ita da tadukar
dakai tare da cewa bnyi ciwo ba nidai nazo ku
yafe ni, sannan ku roqa min abba ya yafe min in
dawo dakina.
Yace, bazan dawo ba har sai kun
yafe min, amma naje gurin umman bashir ta kore
ni tace bazata bari in dawo ba.
Kuma gidanmu
wuya nake sha, kusan rabin aikin gidan nikeyi ga
qannaina duk sun raina ni.
Umma tace, yi shiru
share hawayenki bari zaki koma.
Tsohuwa tace,
ke dai kin cika sa kai a uku suwaiba, gashi abin
kirki bai karbe kiba.
Kina yi ana zaginki ana zagin
'yarki, bishira ta ce wlh duk na daina, yanzu na
gane kune masu sona, umma tace ba komai.
Tadaga waya ta kira alhaji ta fada masa komai
yace to yana zuwa donshi ya qosa asulhunta
yarinyar ta koma dakinta saboda darajar
tsohonta.
Yana zuwa yaji komai nan ya daga
waya yakira Abba, yace yana zuwa yana hanya
ne yace to ya same su gida.
Abba yana shigowa
ganin bishira yahade rai ya zauna nan dai alhaji
ya hada su yayi musu fada da nasiha, sannan
yace baya son abba yace komai komai kuma ko
sun koma gida banda tashin tashina.
Bishira tayi
ta godiya alhaji babba yace su tashi ashiga gurin
umman bashir din tana ganinsu tahau cewa alhaji
dakanka?
Maimakon ace in zo?
Umma tace, a'a
keda zamu zo baki hakuri ai mu ya dace mu
shigo.
Nai dai alhaji yayi bata hakuri tace taci
albarkacinta na hakura, amma da sharadi inta
sake maimaita halin da tayi abaya ko taje ta
takurawa ummi tofa saita tabar gidan.
Bishira
cikin kuka tace ta daina insha Allahu, nan itama
umman bashir din tace dasu umma su yafe mata
sharrin shaidan ne da qaryar barayin imani wato
bokaye da 'yan tsibbu suka ce ba komai.
Nan
alhaji yace da abba yakai bishira gida, ba don son
ranshi ba yadauke tazuwa gida, sam bata damu
da daure fuskarshi ba, dadi da murna fal ranta.
Yana sauke tazai wuce tace, don Allah ka yafe
min sannan ka gaida min ummi, yace zataji.
Tace
to yaushe zan dawo?
Yace, duk lokacin dasu
alhaji suka zo gurin dadynku.
Nan yatafi, ita
kuma ta shiga gida, hajiya zainu ta tsareta wai
sai ta fadi inda taje, tunda ta kira anty tace, bata
can.
Bishira tace naje ba mijina da surukaina
hakuri ne, hajiya zainu tace ni dazai maida ki ai
sai nafi kowa murna.
Na gaji da zamanki da
qazantarki, tunda babanku yaqi ki koma
makaranta yakashe miki kudi ki goge ko kya
samu mai kudin dazai aure ki, to gara kin koma
can kin qarata.
Abba kam shi tunaninshi ta ina
zai soma sanar da ummi dawowar bishira?
hajiya zainu da direba tazo gidan su umma tadire
musu 'yar, sannan tashiga gidan umman bashir
tace, in kin haifi danki na halas ne ba shege ba to
kisa shi ya aiko wa 'yata saki.
Umman tace zoko
kiga dan halas ne in yaso kuje ku nemi arne mara
sallah dan uwanta kazami kubashi.
Nan fa zage-
zage ya tashi har su umma dasauran makota
suka shigo.
Dakyar aka tura hajiya ta tafi, tace
kuma saita kira 'yan sanda anzo antafi da umman
bashir.
Alhji qarami ma cewa yayi maza abba
Abba yarubuta takarda ya aika ma bishira.ZURFIN CIKI book 4 part 32
ZURFIN CIKI book 4 part 32
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:37
Shiko alhji babba da umma suka ce a'a abari
qura ta lafa sannan aje.
Koda aka kwana 2 abba
kin bin alhaji yayi sai wani abokinshi alhaji
yasamu suka tafi tare.
Mahaifin bishira yaji
mamaki cewa ba sakinta abba yayi ba.
Kuma bai
san sun maida 'ya ba, tadai ce mishi kunzo kun
amshi 'yarku, to yanzun tunda haka ne kunga
kenan bishira da uwarta basa son takoma gidan
mijinta ko?
Su alhaji suka ce eh, yace to ku sa
shi ya rubuto takardarta ku kawo min, su alhaji
sukace ba za'ayi haka ba.
Yace, to kuje ku barta
zata gane gidan ubanta bananne yadace tazauna
ba.
Sukai godiya suka tafi.
Harta koma gidan
anty farida mahaifinsu yace tadawo nan gidanshi
badashi take takama ba?
Wato ta kashe auranta
zata je ta kashe na yarta dole ta dawo, tsohuwar
dake musu aiki yace ta koma gida tahuta amma
duk wata tazo ta amshi albashinta.
Sannan yace
bishira itace zata dinga wannan aikin duka ita
kadai, lamarin yayi wa bishira tsauri da yawa,
gashi ba fita duk ta rame ta lalace ga tunanin
'yarta.
Muhibba kuwa tana gurin umma, ummi
ma takan daukota sannan ummi tasamu nasarar
rufe bakin umman bashir, ta hanyar yi mata
kyautuka ko me sukace sai ta aika mata.
Tasa
Abba ya canja mata gado don nata ya lallace,
sannan da fati ta haihu tasa Abba ya sai mata
garar abinci, ita kuma tasa zani da rigunan yara.
Nan fa sai ga sahura babu ko kunya tana shima
ummi albarka, ko bashir ne yakawo gulmarsu
ummi sai tace ai ita bata yo halin uwarta ba.
Tafi-tafi ma in ya kawo sai tace ai su umma da
ummi sun gane kuransu.
Haba sahura kodai ki
gane kuranki?
Abba yasoma damun ummi da
batun ciki, wai shifa yana tsoro kada su gaji su
umma, ummi tace su dai yi addu'a sunje asibiti
ba wata matsala, likita yace in rabonsu yazo zasu
haihu.
Da kyar ummi ta shawo kan Abba ya
amince ta zana (JAMB) don ci gaba da karatu,
sannan ta shiga islamiya.
Abba yayi kyau yayi
kiba ya kara gogewa, haka nan ummi duk wanda
yaganta saita birge shi, daka ganta kaga wayayya
wadda mijinta yasan da ita.
Taci nasarar samun
(POLY) saboda bata samu abinda take so don
zuwa (UNIVERSITY) ba, sai dai ba tasha dokoki
kafin ta fara zuwa.
Bayason kawaye baya son
abokai, irin wanda wasu matan keyi sannan
yadinka mata manyan hijabai, kuma banda hawa
acaba, inya samu sarari zai dinga zuwa da kansa
yana daukarta.
Sai kuma gargadi na karshe kuma
da babbar murya, in har ya daina samun kular
datake bashi ta kowane fanni wai saboda karatu,
to kuwa za adaina karatun gaba daya.
Tace,
insha Allah sai abinda yai gaba.
Ya canja mota,
umma tayi ta fada wai tafi son yasai fili yayi dan
gidanshi irin na zamani yace za'azo gurin
ahankali kada ki damu umma.
Bishira ta sulale ta
tafi na'ibawa gidan anty da kukanta wiwi don
Allah ta taimaka mata taba Abba hakuri ya maida
ta, wlh tagane kuskurenta.
Anty tace, nifa bazan
iya kiran Abba ba don kin riga kin bmu kunya, sai
dai in ke ce zaki kira shi ga waya can.
Ta dauko
ta kira, shikuma ganin kiran anty sai yayi parking
yadauko ummi daga makaranta, ya daga sai yaji
muryar bishira.
Cikin kuka tana cewa, don Allah
abba nice, kayi hakuri indawo dakina, wallh zan
canza, yace ok baki riga kin canza din ba, to bari
inkin canza din sai muyi magana.
Yakashe haka
tayi ta kuka tagama anty tabata wasu kayan
sawanta sannan ta tafi.
In lokacin labarai yayi
haka take zuwa ta tasa TV tayi ta kallonshi tana
kuka, kullum kara sonshi take gashi yayi kyau
idanunshi sun qara haske.
Wata ranar jumma'a
wuraran karfe sha daya ta saci jiki tanufi gurin
aikin Abba, yana fitowa dakin daukar labarai
akace wata tana nemanshi.
Baiji wani mamaki ba
don mata kanzo neman shi wasu suce suna
sonshi wasu suce ganinshi kurum zasuyi don
yana birge su.
Yana zuwa sai yaga bishira, nan
take ya daure fuska tamkar bai taba dariya ba,
duk da cewa acan kasan zuciyarshi yatausaya
mata.
Ta tsugunna gwuiwa 2 tana rokonsa, yace
ke tashi kada ki janyo min mutane, jeki zanzo.
Koda ta tafi cikin murna shi ko harkokinsa
yakama.
Shiru-shiru tana saka rai bashi ba
alamarsa.
Nan kuma tashiga daukar waya
kannanta tana kiranshi, harma yadaina dagawa.
Wataran taje tasamu ahmad tana kuka, ahmad
yace taje zai ganshi.
Rannan kuwa har gida
ahmad yiyi sallama da abba yashiga rokon Abba
ya maidota.
Abba yace taje taroqi mahaifiyarsa
dasu umma insun yarda shikenan.
Har gida
ahmad yaje ya fada mata, bata yi sanyi ba tanufi
gurin umman bashir.
Umman tana zaune da
'ya'yanta suna shan farfesun kifin da ummi ta
aiko musu dashi, tana ganin bishira ta hade rai.
Tace, lapiya?
Bishira tace lpy lau umma zuwa
nayi in roqi gafararki.
Tace nime kika min?
Tace
don Allah dai ki yafe ni, ina son indawo dakina
Abba yace sai kin hakura, tace oho, yanzun kin
yarda ina da kima agurinsa?
To bari kiji bazaki
dawo ba, mai baqar rowa kince nimai kwadayi ke
kuma mai rowa ko?
To kin gani wannan ummi ce
ta dafo mana ta nuna mata kular kifi, sanda
kinanan bana cin komai bansan dana yana samu
ko baya samu ba.
Yanzun abin arziki iri-iri
kidawo ki toshemana kofar samu?
Tace, wlh
bazan toshe ba, umman bashir tace dukda haka
dai bazaki dawo ba.
Tayi takuka sannan tafita,
har zata wuce gidan su ummanshi sai ta tuna
kada suyi mata dariya sai tace baridai ta shiga.
Kyakkyawar karba umma tayi mata suka gaisa,
tazauna umma ta kawo mata ruwa ta amsa
tasha.
Muhibba tana ta tsalle tsallenta kan kujera
zuwa jikin umma, umma tace ji hibba ki gaida
mamanki, ga mamakin bishira sai yarinyar ta
kalleta tace.
Umma niba wannan bace ba
momina, momina sun tafi da babana zaya kaita
makaranta.
Umma tace, wannan ma ummarki ce
yarinyar taruga dakin tsohuwa tana cewa, ita ba
ummarta bace.
Bishira ta bita dakallo, yarinyar
tayi bulbul gata cikin shiga mai kyau da tsafta
kanta yaji kitso da 'yan duwatsu.
Saita soma
kuka tana fadin mahaifiyata ta cuce ni, umma
tace a'a kece kika cuci kanki, inbaki dauki
damuwarki kin kai mata ba yaushe zatasan anyi?
To ynzun dai dubi 'yarki tana gudunki sbd bata
sanki ba, ina amfanin wannan?
Tsohuwa tace
kukan wanikeji ta shigo tana kallon bishira cikin
mamaki tace.
'yar nan kece haka?
Ciwo kikayi ko
ko duniya ce ta juya miki baya?
Kai jama'a dubi
yanda kika kare kikayi bikinkirin.
Ita da tadukar
dakai tare da cewa bnyi ciwo ba nidai nazo ku
yafe ni, sannan ku roqa min abba ya yafe min in
dawo dakina.
Yace, bazan dawo ba har sai kun
yafe min, amma naje gurin umman bashir ta kore
ni tace bazata bari in dawo ba.
Kuma gidanmu
wuya nake sha, kusan rabin aikin gidan nikeyi ga
qannaina duk sun raina ni.
Umma tace, yi shiru
share hawayenki bari zaki koma.
Tsohuwa tace,
ke dai kin cika sa kai a uku suwaiba, gashi abin
kirki bai karbe kiba.
Kina yi ana zaginki ana zagin
'yarki, bishira ta ce wlh duk na daina, yanzu na
gane kune masu sona, umma tace ba komai.
Tadaga waya ta kira alhaji ta fada masa komai
yace to yana zuwa donshi ya qosa asulhunta
yarinyar ta koma dakinta saboda darajar
tsohonta.
Yana zuwa yaji komai nan ya daga
waya yakira Abba, yace yana zuwa yana hanya
ne yace to ya same su gida.
Abba yana shigowa
ganin bishira yahade rai ya zauna nan dai alhaji
ya hada su yayi musu fada da nasiha, sannan
yace baya son abba yace komai komai kuma ko
sun koma gida banda tashin tashina.
Bishira tayi
ta godiya alhaji babba yace su tashi ashiga gurin
umman bashir din tana ganinsu tahau cewa alhaji
dakanka?
Maimakon ace in zo?
Umma tace, a'a
keda zamu zo baki hakuri ai mu ya dace mu
shigo.
Nai dai alhaji yayi bata hakuri tace taci
albarkacinta na hakura, amma da sharadi inta
sake maimaita halin da tayi abaya ko taje ta
takurawa ummi tofa saita tabar gidan.
Bishira
cikin kuka tace ta daina insha Allahu, nan itama
umman bashir din tace dasu umma su yafe mata
sharrin shaidan ne da qaryar barayin imani wato
bokaye da 'yan tsibbu suka ce ba komai.
Nan
alhaji yace da abba yakai bishira gida, ba don son
ranshi ba yadauke tazuwa gida, sam bata damu
da daure fuskarshi ba, dadi da murna fal ranta.
Yana sauke tazai wuce tace, don Allah ka yafe
min sannan ka gaida min ummi, yace zataji.
Tace
to yaushe zan dawo?
Yace, duk lokacin dasu
alhaji suka zo gurin dadynku.
Nan yatafi, ita
kuma ta shiga gida, hajiya zainu ta tsareta wai
sai ta fadi inda taje, tunda ta kira anty tace, bata
can.
Bishira tace naje ba mijina da surukaina
hakuri ne, hajiya zainu tace ni dazai maida ki ai
sai nafi kowa murna.
Na gaji da zamanki da
qazantarki, tunda babanku yaqi ki koma
makaranta yakashe miki kudi ki goge ko kya
samu mai kudin dazai aure ki, to gara kin koma
can kin qarata.
Abba kam shi tunaninshi ta ina
zai soma sanar da ummi dawowar bishira?