← Book details Zurfin Ciki Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 18

Sashe 13

Zurfin Ciki Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wayar umma ce a hannunshi yana
ta danne danne, ba don nishadi ba don kawai ya
rasa me zaiyi.

Dript ya shiga yana ta bin abinda
ke ciki, mamaki ya cikashi lokacin da yaga irin
text din da ummi tasha rubuta mashi don ta tura
ma abba, sai kuma ta fasa.

Tamkar cikin mafarki
abba ya rika karanta sakwanin dama ummi tana
sonshi zurfin ciki ne tayi?

Ya sake bude wani
rubutu cewa, Ya Abba ina sonka, ina kaunarka
duk wani motsi na numfashina kara sonka nake,
ka tausaya mun sonka zai zama ajalina, duk
ciwon da nakeyi na sonka ne.

Ko na rantse ba
zanyi kaffara ba, in kaji haushin kalamaina ka
yafeni, nasan ni ba ajinka bace, amman ka daure
kace kana sona koda bada gaske bane.

Gama
karanta sakon yayi dai dai da dawowa da ummi
dakin, da sauri suka nufeta idonta biyu saidai
daga gani tasha azaba.

Tayi wujiga wujiga.

Abba
ya kama hannunta cikin matsanancin sonta da
tausayi.

Sannu suka dinga yimata, nurse tabasu
magungunan da za'a rika bata, umma kuma ta
dauki wayarta don sanar da alhaji an gama aikin.

Abba yasa bakinshi dai dai kunnenta yace ina
sonki ummi, ina matukar sonki.

Duk da tana cikin
wani hali taji kalaman nasa har a tafin kafarta.

Ta bude jajayen idonta ta dubeshi, ya sakale
hannunshi cikin tafin hannunta ya hade su.

Ta
girgiza kai dai dai lokacin da nurse din ta sake
shigowa tace ga kayanta, ya amsa zaninta ne da
siket da sauransu.

Tace ka barta tayi bacci kafin
ta tashi zafin gurin ya ragu, kila zuwa dare a
sallame ku.

Umma tace to mungode.

Nurse tace
yarinyarki nada dauriya, anyi mata allurar kashe
zafi bata kama jikinta ba amman bata yimuna ihu
ba.

Likita ma ya yabata da kokarie ta, Abba ya
kalli ummi cikin tausayi.

Sai gurin karfe ukku ta
farka wurin kam ya dan lafa da radadin, abba ne
yaje gida ya dafo masu abinci sannan ya nufi
wurin aikin shi.

Don ranar bada wuri zashi ba.

Tunda ummi ta farka take ta kokarie tunowa shin
kalaman da taji cikin mafarki ne ko kuwa ido biyu
ne?

Bakwai na dare likita ya shigo ya kara duba
ummi sannan yace suna iya tafia gida.

Ya basu
maganin sha sannan yace ta rika shiga ruwan
zafi da dettol.

Umma ta kira abba ta fada masu
batun sallama.

Yace su jirashi yana zuwa.

Ummi
tace da ummansu su alhaji pha?

Tace sunxo kina
bacci harda ummanku sahura.els / ZURFIN CIKI book 4 part 28
ZURFIN CIKI book 4 part 28
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:30
Bansan lokacin dana dauka ina rigimniya da sonki
danqare a zuciyata.Ummi da ban sameki ba da
tuni bana garin Kano domin lokacin yanke
shawara nayi in nemi canjin aiki zuwa wata jihar
har yau ban daina yiwa Salisu addua ba wanda
shine mutum na farko da ya soma tsegunta min
kin zama mata gareni So, Ummi baya raina
abinda yake so da nayi zaton zubar da kima ne in
furta maki kalmar so musammam in na tuna ke
baki soma, zurfin a so bashida wani amfani don
na sha wahala.Ba zan Qara boye dimbin son da
nike maki ba Ummi ko gaban wa zan nuna kina
jina matsala?

Ummi wadda ke zaton mafarki take
sai taji bakinta yana furta wayyo dadi Ya Allah
kada ka farkar dani in har bacci nike Abba yace
ciji yatsanki zakiji zafi Ummi nine Abban ki mai
sonki wanda ya reneki tun kina zanen gobe.

Hawaye suka soma zubo mata cikin muryar kuka
tace Ya Abba da gaske kana sona?

Nafi zaton
tausayina yasa ka furta haka, Amma koba gaske
ba ne na gode kuma naji dadi Amma ka sani Ya
Abba ina sonka mai tsanani sai tasa kuka.

Yace
ummi yi shiru, in kukan takaici ne kukan ya kare.

Nima na jima ina sonki jiya naga sakonki a wayar
umma da kike rubutawa mai dauke da nuna sonki
gareni.

Sai zurfin ciki ya hanaki, don allah ummi
kada ki koma zurfin ciki a sona, ki zazzage min
duk irin sonki gareni.

Ummi tace yau kam ji nake
kamar a mafarki.

Sun nutsa a cikin hirar so suna
ta baiwa juna labarin halin da suke shiga a baya,
a lokacin daya ganta da wani namiji yace
hankalinsa yayi mugun tashi.

Sai lokacin daya
fuskanci bashir na sonta, ita kuma Tace ta tsani
koh mace ta kira layin shi, zainab kuwa data
samu labarin ta kamar ta mutu.

Tace ko bishira
bata kishi kamar yarda take kishin zainab, sunyi
nisa basu san sun kwana zance ba, sai da ummi
taji kiran sallah.

Tace ya abba kaji abunda naji,
yace sallah ake kira naji, kin sani kwana zance.

Ban gaji dajin muryarki ba amarya tah.

Ummi
tace gari yayi saurin wayewa kaje kayi muna
godia ga allah ta hanyar nafita, yace to matata.

Hamdala ta rikayi har bacci ya dauketa, muryar
umma taji tana cewa ummi ki tashi kiyi wanka ki
gasa jikinki.

Tana zaune cikin baho wanda umma
ta zuba ruwan dimi da dettol, tsohuwa ta shigo
cikin bandakin.

Ummi tace don allah tsohuwa fita,
tace don allah ja can anki a fita din, ta saka
hannu cikin ruwan wankan ummi dake gefe a
bokiti.

Tace ina suwaiba?

Ai karo mata ruwan
zafi, wannan ruwa yaushe zata gasa jikinta, idan
da dan tawul dauko in danna mata jikin.

Ummi
tace nidai tsohuwa ki barshi don allah, sai kace
wata mai jego?

Tsohuwa tace tafi can kuda baku
san darajar jikinku ba.

Wannan rawar kan da mai
sunan malam keyi idan ba'a gyara kiba saiki ba
sai zance ya dawo baya, idan anyi magana ku
yan zamani kuce bamu waye ba.

Alhali ku
wayewarku itace kwalliya amman jiki ba'a san a
gyara ba, umma tazo ta kara mata ruwan zafi a
cikin bokiti.

Tsohuwa tace yau a sawo bagaruwa
a tafasa ruwan shigar tata da ita don tayi saurin
warkewa.

Kuma ko ina zai hade, in kin koma
gidanki kin kwana biyu ki dinga hada bagaruwa
da alim kina tafasa su kina shiga.IKI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 29
ZURFIN CIKI book 4 part 29
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:31
Umma Tace xa'asiyo tafita tabar su ummi
nacewa to tsohowa kije mana tace bantafiya sai
naga yanda xakiyi ganin ummi tabata lokaci nan
tsohuwa ta dauki tawul din tashiga nadar ruwa
tana dannama Ummi, Ummi tanacewa itadai
abata tayi da kanta.

Tsohuwa tace gaddamace
daku ya'yan yau kinga duk macce dake rufe
jikinta tafita daban damasu tallar jiki.

Ita macce
anfison a sameta ko yaushe da dumi a jikinta,
yawo babu takalmi ko a tsakargidane yana
ragewa mace dumi sbd sanyinda ke ratsa tafin
kafarta har ni'ima yana ragemata.

Sannan zama
atantagaryar suminti shima yana rage mace, da a
ace zaku gane kunga masu saka hijabinnan da
safa? bakaramin wayo suke yimukuba.

Inda za'a
banbance za a samu sunfiku ni'ima da kyau fata,
don haka sai kin dage Ummi dai tayi shiru, amma
aranta cewa take wannan tsohowa ko ina tasan
wannan duk bayanin?

Filo aka ajewa Ummi ta
zauna tana karin kumallo, duk takosa taga
abbanta, koda ta tsinkayi sallamarsa tamkar
tamike ta taroshi.

Amma dole yaje yagaida su
alhaji, tsohuwa tace aefa mu kuma bana munga
takanmu don nan zaka dinga likemana.

Yace
dadin abundai nima nan gidan ubanane, da
uwata.

Umma tana kicin tanamasu dariya.

Tunda
ya zama idanunsu sunsarke da juna sun kasa ko
magana Ummi ce tayi karfin halin lumshe ido
sannan tabude tace sannu daxuwa.

Tasowa yayi
ya tsugunna kusa da 'its, yajikin babyna?sunan
yamata dadi, naji sauki bari in kawomaka abun
karinka. yamika mata tafin hannunsa tasaka nata
yahadasu ya yasarke, murya kasa kasa yace
barshi na' amso.

Ta kula abba mutum ne maison
wasa da tafin hannu.

Ita kanta tanason hakan da
akwai wani sako da tafin hannu ke isarwa acikin
duniyar ma'abota so, kila wannan dalilin ne yasa
abba ke kashema tafin hannusa kudi da mayukan
da ke saka laushin hannu har ita mah ya
saimata.

Koda umma ta shigo Ummi tayi kokarie
amshe hannunta amman abba yaki saki, kuma a
hakan ya karya.

Umma kasa zaman dakin tayi
domin a baki abba yake ba Ummi abinci, umma
nafita taceels / ZURFIN CIKI book 4 part 30
ZURFIN CIKI book 4 part 30
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:33
Daren ranar duk suna kan kujera doguwa a dakin
umma ya bude mata laptop wai yana koya mata
kanta kwance a cinyarsa, umma ta shigo dakin
tsohuwa tace tsohuwa zaifi kyau mu sallami
yaran nan na gaji da ganin wannan aiki nasu ai
tasamu sauki.

Tsohuwa tace suwaiba ina laifin ta
kwan goma ma, umma tace anya zasu kwan
goma nan?

Gobe bakwai guda ta koma dakin ta,
tsohuwa tace shine nan.

Abba yace Ummi kinfa
samu sauki ba zakizo mu koma gidan mu ba?

Tace su umma ne zasu maidani ai nima ya abba
inason in koma yace yau nan zan kwana in sunga
haka sun kuramu, Ummi tace ya abba kayi hnkr
kada ka kwana, shine yace kin yarda goma inxo
mutafi ko ba sanin su umma?

Tasa dariya tace
taf inajin kunya bazan iya binka ba yace to kuwa
zan kwana a nan.

Suna cikin haka umma ta leko
tace abba bazakaje gida ba yanxo fa sha biyu
saura, yace umma nima nan zan kwana.

Ta rike
haba nan din lafia?

Yace to umma nima ba gidan
mu bane?

Ummi tace dama yafi umma kada yaje
wani abu ya rudashi, umma tace a'a abba tashi
ka tafi insha allah gobe Ummi zata koma yayi
murmushi tare da cewa nagode umma.nan dai ya
tattara yanashi yanashi ya tafi gida cike da
kewar matarshi, itama Ummi lamo tayi a gado.

Bayan umma ta gama yimata fada ta bari ta
warke taki ko, sai cewa tayi umma ni fa na
warke.

Umma ta kalli Ummi cike da mamaki tace
yaran yazo saidai a barsu.

Shiyasa akace idan
macce ta isa aure ayi mata a huta.
Chapter 13 · 0% Book details