← Book details Zurfin Ciki Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 18

Sashe 14

Zurfin Ciki Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ita kam Ummi
tana ganin a barta tabi mijinta ta faranta mashi
shine abinda yafi dacewa don yanxu ba inda ya
kai mata dakinta dadi bacci.

Duk da kashedin da
tsohuwa tasa abba dakinta tayi mashi na cewa
ya bar Ummi sai ta kara sati kafin yace zai
kulata da sunan auratayya, bai sa abba jin zai iya
ba.

Don haka koda ta fada mashi cewa yayi kadai
da huruminki da wanda ba naki ba duk sai kin
shiga?

To nidai ki lafa man haka.

Ya fice a dakin.

Ita kuma tana ta fadanta tana cewa "Na shiga din
dan neman yaro, da kyar ya barta ta kara kwana
biyu ya afka mata don shi hkr sa ya kare, ta
nuna mashi ita fa tsoro take ji kada ta wahala, ya
lallasheta yace ba wani wahala.

Ummi tana son
faranta ran mijinta.

Don haka ta jure duk da
yarda yazo mata ba sauki, sai dai tasha albarka
kuma ta kara samun wani matsayi na
musammam a gunsa.

Cikin satin ta zama yar
lelenshin kafin sati biyu ta hardace duk wani
darasi da abba yake koya mata, abba jinsa yake
kamar wannan lokacin ne ya fara rayuwar
angoncinsa.

Sam ya manta yana da wata mata
uwa duniya saida Aunty ta kirashi tace lafia baya
kiran matarsa sai ga abba da girman shi ya girba
karya.

Wai ya kira ya kasa samunsu Aunty ta
yanda tunda farkon tafiyarsu yana kiransu sun
gaisa da bishira tana tmbyrshi ina hibbarta?

Sai
lokacin ya tuna kwana biyu bai ganta don tana
gidansu umman bashir, amman sai yace tana
lafia in yaje zai kirata taji gwarancin yar tata.

La'asar sur suka jero ita da abba don su dan
zaga kurum.

Sun shigo gidan ahmad da muktar
duk basu rabu ba saida sukaji sun saba da ummi.

Don ita haka take yana da wuya kayi zaman awa
guda da ita bakaji ta kwanta maka a rai ba.

Abba
yaji dadi yarda Ummi ta nuna kauna ga matan
abokanin nasa, yasan bada jimawa ba matansu
zasu zama kawaye kamar yarda yaso da bishira
amman taki.

Daga can suka nufi layin su gidan
su umman bashir Ummi tace su fara shiga su
dauki muhibba abba yace bazata yarda dake ba.

Ummi tace zata yarda muje a ran abba tsoro
yake gada umman bashir ta gwasaleta Ummi, sun
sameta tana shara da sauri Ummi ta amsa ta
soma sharewa hakan ya faranta ran abba sai dai
da ya kalli umman bashir yaga tana hararar
Ummi, saida ta gama taxo ta zauna suka gaisa
abba na rike da hibba tayi kaca kaca da kunu
gashi duk ya dunkule dama ko lokacin da bishira
tana nan haka zakaga yar duk kazanta.

Ummi ta
bude post dinta ta cire dari biyu guda biyu ta
mikawa umman bashir gashi umma kin sai goro
saida ta tabe baki ta amsa babu ko godia, sai dai
abba cikin jin dadi yace angode, da hibba taki
binsu Ummi tace kamal xo ka siyo wa hibba
alawa, kinga baba kamal baya nan xo muje in
sayo maki.

Cikin sa'a sai taxo zasu fita sai ga
bashir dauke kai yayi tare da jan tsaki daya shiga
gidan sai ya hau umma da fada Wai ta daina
barin Ummi da wannan abba suna zuwa in ba
haka ba zasu kawo mata wani asiri.

Umman
bashir tace suta zuwa ma indan ta nine mi jiya
tayi bare yau, ka gansu dari hudu yanxu ta bani
don haka bazan hana zuwa ba amma fa ina nan
yarda nake bazan canza ba, suna shiga gidan su
umma kicin ta wuce ruwan zafi ta zubu ta cude
muhibba tas, ta wanke mata kai ta chajeshi ta
shafeta da mai nan ma basu jima ba suka nufi
gida zanen umma ta ansa ta goye muhibba, shine
ya bude dakin bishira duk kayan yarinyar sun rine
da datti, Ummi dai ta zazzaba yace .ba maidata
za'ayi ba, Ummi tace ta dan kwana biyu mana.

Yace tana fitsari fa.

Ummi tace kasawo muna
pampers Yace shikenan duk da ya nuna bayaso
yarinyar ta zauna gurinsu amman yaji dadi sai
lokacin bacci daya shigo ya shigo da pampers din
ta saka mata Sannan ta kwantar da ita can gefe
ta azama mata pillo guda haba guda baya, su
kuma suka kwanta a nasu makwancin suka
cigaba da soyewa. novels / ZURFIN CIKI book 4 part 31
ZURFIN CIKI book 4 part 31
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:36
Ummi tana son yara don haka hibba ta dinga
samun gata, satinta guda umman bashir ta dinga
jaraba sai an dawo da ita.

Wai kwadayi ne don in
bishira tadawo ta bata tsaraba, amma koda ta
tafi da hibban yarinyar sai taqi sai kuka har dasu
amai.

Dole aka dawo da ita, don alhaji karami
cewa yayi atattara mata kayanta duka inyasake
samun an maido da ita sai ya saba ma umman
bashir.

Hakan da babbar sallah abba yakashe
musu kudi ita da hibba, sai dai duk abinda yasai
ma ummi to ya aje ma bishira nata.

Ita kam tana
can duk addu'arta akan ummi ne, kafin ta dawo
ummi tafita, don haka data dawo da kwarin
gwuiwarta ce wa bazata samu ummi agidan ba.

La'asar sakaliya, direban gidansu ya iso da ita
gidan kamar yanda mahaifinsu ya umarce shi
cewa in ya dauko su kada yaso dasunan, ya dire
kowa agidanta.

Kasancewar unguwa uku suka
soma zuwa sai anty ta taya bishira diban kaya
su shiga.

Daidai kofar dakin bishiran abba na
kwance rigingine, 'yar T-shirt ajikinshi fara kar.

Dawandon jeans gajere iyaka gwuiwa.

Ummi
kuma dogon wando ne irin mai kama jikin nan
dariga mai kamar singileti kanta yasha kana nan
kitso, tayi filo da kirjinshi yana bata labarin wata
mota da yake son yabada tashi yayi ciko.

Ita
kuma tana ce masa ya dai je ya shawarci umma,
muhibba kuwa tana ta faman wasa da sabbin
kayan wasanta da ummi tasai mata.

Ita ma cikin
'yar shimi mai kyau, kanta kuwa ummi tayi mata
kitson (3 in 1).

Sororo bishira ta tsaya tana
kallonsu, sam bata tsammaci a irin addu'ar
datayi zata dawo ta samu ummi agidan ba.

Basu
ganta ba saida anty tayi sallama tare da cewa, ya
naga kin tsaya? da sauri suka waiwayo duk suka
mike.

Gaban ummi yayi wata muguwar faduwa,
amma duk dahaka cikin fara'a ta nufe su, bishira
ta hade rai matuqa sannan taqi ko kallon ummi
ta nufi 'yarta.

Anty kam cikin fara'a suka gaisa da
ummi harta zage jakarta dake kafadarta tabawa
ummi wani dan agogo mai kyau.

Nan dai ummi
tayi ta godiya shima abba ya mata godiya.

Abban
ne ya shigar mata da kayan daki, ummi tana
cewa anty kin mana dawowar bazata, dakin fada
da an share miki dakin.

Nan ma bata tanka ba,
ummi dai data gaji dayi mata sannu bata amsa
ba sai kurum ta nufi dakinta, zuciyarta babu dadi,
tasan yanzun ya Abba zai raba jin da yake da ita
zuwa su biyu.

Bishira tayi kyam tana ta qamshi
don anty baza su barta tazauna masu da qazanta
ba, ga haqorin makka an sako ana ta qwambo.

Ranar dakinta Abba yakwana, yanda bata ga
wata rawar jiki daga gare shi ba tayi zargin ummi
tasamu lafiya.

Hakan ya qara dagula mata lissafi,
tayi rabon tsarabarta daga kawayenta sai
maqota, don ko umman bashir daga zam-zam
bata qara mata komai ba.

Dama tana cike da
haushin umman data bari ummi ta daukar mata
'ya gashi nan muhibba ta liqe ma ummi.

Hakan
ya shaqar da umman bashir har tace amaida
mata zam-zam dinta ita bata sha.

Wato don taje
makka shine zato zo ta canza hali?

Ita kuma
bishira ta amsa tare da cewa, ai ba ita ta aike ni
makkan bada har sai tazabi abinda zan bata.

Ummi ko zam zam din ba abata ba, kuma ko
ajikinta.

Abba kam shita kawo masa dogayen
riguna da T-shirt masu kyau, amma su anty ne
suka matsa mata sai ta saya.

Ranar daya dawo
daga dakin bishira ummi tana fashin sallah gashi
yanuna yana dalarura alokacin.

Sai tace ta yafe
masa yau dagobe yaje gurin anty bishira, yace
A'a tace ba haramun bane nina amince, yace
nasani.

Shiba yason sai yatafi tafara damuwa ko
tazo tana jin haushinsa, tace ba komai saida
yatafin kuwa har kuka tayi don kishi.

Amma
tabawa zuciyarta hakuri tasan wata rana wannan
jarumtar datayi zata zame mata alkhairi.

Ita ko
bishira koda yazo mata sam bata damu ta
bincika ba, tunda taga ba girkinta ba, saima ta
hau murna yayo satar kwana ya bata musamman
dataga dayayi wanka yakoma dakin ummi, haka
washegari.

Don haka sai tashiga daga hanci har
da 'yan habaice habaice, kafin tadawo tun da
dama da namiji dan uwansa yake kwana.

Tana
nufin ummi bata ba tayi masa amfanin komai
wannan yasa ummi ta daura aniyar cusa mata
takaici, aranta tace tunda cinikinki labe nikuma
zansa miki hawan jini.

Kamal yazo daukar abincin
da ummi ta saba sawa yau har da kunun gyada
tayi.

Bishira ta kalle shi, wai kai wannan abincin
na waye kullum kake zuwa dauka?

Yace na
ummarmu ne.

Ta taba baki, ummar nan taku
kwadayinta yayi yawa, ko kuwa itama asirin ya
kamata ne?

Kamal kuwa yaje yafada sai ga
umman bashir agidan suna zage zage da bishira,
tana ce ma bishira dadin abin gidan dana nazo
kwadayin ba gidan ubanki ba.

Marowaciyar bnza
ai dama ina da cikinki, lokacin da Abba yasai
maku TV, yace ki bani naki sai ki kace gara kiyar.

Bishira tace, Eh na hana TV aiba wani shegen ya
sai minba, ubana yasai min, kuma nace mai
kwadayin yarinyar daki kace uwarta mai asiri,
menene na amsar abincinta kici banda kwadayi?

Shiyasa kika bata 'yata ashe don asami abinci
ne, umman tasa kuka ni ke ke zagi?

Yau ko abba
zai zo gidan nan zai zaba ko ni ko ke.

Ummi dai
tana daki tana jinsu. (aranta tace dadi na da
gobe saurin zuwa).

Bishira tace dama ya darajaki
ne shine za kice haka, yazo din nace mai kwadayi
harda rainawa na baki zam zam butulu duk
abinda na miki kin manta kece kika aikeni
makkan?
Chapter 14 · 0% Book details