Sashe 7
Zuciyar Mace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hasana ta yi kamar ba ta ji shi ba, don ita ma ta san gishirin ya yi yawa, ta manta shaf ta zuba, dab da za ta gama girkin ta ƙara zubawa, don haka ba ta da ta cewa. Ya sake tsaki ya ce"Wannan abincin dai ci kar ka mutu kawai, an zabga wa mutane gishiri a abinci" Ya sake tsaki.
A fusace ya ce"Ina ta magana...!"
Ta ce"To me kake so na ce? Ku maza dama haka kuke, sai mace ta yi daidai sau dubu, ba za ku tabe ta ba, amma idan ta yi ba daidai ba sau ɗaya sai kun yi ƙorafi, hannuna ne ya kufce na saka da yawa".
Ya ce"Hmm! Gaskiya na yarda, duk wanda ya mutu da mace ɗaya shi ya ga ƙarshen wulaƙanci, gida biyu maganin gobara, Allah dai Ya kai damo ga harawa!".
Ba ta sake bi ta kansa ba, har ya gama ya fice.
Yau da daddare da wuri ya dawo, hakan ya sa Hasana ta raya a ranta ƙila yau ɗin ya kira ta, amma sai ta ji shiru, don ko leƙo su ma bai yi ba, tana jin lokacin da ya saka sakata a ɗakin, bayan ya gama uzururrukansa, kamar awa ɗaya a tsakani ta tashi ta sakko daga gadon, ta kalli agogo, sai yanzu goma ta yi, ta manta rabon da ya dawo gida kafin ƙarfe goma, sai dai idan ana tsananin sanyi, ko kuma da damuna. Ta saka hijjabi, ta fito a hankali kamar jiya, ta leƙa ta windo, ta ga ɗakin da hasken tv ga kuma sauti alamar ya kunna kallo, amma yana kwance a katifa waya kare a kunnensa ga murmushi shimfiɗe a fuskarsa, da alama yana cike da shauƙi, takaici ya rufe ta, duk abin da Nura yake yi mata na ɓacin rai, har yanzu tana ƙaunarsa, soyayya ce aka sha ta nuna wa sa'a kafin aurensu.
Ta gama yankewa a zuciyarta sai ta hana shi sukuni, don haka ta koma ta wajen ƙofar ta fara ƙwanƙwasawa. Nura da ya nutsa a kofin soyayya da wata wacce ya yi mata laƙabi da baba Leemat, sosai ya yi mamakin wannan bugun ƙofar, da ya dawo sai da ya duba ƙofar Hasana ya ga a rufe, kuma ya santa da baccin wuri, ya ce da baba Leemat yana zuwa, ya katse kiran yana haɗe gira ya ce"Wace?"
Ta ce"Ni ce".
Ya zo ta buÉ—e yana cewa"To ya aka yi, ni har na fara bacci ma?"
Za ta kutsa kai ciki, ya É—an tare yana cewa"Wai mene ne?"
Ta ce"Akwai wani film da nake kallo a bollywod, shi ne na ce tun da akwai wuta ga ka, ka dawo da wuri bari na zo na ci albarkacin turakar Oga". Ta ƙarasa da murmushi.
Sai ya matsa ta shige ta zauna, ta canza tasha, amma gabaɗaya hankalinta yana kanshi, wayarsa tana ta kawo haske ya ƙi ɗauka, can dai ya tashi ya fice daga ɗakin, ya tura ƙofar ɗakinta a hankali ya shiga, ya haska ya ga Aiman ya baje yana ta baccin shi, ya ji fanka, ya kai hannu ya fara jijjiga shi, yaro kuwa ya fara mutsu-mutsu, sai ya tashe shi ya zaunar, ai kuwa ya fara ƙananun kuka, ya yi saurin ficewa daga ɗakin.
Ya koma nashi É—akin yana cewa"Na ji kamar kukan Aiman".
Ita ma ta jiyo sama-sama, don haka ta tashi, ta ce"Bari na É—akko shi".
Ya ce"Ina? Kin ga Malama ki yi kwanciyarki kawai, saboda ni ma bacci nake ji".
Tana fita ya mayar da sakata.
*********
Baba ransa ya kai maƙurar ɓaci, ya kai ya kawo a tsakar gida rungume da hannuwa a bayansa, ya ma kasa cewa komai. Can Mama Karime ta ce"Malam ba fa shiru za ka yi, kamata ya yi a bi sahunta tun kafin ta yi nisa".
Sai kuwa ya zaburo kamar mai jira, ya ce"To a gidan uban wa zan nemo ta? Ni dai na san abu ɗaya, yanzu Nuratu baƙinciki da hassada kawai take yi mini, wallahi saboda ta hango ɗan abin da zan samu a jikinta shiyasa ta yi mini haka, amma babu komai". Ya shige ɗakinsa.
Ita kuwa Nuratu motarsu tana harbawa titi, ita ma ta harba duniyar tunanin makomarta, sam ba ta hango haske a gobenta, ta san babu ta yadda za a yi Abdul ya karɓi uzurinta, fatanta ya yarda da ita ko da ba zai aure ta ba, ita ta yarda ta sadaukar da mutuncinta don farincikinsa. Sai dai idan bai aure ta ba, wa zai aure ta ya kalleta da mutunci? Gani take shi ma Alhaji Hashimu da ya yi alƙawarin aurenta ya yi maganga ne kawai a cikin mayen giyar so, bayan auren ba lallai ya riƙe ta da daraja ba, sannan yana da mata har uku da yaran da ba ta san adadinsu ba, ta tabbata wasu sun girme mata, yanzu ya za ta yi idan suka ji ta yi ciki a waje kafin auren? Anya gori zai bar ta ta zauna lafiya?
Da wannan tunane-tunanen fal zuciyarta aka ƙarasa Kaduna, kowa ya sauka, ta samu babur ya ƙarasa da ita unguwar da za ta je, sai da ta kai ƙofar gidan sannan ta fara fargaba, ta san dai wannan tafiyar ba gudu sunanta ba, don inda ta zo ɗin ba mafaka ba ce ba, kawai ta zo ne saboda ƙwaƙwalwarta ta samu hutu, kuma zuciyar Baba ta yi sanyi, don idan ya tashi yi mata hukunci ta samu sassauci. Ta kai hannu tana ƙwanƙwasa get ɗin gidan, sai da ta buga sau uku, sannan daga ciki aka tambaya waye, ta ɗaga murya ta ce"Ni ce".
Babu jimawa aka buÉ—e, wata mace ce wacce za ta kai shekara ashirin da bakwai ta buÉ—e, ta É—an saki fuska ta ce"Nuratu" Tana kallon tsohuwar akwatinta.
Nuratu ma ta É—an saki fuska ta ce"Anti Nawwara".
Ta matsa mata, ta shiga jaye da akwatin, Nawwarar ta yi gaba tana binta har zuwa falo, ta zauna, ita kuma ta ƙwala wa mijinta kira"Honey!".
Sai ga shi ya fito, yana gyara agogon hannunsa, ya yi turus ganin Nuratu, da mamaki ya ce"Nuratu, ke ce kuwa?"
Sai idonta ya kawo ruwa, ta ce"Ni ce, Yaya Kabir ina kwana".
Bai amsa gaisuwar ba, ya ce"Amma dai ba lafiya ba ko Nuratu?"
Nawwara ta ce"Ina fa lafiya? Ko sadakar ukun babarta ba a yi ba, ka ga ta yo nan ai ka san akwai matsala".
Ya ce"Mene ne ua faru Nuratu?" Sai ta fashe da kuka.
Nawwara ta ce"A'a yi haƙuri, ta huta tukunna, kafin nan zuciyarta ta yi sanyi ma".
Ta ja hannunta, ta kai ta É—aki, ta zaunar a bakin katifa, ta koma kitchen ta haÉ—o mata shayi da biredi, har ma da sauran dankali da suka rage, ta kai mata, ta ce"Maza ki ci".
Dayake gidan ba baƙonta ba ne, sai ta fara tashi ta yi wanka, ta canza kaya, sannan ta ci abincin, ta ɗakko wayarta, ta kunna data, saƙonni suka gama shigowa tass babu na Abdul, hawaye ya sakko mata, ta san yana can cikin ƙunci, ta yi masa sallama a rubuce, ba ya online, babu jimawa kuma ta ga tik biyu, alamar ya hau, ya duba saƙon nata, sai ya fara typing, tana ta fargabar abin da zai rubuto, har ya gama ya turo, "Wannan shi ne sakayyar soyayyata a gare ki ko? Na gode Nuratu, Allah Ya saka da alkhairi". Abin da ya rubuta kenan, sai ya bi bayansa da stika ta namiji yana kuka sosai.
Ita ma kukan ta fara, ta danna viice ta ce"Na san ban cancanci ka saurare ni ba, amma don Allah ka daure ka ji bayanina, ba don halina ba, na yi komai ne saboda cika maka burinka, rayuwarka ta inganta".
Bayan ya saurara ya tura mata emoji na mamaki, ta sake yin voice ta ce"Don Allah ka yi haƙuri, ka fahimce ni, na fi kowa shiga ƙunci sanadin wannan kuskuren da na yi".
Ta typin ya ce mata"Cikin wane ne? Kar ki ba ni amsar da za ta wuce kalma uku, don ba ni da lokacin sauraron tsarinki".
Sarai ta san halinsa, tun da ya ce haka, idan ta ba shi amsa akasin yadda ya buƙata, zai iya yin blocking ɗinta, don haka ta rubuta masa "Agent ɗin da ya yi maka hanyar tafiyarka ne" Ta tura masa.
Abdul yana karantawa, ƙirjinsa ya doka da ƙarfi, ya fara karanto innlillahi wa inna ilaihi raji'un! Ya fara tunanin yanzu a kan shi ta ba da kanta ga wani banza? Nan ya tuna ranar da yake tunanin abun ya faru, da abokinsa Usman ya ce masa, ya ganta ta fito daga mota tare da Agent ɗin nan, amma Abdul fir ya ce ba ita ba ce, sannan a ranar mutumin ya kira shi ya yi masa alƙawarin tafiya. Ya kashe data yana mamakin irin _zuciyar mace_.
08028966015
[11/21, 11:35 AM] Sadiya Abdulrazak: *ZUCIYAR MACE*
BY
SADIYA ABDULRAZAƘ
*FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATIONS*
(Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation)
https://chat.whatsapp.com/F6SvzSmHfQfJmhV5NN5CDY
PAGE 6
Shiru bai ma sake kunna data ba, ballantana ta ji hukuncin da zai yanke, ta sake tura masa saƙo, ta ce"Ka yi haƙuri don Allah, ni ban ce dole sai ka aure ni ba, kawai dai ka yarda ba yaudara ce ta saka na yi haka ba, ba kuma son abin duniya ba, kawai na yi ne saboda na taimake ka".
A fusace ya ce"Ina ta magana...!"
Ta ce"To me kake so na ce? Ku maza dama haka kuke, sai mace ta yi daidai sau dubu, ba za ku tabe ta ba, amma idan ta yi ba daidai ba sau ɗaya sai kun yi ƙorafi, hannuna ne ya kufce na saka da yawa".
Ya ce"Hmm! Gaskiya na yarda, duk wanda ya mutu da mace ɗaya shi ya ga ƙarshen wulaƙanci, gida biyu maganin gobara, Allah dai Ya kai damo ga harawa!".
Ba ta sake bi ta kansa ba, har ya gama ya fice.
Yau da daddare da wuri ya dawo, hakan ya sa Hasana ta raya a ranta ƙila yau ɗin ya kira ta, amma sai ta ji shiru, don ko leƙo su ma bai yi ba, tana jin lokacin da ya saka sakata a ɗakin, bayan ya gama uzururrukansa, kamar awa ɗaya a tsakani ta tashi ta sakko daga gadon, ta kalli agogo, sai yanzu goma ta yi, ta manta rabon da ya dawo gida kafin ƙarfe goma, sai dai idan ana tsananin sanyi, ko kuma da damuna. Ta saka hijjabi, ta fito a hankali kamar jiya, ta leƙa ta windo, ta ga ɗakin da hasken tv ga kuma sauti alamar ya kunna kallo, amma yana kwance a katifa waya kare a kunnensa ga murmushi shimfiɗe a fuskarsa, da alama yana cike da shauƙi, takaici ya rufe ta, duk abin da Nura yake yi mata na ɓacin rai, har yanzu tana ƙaunarsa, soyayya ce aka sha ta nuna wa sa'a kafin aurensu.
Ta gama yankewa a zuciyarta sai ta hana shi sukuni, don haka ta koma ta wajen ƙofar ta fara ƙwanƙwasawa. Nura da ya nutsa a kofin soyayya da wata wacce ya yi mata laƙabi da baba Leemat, sosai ya yi mamakin wannan bugun ƙofar, da ya dawo sai da ya duba ƙofar Hasana ya ga a rufe, kuma ya santa da baccin wuri, ya ce da baba Leemat yana zuwa, ya katse kiran yana haɗe gira ya ce"Wace?"
Ta ce"Ni ce".
Ya zo ta buÉ—e yana cewa"To ya aka yi, ni har na fara bacci ma?"
Za ta kutsa kai ciki, ya É—an tare yana cewa"Wai mene ne?"
Ta ce"Akwai wani film da nake kallo a bollywod, shi ne na ce tun da akwai wuta ga ka, ka dawo da wuri bari na zo na ci albarkacin turakar Oga". Ta ƙarasa da murmushi.
Sai ya matsa ta shige ta zauna, ta canza tasha, amma gabaɗaya hankalinta yana kanshi, wayarsa tana ta kawo haske ya ƙi ɗauka, can dai ya tashi ya fice daga ɗakin, ya tura ƙofar ɗakinta a hankali ya shiga, ya haska ya ga Aiman ya baje yana ta baccin shi, ya ji fanka, ya kai hannu ya fara jijjiga shi, yaro kuwa ya fara mutsu-mutsu, sai ya tashe shi ya zaunar, ai kuwa ya fara ƙananun kuka, ya yi saurin ficewa daga ɗakin.
Ya koma nashi É—akin yana cewa"Na ji kamar kukan Aiman".
Ita ma ta jiyo sama-sama, don haka ta tashi, ta ce"Bari na É—akko shi".
Ya ce"Ina? Kin ga Malama ki yi kwanciyarki kawai, saboda ni ma bacci nake ji".
Tana fita ya mayar da sakata.
*********
Baba ransa ya kai maƙurar ɓaci, ya kai ya kawo a tsakar gida rungume da hannuwa a bayansa, ya ma kasa cewa komai. Can Mama Karime ta ce"Malam ba fa shiru za ka yi, kamata ya yi a bi sahunta tun kafin ta yi nisa".
Sai kuwa ya zaburo kamar mai jira, ya ce"To a gidan uban wa zan nemo ta? Ni dai na san abu ɗaya, yanzu Nuratu baƙinciki da hassada kawai take yi mini, wallahi saboda ta hango ɗan abin da zan samu a jikinta shiyasa ta yi mini haka, amma babu komai". Ya shige ɗakinsa.
Ita kuwa Nuratu motarsu tana harbawa titi, ita ma ta harba duniyar tunanin makomarta, sam ba ta hango haske a gobenta, ta san babu ta yadda za a yi Abdul ya karɓi uzurinta, fatanta ya yarda da ita ko da ba zai aure ta ba, ita ta yarda ta sadaukar da mutuncinta don farincikinsa. Sai dai idan bai aure ta ba, wa zai aure ta ya kalleta da mutunci? Gani take shi ma Alhaji Hashimu da ya yi alƙawarin aurenta ya yi maganga ne kawai a cikin mayen giyar so, bayan auren ba lallai ya riƙe ta da daraja ba, sannan yana da mata har uku da yaran da ba ta san adadinsu ba, ta tabbata wasu sun girme mata, yanzu ya za ta yi idan suka ji ta yi ciki a waje kafin auren? Anya gori zai bar ta ta zauna lafiya?
Da wannan tunane-tunanen fal zuciyarta aka ƙarasa Kaduna, kowa ya sauka, ta samu babur ya ƙarasa da ita unguwar da za ta je, sai da ta kai ƙofar gidan sannan ta fara fargaba, ta san dai wannan tafiyar ba gudu sunanta ba, don inda ta zo ɗin ba mafaka ba ce ba, kawai ta zo ne saboda ƙwaƙwalwarta ta samu hutu, kuma zuciyar Baba ta yi sanyi, don idan ya tashi yi mata hukunci ta samu sassauci. Ta kai hannu tana ƙwanƙwasa get ɗin gidan, sai da ta buga sau uku, sannan daga ciki aka tambaya waye, ta ɗaga murya ta ce"Ni ce".
Babu jimawa aka buÉ—e, wata mace ce wacce za ta kai shekara ashirin da bakwai ta buÉ—e, ta É—an saki fuska ta ce"Nuratu" Tana kallon tsohuwar akwatinta.
Nuratu ma ta É—an saki fuska ta ce"Anti Nawwara".
Ta matsa mata, ta shiga jaye da akwatin, Nawwarar ta yi gaba tana binta har zuwa falo, ta zauna, ita kuma ta ƙwala wa mijinta kira"Honey!".
Sai ga shi ya fito, yana gyara agogon hannunsa, ya yi turus ganin Nuratu, da mamaki ya ce"Nuratu, ke ce kuwa?"
Sai idonta ya kawo ruwa, ta ce"Ni ce, Yaya Kabir ina kwana".
Bai amsa gaisuwar ba, ya ce"Amma dai ba lafiya ba ko Nuratu?"
Nawwara ta ce"Ina fa lafiya? Ko sadakar ukun babarta ba a yi ba, ka ga ta yo nan ai ka san akwai matsala".
Ya ce"Mene ne ua faru Nuratu?" Sai ta fashe da kuka.
Nawwara ta ce"A'a yi haƙuri, ta huta tukunna, kafin nan zuciyarta ta yi sanyi ma".
Ta ja hannunta, ta kai ta É—aki, ta zaunar a bakin katifa, ta koma kitchen ta haÉ—o mata shayi da biredi, har ma da sauran dankali da suka rage, ta kai mata, ta ce"Maza ki ci".
Dayake gidan ba baƙonta ba ne, sai ta fara tashi ta yi wanka, ta canza kaya, sannan ta ci abincin, ta ɗakko wayarta, ta kunna data, saƙonni suka gama shigowa tass babu na Abdul, hawaye ya sakko mata, ta san yana can cikin ƙunci, ta yi masa sallama a rubuce, ba ya online, babu jimawa kuma ta ga tik biyu, alamar ya hau, ya duba saƙon nata, sai ya fara typing, tana ta fargabar abin da zai rubuto, har ya gama ya turo, "Wannan shi ne sakayyar soyayyata a gare ki ko? Na gode Nuratu, Allah Ya saka da alkhairi". Abin da ya rubuta kenan, sai ya bi bayansa da stika ta namiji yana kuka sosai.
Ita ma kukan ta fara, ta danna viice ta ce"Na san ban cancanci ka saurare ni ba, amma don Allah ka daure ka ji bayanina, ba don halina ba, na yi komai ne saboda cika maka burinka, rayuwarka ta inganta".
Bayan ya saurara ya tura mata emoji na mamaki, ta sake yin voice ta ce"Don Allah ka yi haƙuri, ka fahimce ni, na fi kowa shiga ƙunci sanadin wannan kuskuren da na yi".
Ta typin ya ce mata"Cikin wane ne? Kar ki ba ni amsar da za ta wuce kalma uku, don ba ni da lokacin sauraron tsarinki".
Sarai ta san halinsa, tun da ya ce haka, idan ta ba shi amsa akasin yadda ya buƙata, zai iya yin blocking ɗinta, don haka ta rubuta masa "Agent ɗin da ya yi maka hanyar tafiyarka ne" Ta tura masa.
Abdul yana karantawa, ƙirjinsa ya doka da ƙarfi, ya fara karanto innlillahi wa inna ilaihi raji'un! Ya fara tunanin yanzu a kan shi ta ba da kanta ga wani banza? Nan ya tuna ranar da yake tunanin abun ya faru, da abokinsa Usman ya ce masa, ya ganta ta fito daga mota tare da Agent ɗin nan, amma Abdul fir ya ce ba ita ba ce, sannan a ranar mutumin ya kira shi ya yi masa alƙawarin tafiya. Ya kashe data yana mamakin irin _zuciyar mace_.
08028966015
[11/21, 11:35 AM] Sadiya Abdulrazak: *ZUCIYAR MACE*
BY
SADIYA ABDULRAZAƘ
*FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATIONS*
(Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation)
https://chat.whatsapp.com/F6SvzSmHfQfJmhV5NN5CDY
PAGE 6
Shiru bai ma sake kunna data ba, ballantana ta ji hukuncin da zai yanke, ta sake tura masa saƙo, ta ce"Ka yi haƙuri don Allah, ni ban ce dole sai ka aure ni ba, kawai dai ka yarda ba yaudara ce ta saka na yi haka ba, ba kuma son abin duniya ba, kawai na yi ne saboda na taimake ka".