Sashe 3
Yar Zaman Wanka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Imran ne tafe a kan machine ɗinsa roba -roba matashi ne matashi ne dan ba zai haura shekara 26 ba ɗan gayu ne dan yanzu ma yana tafe a machine ɗin sai wani dube -duben jiki yake, lokaci zuwa lokaci yana sanya hannu ya karkaɗe rigarsa duk da ba komai a jiki amma saboda kawai tsabar tsafta da ƙyanƙyami yake karkaɗewa. Imran bashi da son mutane gashi da ƙyamatar ya ga an kusanci inda yake sai wanda ya yi niyya sai kuma wanda jininsa ya haɗu da nasa. Ba ya son duk wani abu da zai shiga tsakaninsa da farincikinsa wato matarsa Sadiya yana son ta sosai saboda auren soyayya suka yi hakan ya sanya ba ya son duk wani abu da zai sa ya yi nesa da ita ko ya nesanta shi da abar ƙaunar tasa. Ya fi so koyaushe idan yana gida ya kasance tare da matarsa, gashi mutum mai yawan buƙata, shi ya sa ko yaya ba ya son wani abu ya haɗashi da Sadiya bare ta yi fushi, idan kuwa hakan ta kasance to ya kan yi iya ƙoƙarinsa ya shawo kan ta dan kar ya rasa biyan buƙatarsa dan bashi da haƙuri ko kaɗan a wannan harkar, sai ya samu matar tasa ita ma mai burin faranta masa bata so ko kaɗan ta hana shi kan ta.
Ya kusa ƙarasowa gidansa ya hango wata ƙatuwar jakar bakko a ƙofar gidan, cikin mamaki yake kallon jakar da kuma neman dalilin ajiyeta a ƙofar gidansa.
Cikin sauri da azama ya ƙaraso har yana neman faɗuwa a machine ɗin dan ba ya ƙaunar abin da zai haɗa shi da kayan wasu, dan shi akwai tsare gidan ko maƙota iyakarsu gaisuwa tsakaninsa da su dama shi ba wani yawan magana yake ba bare zaman majalissa in har ba wurin aiki ya tafi ba to yana gida tare da iyalansa, sai ko idan ya je gaishe da Hajiyarsa. Yana faka machine ɗin ya ƙanƙance idanu yana kallon jakar, kallon da ya mata ma sai ya ji yana tsantsaninta dan sai ya ga duk ta yi wani ƙura, ko kuwa dan bai yarda da jakar bane oho ya ɗago kai yana son gano yadda aka yi jakar ta zo ƙofar gidansa sai ya ji wata murya tamkar daga sama an ce.
"Shikenan ma na huta ga Imirana nan" Shiru ya yi tare da runtse idanunsa da ƙarfi, jin an kirashi da sunan da ba ya so kwata-kwata, kuma ma duk duniya ya san babu mai kiransa da sunan nan sai kakar Sadiya wato Inna Azumi ita kaɗai ke kiransa, kuma ya shaida muryarta dan ko daga bacci ya tashi ba zai kasa shaida muryarta ba.
Shi ya rasa me yasa matar nan take son takurawa rayuwarsa, sam ba ya son wannan nuna ƙoƙon usulin da take nuna masa dan yana auren jikarta, shi ko ƴarta yake aure ba ya son takurawa amma ita ta kasa ganewa, sannan duk miskilancinsa na ƙin son magana da mutane sai da ya daure ya faɗa mata cewa Imran ake kiransa dan idan ta kirasahi da Imirana nan ji yake kamar ta kwaɗa masa gudum a kan sa.
"Ashe ma kana kusa har nake bin gidan maƙotanku ka ganni nan saukar yanzu tsal ɗin nan" Ta ƙara faɗa tana ƙarasowa wajensa ba tare da ta jira ya ce wani abu ba, cije gefen lips ɗinsa ya yi yana ji da a ce wani ne da ban ba tsohuwa ba yake damunsa kamar yadda tsohuwar nan ke damunsa da sai ya ɗau mummunan mataki.
"Eh" Kawai ya ce hakan ma dan ta kasa kunne ne ta gane me ya ce amma da gungune ya yi maganar.
"Allahu akbar Imirana har yanzu dai kana nan da wannan mugun halin naka, kai wane irin mutum ne da baka sakewa da mutane ku yi magana ma ta fatar baki kawai ni fa kakar ka ce ba sirikar ka ba" Ta faÉ—a tana kallon fuskarsa da ya haÉ—e ta murtuk kamar zai saki kuka.
"Sauri nake" Shi ne kawai abin da ya ce, shi ma dai da ƙunƙunen ya faɗa.
"Oh Allah na shiga aljanna na maƙale, yanzu baka ce min Inna ina wuni an zo lafiya ba sai ka zauna kana min magana kamar mai ciwon haƙori, ko kallon arziƙi na kasa samu daga wajenka"
Banza ya mata ya fara ƙoƙarin buɗe ƙofar gidan.
Inna Azumi kuwa baki ta taɓe, dan ta lura in ta ce za ta ga yadda take so to zuciyarta sai ta yi bindiga bata samu yadda take son ba, gwara ta lallaɓashi a rabu lafiya, bare ita da ta zo dandalar arziƙi.
"Sa'adiyyar ta sauka ne?" Ta faɗa tana kallonsa yana cire kwaɗo daga jikin ƙofar gidan.
Bai bata amsa ba a take ta tuna da katoɓarar da ta yu, dan dama Sa'adiyya take kiran Sadiya amma saboda kwainane irin nasa ya ce wai ta fiya ɓatawa mutane suna ganin baya iya faɗar Sadiya sai Sa'adiyya sai take cewa Halima saboda jarabar Imran ɗin dan duk ranar da ta zo gidansa haka zai yi ta mita a ƙunƙunen nan har dai ta ɗan canja sannan ta samu salama.
"Na ce Halimar bata sauka bane?" Ta gyara sunan dan ta matsu ta ji halin da jikarta ke ciki.
" Ta sauka" Ya faɗa a takaice yana tura ƙofar gidan ya shige ya bar Inna Azumi a tsaye baki sake, da ya shige ma sai da ya ɗan turo ƙofar.
"Yau na ga abin da ya isheni, a haka zan yi har kwana hamsin ɗin, ana wannan zaman doya da manjan, taɓɗi aikiwa duk abin amarya sai an sha manta wallahi ko me za ka yi sai na zaina ZAMAN WANKAN nan dan ban ga abin da zai sanya na fasa ba dan kana wannan fisfigar" Ta faɗa a ranta tana tura ƙofar ita ma ta shiga gidan tare da jan jakarta ta shigar da ita dakyar saboda nauyi, Imran da ya dawo domin ya ɗakkowa Sadiya zani saboda zannuwan sun yi kaɗan yana cikin sanya zanin a leda ya jiyo ƙaran jakar Inna Azumi tana janta ƙiiiii.
"Me yasa matar nan ta shigo min da ƙazamar jakarta gidana" Ya faɗa a ransa, ya yi sauri ya fito daga ɗakin ya dawo falo ya sanya hannu ya fusgi labule da ƙarfi ya fito daga ɗakin tare da rufo ƙofar dan ma kar ta yi gigin shigar masa da jakarta ɗaki dan ba ya jin zai iya bacci ma idan jakar tana ɗakin saboda ƙyanƙyami.
Baki sake Inna Azumi ke kallonsa har ya gama kulle falon, yana wani É—aÉ—É—aga kai kamar ya ga kashi ya ce.
"Asibiti zan koma" Sai da Inna Azumi ta saurara da kyau sannan ta gane me ya ce.
"Yo ni ma ina na ga ta zama, ai ba zama wai an É—aurawa karya zani, mu tafi sabitin in je in gan su dan can ma gidansu na fara zuwa a rufe, na zo nan É—in ma ashe dai basu dawo daga asibitin ba"
"Eh" Kawai ya ce dan shi kamar mai ciwon baki haka yake ba ya son magana ko Sadiya sai ita ta yi ta masa hira shi dai sai umm da um, um kawai ko da zai yi maganar ma to ba wata mai yawa ba sai dai kuma ranar da ya ga dama sai ya yi maganar amma ba sosai ba.
Yana fitowa ita ma ta fito ya rufe gidan, aikuwa sai ga wani mai napep zai wuce ya tsayar da shi ya ce ya É—auketa sai ya biyo bayansa.
"Wannan yaro da mugun hali yake" Ta faɗa tana taɓe baki ta shiga napep ɗin suka bi bayansa. Maƙociyar Sadiya kuwa da ta leƙo ganin Innar bata dawo ba, ganin Imran ya sa ta juya ta koma gidanta dan ita ko gaishe shi ta yi banza yake yi in ma yana amsawa to ita bata ji, sai ma ta daina gaishe da shi ganin rainin wayo da rainin hankalinsa dan ita tana mamakin yadda Sadiya take zaune da mutum kamar gunki.
Tun da suka fara bin Imran yake zabga uban gudu kamar zai tashi sama, da yake kuma unguwar kwana -kwana ta yi yawa ga ƙurunƙusai sai ya zama na Inna Azumi tana ta tangal-tangal a cikin napep ɗin saboda yadda ɗan sahun shi ma ke zuga gudu abinsa. Inna Azumi hannu ta sanya ta kama ƙarfen napep hagu da dama ta ƙanƙame dan ji take gabaɗaya kamar juyata ma ake yi. Idanu ta ɗaga ta sauke a kan me napep ɗin fa bai wuce shekaru sha tara zuwa ashirin ba, ga wani uwar suma a kan gashin ya yi cibir-cibir har da matajin kai a soke a jikin gashi, ga wani uban kiɗa da ke tashi a napep ɗin tamkar ma kiɗan jijjiga napep ɗin yake.
"Wai ni kai kwa yaro bahaushe ne?" Inna Azumi da bakinta baya shiru ta tambaya tana mai ƙuga maganar da ƙarfi yadda zai ji..
"Ke tsohuwa da wane yare na miki kama"?" Ya faɗa yana sakin wani uban fito da duk ƙaran kiɗan amma bai hana fitowar fiton ba.
"Ai tambayrka na yi dan na ga alama hausa bara ganka ba"
"Inyamuri ne ni, ko na miki ne, kina ciki"
"Amma wannan yaro an yi shegen yaro yanzu ka dubeni tsofe-tsofe da ni ka ce ina sonka? Amma gidanku ba manya"
"Sun ƙare" Ya bata amsar yana sanya hannu ya ciro matajin ya ɗan taza kan ya mayar ya soke.
"Baby kin yi shiru"
"Uwarka ce baby, wallahi tsakani na da kai Allah ya isa, ni Azumi na ga ta kaina.
"Ba dai shaƙa kika yi ba Hajiya, ban da ƙauyanci dan na ce baby ba wai yarinya nake nufi ba, wasan kaka da jika ne fa"
Ya kusa ƙarasowa gidansa ya hango wata ƙatuwar jakar bakko a ƙofar gidan, cikin mamaki yake kallon jakar da kuma neman dalilin ajiyeta a ƙofar gidansa.
Cikin sauri da azama ya ƙaraso har yana neman faɗuwa a machine ɗin dan ba ya ƙaunar abin da zai haɗa shi da kayan wasu, dan shi akwai tsare gidan ko maƙota iyakarsu gaisuwa tsakaninsa da su dama shi ba wani yawan magana yake ba bare zaman majalissa in har ba wurin aiki ya tafi ba to yana gida tare da iyalansa, sai ko idan ya je gaishe da Hajiyarsa. Yana faka machine ɗin ya ƙanƙance idanu yana kallon jakar, kallon da ya mata ma sai ya ji yana tsantsaninta dan sai ya ga duk ta yi wani ƙura, ko kuwa dan bai yarda da jakar bane oho ya ɗago kai yana son gano yadda aka yi jakar ta zo ƙofar gidansa sai ya ji wata murya tamkar daga sama an ce.
"Shikenan ma na huta ga Imirana nan" Shiru ya yi tare da runtse idanunsa da ƙarfi, jin an kirashi da sunan da ba ya so kwata-kwata, kuma ma duk duniya ya san babu mai kiransa da sunan nan sai kakar Sadiya wato Inna Azumi ita kaɗai ke kiransa, kuma ya shaida muryarta dan ko daga bacci ya tashi ba zai kasa shaida muryarta ba.
Shi ya rasa me yasa matar nan take son takurawa rayuwarsa, sam ba ya son wannan nuna ƙoƙon usulin da take nuna masa dan yana auren jikarta, shi ko ƴarta yake aure ba ya son takurawa amma ita ta kasa ganewa, sannan duk miskilancinsa na ƙin son magana da mutane sai da ya daure ya faɗa mata cewa Imran ake kiransa dan idan ta kirasahi da Imirana nan ji yake kamar ta kwaɗa masa gudum a kan sa.
"Ashe ma kana kusa har nake bin gidan maƙotanku ka ganni nan saukar yanzu tsal ɗin nan" Ta ƙara faɗa tana ƙarasowa wajensa ba tare da ta jira ya ce wani abu ba, cije gefen lips ɗinsa ya yi yana ji da a ce wani ne da ban ba tsohuwa ba yake damunsa kamar yadda tsohuwar nan ke damunsa da sai ya ɗau mummunan mataki.
"Eh" Kawai ya ce hakan ma dan ta kasa kunne ne ta gane me ya ce amma da gungune ya yi maganar.
"Allahu akbar Imirana har yanzu dai kana nan da wannan mugun halin naka, kai wane irin mutum ne da baka sakewa da mutane ku yi magana ma ta fatar baki kawai ni fa kakar ka ce ba sirikar ka ba" Ta faÉ—a tana kallon fuskarsa da ya haÉ—e ta murtuk kamar zai saki kuka.
"Sauri nake" Shi ne kawai abin da ya ce, shi ma dai da ƙunƙunen ya faɗa.
"Oh Allah na shiga aljanna na maƙale, yanzu baka ce min Inna ina wuni an zo lafiya ba sai ka zauna kana min magana kamar mai ciwon haƙori, ko kallon arziƙi na kasa samu daga wajenka"
Banza ya mata ya fara ƙoƙarin buɗe ƙofar gidan.
Inna Azumi kuwa baki ta taɓe, dan ta lura in ta ce za ta ga yadda take so to zuciyarta sai ta yi bindiga bata samu yadda take son ba, gwara ta lallaɓashi a rabu lafiya, bare ita da ta zo dandalar arziƙi.
"Sa'adiyyar ta sauka ne?" Ta faɗa tana kallonsa yana cire kwaɗo daga jikin ƙofar gidan.
Bai bata amsa ba a take ta tuna da katoɓarar da ta yu, dan dama Sa'adiyya take kiran Sadiya amma saboda kwainane irin nasa ya ce wai ta fiya ɓatawa mutane suna ganin baya iya faɗar Sadiya sai Sa'adiyya sai take cewa Halima saboda jarabar Imran ɗin dan duk ranar da ta zo gidansa haka zai yi ta mita a ƙunƙunen nan har dai ta ɗan canja sannan ta samu salama.
"Na ce Halimar bata sauka bane?" Ta gyara sunan dan ta matsu ta ji halin da jikarta ke ciki.
" Ta sauka" Ya faɗa a takaice yana tura ƙofar gidan ya shige ya bar Inna Azumi a tsaye baki sake, da ya shige ma sai da ya ɗan turo ƙofar.
"Yau na ga abin da ya isheni, a haka zan yi har kwana hamsin ɗin, ana wannan zaman doya da manjan, taɓɗi aikiwa duk abin amarya sai an sha manta wallahi ko me za ka yi sai na zaina ZAMAN WANKAN nan dan ban ga abin da zai sanya na fasa ba dan kana wannan fisfigar" Ta faɗa a ranta tana tura ƙofar ita ma ta shiga gidan tare da jan jakarta ta shigar da ita dakyar saboda nauyi, Imran da ya dawo domin ya ɗakkowa Sadiya zani saboda zannuwan sun yi kaɗan yana cikin sanya zanin a leda ya jiyo ƙaran jakar Inna Azumi tana janta ƙiiiii.
"Me yasa matar nan ta shigo min da ƙazamar jakarta gidana" Ya faɗa a ransa, ya yi sauri ya fito daga ɗakin ya dawo falo ya sanya hannu ya fusgi labule da ƙarfi ya fito daga ɗakin tare da rufo ƙofar dan ma kar ta yi gigin shigar masa da jakarta ɗaki dan ba ya jin zai iya bacci ma idan jakar tana ɗakin saboda ƙyanƙyami.
Baki sake Inna Azumi ke kallonsa har ya gama kulle falon, yana wani É—aÉ—É—aga kai kamar ya ga kashi ya ce.
"Asibiti zan koma" Sai da Inna Azumi ta saurara da kyau sannan ta gane me ya ce.
"Yo ni ma ina na ga ta zama, ai ba zama wai an É—aurawa karya zani, mu tafi sabitin in je in gan su dan can ma gidansu na fara zuwa a rufe, na zo nan É—in ma ashe dai basu dawo daga asibitin ba"
"Eh" Kawai ya ce dan shi kamar mai ciwon baki haka yake ba ya son magana ko Sadiya sai ita ta yi ta masa hira shi dai sai umm da um, um kawai ko da zai yi maganar ma to ba wata mai yawa ba sai dai kuma ranar da ya ga dama sai ya yi maganar amma ba sosai ba.
Yana fitowa ita ma ta fito ya rufe gidan, aikuwa sai ga wani mai napep zai wuce ya tsayar da shi ya ce ya É—auketa sai ya biyo bayansa.
"Wannan yaro da mugun hali yake" Ta faɗa tana taɓe baki ta shiga napep ɗin suka bi bayansa. Maƙociyar Sadiya kuwa da ta leƙo ganin Innar bata dawo ba, ganin Imran ya sa ta juya ta koma gidanta dan ita ko gaishe shi ta yi banza yake yi in ma yana amsawa to ita bata ji, sai ma ta daina gaishe da shi ganin rainin wayo da rainin hankalinsa dan ita tana mamakin yadda Sadiya take zaune da mutum kamar gunki.
Tun da suka fara bin Imran yake zabga uban gudu kamar zai tashi sama, da yake kuma unguwar kwana -kwana ta yi yawa ga ƙurunƙusai sai ya zama na Inna Azumi tana ta tangal-tangal a cikin napep ɗin saboda yadda ɗan sahun shi ma ke zuga gudu abinsa. Inna Azumi hannu ta sanya ta kama ƙarfen napep hagu da dama ta ƙanƙame dan ji take gabaɗaya kamar juyata ma ake yi. Idanu ta ɗaga ta sauke a kan me napep ɗin fa bai wuce shekaru sha tara zuwa ashirin ba, ga wani uwar suma a kan gashin ya yi cibir-cibir har da matajin kai a soke a jikin gashi, ga wani uban kiɗa da ke tashi a napep ɗin tamkar ma kiɗan jijjiga napep ɗin yake.
"Wai ni kai kwa yaro bahaushe ne?" Inna Azumi da bakinta baya shiru ta tambaya tana mai ƙuga maganar da ƙarfi yadda zai ji..
"Ke tsohuwa da wane yare na miki kama"?" Ya faɗa yana sakin wani uban fito da duk ƙaran kiɗan amma bai hana fitowar fiton ba.
"Ai tambayrka na yi dan na ga alama hausa bara ganka ba"
"Inyamuri ne ni, ko na miki ne, kina ciki"
"Amma wannan yaro an yi shegen yaro yanzu ka dubeni tsofe-tsofe da ni ka ce ina sonka? Amma gidanku ba manya"
"Sun ƙare" Ya bata amsar yana sanya hannu ya ciro matajin ya ɗan taza kan ya mayar ya soke.
"Baby kin yi shiru"
"Uwarka ce baby, wallahi tsakani na da kai Allah ya isa, ni Azumi na ga ta kaina.
"Ba dai shaƙa kika yi ba Hajiya, ban da ƙauyanci dan na ce baby ba wai yarinya nake nufi ba, wasan kaka da jika ne fa"