Sashe 7
Rayuwa Da Macijiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushin jin daɗi tayi tace. "Babu makawa wannan ita ce hanyar da zanbi domin barin wannan dajin. Batareda wani tunani bah ta nufi wajan kofar da sauri.
Babu zato taji kifiyoyi na fitowa ta koh ina. Da sauri ta kwanta ƙasa, yayinda gaban ta ya tsananta faɗuwa.
Cigaba da harbo kifyoyin🏹 aka yi babu kagautawa. Ganin abun bana ƙare wa bane ya sata miƙewa da sauri.
Da mugun gudu ta nufi kofar da take tunanin ita ce hanyar futa. Cikin sa'a ta isa baƙin kofan batare da ta bari koh da ɗaya daga cikin kifiyan ya cake ta ba.
Hajiyan zuciya ta shiga sauke wa. Saurin Daga kanta tayi tare da dora wa akan wannan kofan. Rubutu taga anyi a jiki wanda ita kanta ba tasan me aka rubuta bah.
Sannan wannan kofar ba za ta taɓa bude wa bah batare da anyi kalmomin bada izinin wucewa bah.
Riƙe kanta tayi alamin tana yin nazarin wani abu, da sauri ta ɗago sannan tace. "Maza buɗe".
Shiru taji, taga kofa bai buɗe bah, cikin daƙewa ta cigaba da jarraba sa'ar ta,amma ina,koh gizau kofar batayi bah.
Soma gajiya Dua tayi, yayinda take ganin cewa nan zata karashe rayuwar ta. Maganganun aljanun dazu ne ya fara i mata yawo a kwakwal wa.
"Halitta ɗaya ce a duniyar nan zata iya bin ta wannan kogin kuma wannan halittar itace sarauniyar macizai, idan har ke ɗin ce da gaske toh zaki bi wajan nan batare da wani abu na cutar wa ya tunkari inda kike bah".
Buɗe idanuwan ta tayi, sannan ta miƙar da hannun ta tare da ɗora wa akan kofar tace. "A matsayina na shugaba da kuma sarauniya na macizai da sauran halittun boye, ina bukatar wannan kofar ta buɗe yanzu kamar yadda na buƙata".
Cikin kankanin lokaci kofar ta fara girgiza, hatake shima wannan dajin ya soma girgiza, faɗuwa Dua tayi ƙasa yayinda ganyayya kin hannun ta suka soma zube wa. Saurin miƙewa tayi ta kara faɗin. "Idan har niɗin ce da gaske shugabar ka, ina so ka buɗe min hanya yanzu".
a hankali kofar ta fara wangale, daga karshe kofar ta buɗe gaba ɗaya.
Farin ciki ne gaba ɗaya ya bayyana kan fuskarta, cike da farin ciki ta sanya kafar ta na dama tare da shi cewa cikin kofar.
Shigar ta keda wuya kofar ta rufe kanta.
Dua bata ganta a koh ina bah sai a cikin fadar Mai gari. Miƙewa tayi da sauri ta fara kwallah kiran Inna wuro.
Ba zato bah tsammani suka jiyo muryar ta, waigawa suka yi da sauri, hatake suka ɗora idanuwan su akan ta tana riƙe da magunguna.
A lokacin bah Dua suka gani bah, gobe mai haske suka gani a tattare da ita.
Da gudu ta nufi wajan Inna wuro tare da rungume ta sannan ta ɗago kai ta kalle ta tace. "Dama na faɗa muku cewa zan shiga kuma na fito lafiya batareea wani abu na cutar wa ya tunkari inda nake bah, yanzu dai kun tabbatar da cewa zan iya kare kaina batare da taimakon kowa bah koh ".
Kallon ta Mai gari yayi yace. "Babu wani ɗan adam da ya taɓa shiga wannan dajin ya fito a raye bah, amma ke kin shiga kuma kin tsinko magunguna sannan kuma kin fito bstareda kinji koda kwarzane bah ".
"Tabbas akwai wani ɓoyayyen al'amari game da ke, yanzu na yarda keɗin jaruma ce, kije na baki dama kije birni domin yin karatu kamar yadda kika bukata".
Kuma sannan zamu haɗa kuɗi baƙi ɗaya mu biya miki kuɗin da zaki je birni. Domin a yau ɗin nan kin sanya fuskar kowa murmushi, sannan ki mamaye zuciyoyin mu da farin ciki".
Maza kije ki shirya kayan ki domin yau ɗin nan zaki je birni karatu. Tsalle Dua ta daka tare da faɗin na gode sosai Mai gari, yanzu zanje na haɗa kayana, sai wani yayi min jagora ya kaini baƙin hanyar fita daga wannan ƙauyen".
Tana kaiwa nan ta shige cikin gidan su.
*KANO STATE BIRNIN TARAYYA*
Ƙerarriyar mota na hango kirar Mercedes Benz ta shiga makarantar Northwest university da gudu, inda gaba ɗaya dalibai idonsu akan wannan motar. Tabbas sun san da cewa mutum ɗaya ne yake gudu kamar ana gasan tseren mota a wannan makaranta. Gaba ɗaya ya zamana ya cika makarantar da ƙura.
Tsayuwa motar tayi . Lokaci ɗaya naga an buɗe kofan motan . Ganin wanda ke cikin motar yasa gaba ɗaya dalibai Jan jini jikin su. Sanin cewa tabbas president ɗin ɗalibai na makaranta ne wato Ahmad Yasir Bello, yasa gaba ɗaya nufan inda yake sannan suka fara kwasan gaisuwa.
Kafa naga an fito dashi, wanda ke sanye da canvas blue, daga bisani ya fito daga cikin motar. dukkan yabo su tabbata ga ubangiji Wanda yayi wannan kyakyyawar halitar. Fari ne amma farin sa irin yan black Americans ne. Fuskar sa a murtuke kamar bai taɓa dariya ba.
Yayinda yake ɗauke da madaidaicin hanci da baki wanda ke pink colour.
Sanye yake da jeans din wando blue sai t shirt fari da facing cap blue. Wannan kaya ba karamin kyau yayi wa Ahmard bah, wanda ɗalibai ke masa lakabi da A.y the school president.
Cikin lion voice ɗin sa yace. "Maza kowa ya ɓace daga nan, sannan bana son naga kowa ya wuce wani guri in bah department ɗin sa bah, understood?".
Yes gaba ɗaya suka furta,cikin kankanin lokaci kowa ya nufi class ɗinsa, duda cewar ba kowane class ne suke da lecture yanzu bah, amma saida kowa ya shiga sabo da sanin halin Ahmard baya raga wa kowa.
Wani mature guy na hango yana nufo inda Ahmad yaƙe. Karasa wa inda Ahmad ke tsaye yake tare da sakar masa murmushi yace. "Our president, kana aiki da kyau, chab wannan da kana shigowa makaranta jikin kowa zai fara kakkarwa kamar sunga mala'ikan mutuwa".
"Gaskiya ya kama ta ka rage wannan abu da kake yi gaba ɗaya abin da kake yi is not fair".
Haɗe rai Ahmad ya ƙara yi tare da kara murtuke fuska sannan yace dashi. " waya baka izinin fitowa daga class Abdul?.
Kallon sa Abdul yayi, lokaci ɗaya ya ƙyalkyale da dariya, saida yayi mai isarsa sannan yace. "Nima da nake abokin ka baka barni bah, lallai kamm Ahmad wuyan ka ya isa yanka, amma ina fatan wata rana wata ta saukar maka da wannnan jiki dakai da kuma taurin kai.
Murmushi gefen baki Ahmad yayi yace. "Babu ita, kuma ba zata taɓa bayyana bah, banga wacce ta isa ta saukar min da izza ta bah".
Kallon sa Abdul yayi sannan yace. "Idan kuwa Allah ya bayyana ta fah?
Maida kallon sa kan Abdul Ahmad yayi sannan yace. "Duk ranar da Allah ya bayyana ta, sannan kuma naja taja magana ta ba tare da tsoro kan fuskarta bah, ni kuma nayi maka alƙawarin cewa daga ranar, duk abinda kace nayi ni kuma saina yi. Wannan alkawari na ne ".
*TOH FAN'S MEYE RA'AYIN KU GAME DA AHMARD, SHIN DUA ZATA ZO BIRNIN NE KOH A'a. TABBAS AKWAI KALLO GABA*.
COMMENTS & SHARE PLEASE 🙏🙏🙏
ALKALAMIN ✍️
A'ISHA M.B💞💞💞
(Zinariyar🪙 Jajirtattu)
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
🌹BISSMILLAHI RAHMANI RAHIM🌹
*🌸RAYUWA DA MACIJIYA* 🐍 🐍🐍
*PAID BOOK ₦400 complt*
kacal babu tsada
*9043687746 Hassana Aliyu Opay bank*
*Evidence of payment*
09130398321
FREE PAGE 1️⃣0️⃣➡️1️⃣1️⃣
WRITTEN & DIRECTED ✍️ BY A'ISHA M.B💞
(Zinariyar 🪙 Jajirtattu)
*_______________________________*
"Uhmm Ahmard kenen sarkin rigima, toh shikenen ni kuma nace maka wannan ranar saita zo, kaje ka rubuta zaka ce na faɗa maka".
"Ni abin da ma yasa kaga na fito daga class bah komai ba ne, illa kiran ka da Uncle Sharif ya ce nayi".
"Mene ne mutumin nan yaƙe buƙata ne? Na faɗa masa cewa bana son takura a rayuwata, yanzu ina zuwa gaba ɗaya zai cikani da warin baki".
Dariya Abdul yayi sannan yace dashi. "wallahi Ahmad kana da wuyar sha'ani, yanzu malamin naka kake wa wannan cin fuskar? Gaskiya kana buƙatar a saita ka ".
Fuskar Ahmad ne ya sauya daga walwala zuwa ɓacin rai, sannan ya kalli Abdul yace. "Go back to your class Abdul". Ya faɗa tare da kauda kai gefe.
"Shike nen ai zan tafi, ni na isa naja da maganar ka, kaga tafiya ta ma". Ya karashe maganar tare da barin harabar wajan.
Ganin akan da Ahmad yayi yasa shima ya nufi office din Uncle Sharif.
Ɓangaren Du'a kuwa, saida ta shirya tsaff ta haɗa gaba ɗaya kayan ta masu kyau sannan ta saka su a cikin jakar ta na saƙa, ta cinciɓe ta sannan ta fito da ita harabar ƙauyen.
Ɗaukar wayar sa Mai gari yayi tare da kiran ƙanwar sa Sakina, sannan yayi mata bayanin zuwan da Du'a zata yi gidan ta.
"Allah ya kawo ta lafiya kawai Sakina ta faɗa".
Sallama Mai gari yayi mata daga bisani ya katse wayar. Kallon Du'a yayi sannan ya mai da kallon sa ga maza biyu dake tsaye yace dasu. "Kune nake so ku raka Du'a har gidan Sakina sabo da kune ƙaƙƙarfan maza a wannan ƙauye, kuma inada tabbacin za ku ƙare ta ".
"In sha Allahu mah zamu kare ta duda cewar Allah ne mai karewa, amma muma zamu yi iya bakin ƙoƙarin mu wajan ganin babu wani abu na cutar wa ya nufi inda ta ke bah". Cewar ɗaya daga cikin mazan.
Miƙa wa Du'a kuɗaɗe dake hannun sa Mai gari yayi, Du'a ta karɓa, tana mai cewa. "Ina matuƙar godiya da bani damar zuwa birni, kuma nayi muku alƙawari bazan taɓa baku kunya bah, baza ku taɓa dana sanin bari na da kuka yi naje birni bah".
"In sha Allahu abin da ya kaini chan shi zan yi, kuma na gode da kulawar ku a gare ni ".
Ta karashe maganar tare da nufa inda Inna wuro ta ke, durkusawa tayi sannan tace."inna ina son ki saka min albarka, sannan kiyi min addu'a Allah ya bani abin da naje nema ".
Murmushi Inna wuro tayi tace. "Allah ya yi miki albarka ƴata, ya baki nasaran cim ma burin ki na alhkairy, yasa ki gane duk abin da aka koyar dake ".
Babu zato taji kifiyoyi na fitowa ta koh ina. Da sauri ta kwanta ƙasa, yayinda gaban ta ya tsananta faɗuwa.
Cigaba da harbo kifyoyin🏹 aka yi babu kagautawa. Ganin abun bana ƙare wa bane ya sata miƙewa da sauri.
Da mugun gudu ta nufi kofar da take tunanin ita ce hanyar futa. Cikin sa'a ta isa baƙin kofan batare da ta bari koh da ɗaya daga cikin kifiyan ya cake ta ba.
Hajiyan zuciya ta shiga sauke wa. Saurin Daga kanta tayi tare da dora wa akan wannan kofan. Rubutu taga anyi a jiki wanda ita kanta ba tasan me aka rubuta bah.
Sannan wannan kofar ba za ta taɓa bude wa bah batare da anyi kalmomin bada izinin wucewa bah.
Riƙe kanta tayi alamin tana yin nazarin wani abu, da sauri ta ɗago sannan tace. "Maza buɗe".
Shiru taji, taga kofa bai buɗe bah, cikin daƙewa ta cigaba da jarraba sa'ar ta,amma ina,koh gizau kofar batayi bah.
Soma gajiya Dua tayi, yayinda take ganin cewa nan zata karashe rayuwar ta. Maganganun aljanun dazu ne ya fara i mata yawo a kwakwal wa.
"Halitta ɗaya ce a duniyar nan zata iya bin ta wannan kogin kuma wannan halittar itace sarauniyar macizai, idan har ke ɗin ce da gaske toh zaki bi wajan nan batare da wani abu na cutar wa ya tunkari inda kike bah".
Buɗe idanuwan ta tayi, sannan ta miƙar da hannun ta tare da ɗora wa akan kofar tace. "A matsayina na shugaba da kuma sarauniya na macizai da sauran halittun boye, ina bukatar wannan kofar ta buɗe yanzu kamar yadda na buƙata".
Cikin kankanin lokaci kofar ta fara girgiza, hatake shima wannan dajin ya soma girgiza, faɗuwa Dua tayi ƙasa yayinda ganyayya kin hannun ta suka soma zube wa. Saurin miƙewa tayi ta kara faɗin. "Idan har niɗin ce da gaske shugabar ka, ina so ka buɗe min hanya yanzu".
a hankali kofar ta fara wangale, daga karshe kofar ta buɗe gaba ɗaya.
Farin ciki ne gaba ɗaya ya bayyana kan fuskarta, cike da farin ciki ta sanya kafar ta na dama tare da shi cewa cikin kofar.
Shigar ta keda wuya kofar ta rufe kanta.
Dua bata ganta a koh ina bah sai a cikin fadar Mai gari. Miƙewa tayi da sauri ta fara kwallah kiran Inna wuro.
Ba zato bah tsammani suka jiyo muryar ta, waigawa suka yi da sauri, hatake suka ɗora idanuwan su akan ta tana riƙe da magunguna.
A lokacin bah Dua suka gani bah, gobe mai haske suka gani a tattare da ita.
Da gudu ta nufi wajan Inna wuro tare da rungume ta sannan ta ɗago kai ta kalle ta tace. "Dama na faɗa muku cewa zan shiga kuma na fito lafiya batareea wani abu na cutar wa ya tunkari inda nake bah, yanzu dai kun tabbatar da cewa zan iya kare kaina batare da taimakon kowa bah koh ".
Kallon ta Mai gari yayi yace. "Babu wani ɗan adam da ya taɓa shiga wannan dajin ya fito a raye bah, amma ke kin shiga kuma kin tsinko magunguna sannan kuma kin fito bstareda kinji koda kwarzane bah ".
"Tabbas akwai wani ɓoyayyen al'amari game da ke, yanzu na yarda keɗin jaruma ce, kije na baki dama kije birni domin yin karatu kamar yadda kika bukata".
Kuma sannan zamu haɗa kuɗi baƙi ɗaya mu biya miki kuɗin da zaki je birni. Domin a yau ɗin nan kin sanya fuskar kowa murmushi, sannan ki mamaye zuciyoyin mu da farin ciki".
Maza kije ki shirya kayan ki domin yau ɗin nan zaki je birni karatu. Tsalle Dua ta daka tare da faɗin na gode sosai Mai gari, yanzu zanje na haɗa kayana, sai wani yayi min jagora ya kaini baƙin hanyar fita daga wannan ƙauyen".
Tana kaiwa nan ta shige cikin gidan su.
*KANO STATE BIRNIN TARAYYA*
Ƙerarriyar mota na hango kirar Mercedes Benz ta shiga makarantar Northwest university da gudu, inda gaba ɗaya dalibai idonsu akan wannan motar. Tabbas sun san da cewa mutum ɗaya ne yake gudu kamar ana gasan tseren mota a wannan makaranta. Gaba ɗaya ya zamana ya cika makarantar da ƙura.
Tsayuwa motar tayi . Lokaci ɗaya naga an buɗe kofan motan . Ganin wanda ke cikin motar yasa gaba ɗaya dalibai Jan jini jikin su. Sanin cewa tabbas president ɗin ɗalibai na makaranta ne wato Ahmad Yasir Bello, yasa gaba ɗaya nufan inda yake sannan suka fara kwasan gaisuwa.
Kafa naga an fito dashi, wanda ke sanye da canvas blue, daga bisani ya fito daga cikin motar. dukkan yabo su tabbata ga ubangiji Wanda yayi wannan kyakyyawar halitar. Fari ne amma farin sa irin yan black Americans ne. Fuskar sa a murtuke kamar bai taɓa dariya ba.
Yayinda yake ɗauke da madaidaicin hanci da baki wanda ke pink colour.
Sanye yake da jeans din wando blue sai t shirt fari da facing cap blue. Wannan kaya ba karamin kyau yayi wa Ahmard bah, wanda ɗalibai ke masa lakabi da A.y the school president.
Cikin lion voice ɗin sa yace. "Maza kowa ya ɓace daga nan, sannan bana son naga kowa ya wuce wani guri in bah department ɗin sa bah, understood?".
Yes gaba ɗaya suka furta,cikin kankanin lokaci kowa ya nufi class ɗinsa, duda cewar ba kowane class ne suke da lecture yanzu bah, amma saida kowa ya shiga sabo da sanin halin Ahmard baya raga wa kowa.
Wani mature guy na hango yana nufo inda Ahmad yaƙe. Karasa wa inda Ahmad ke tsaye yake tare da sakar masa murmushi yace. "Our president, kana aiki da kyau, chab wannan da kana shigowa makaranta jikin kowa zai fara kakkarwa kamar sunga mala'ikan mutuwa".
"Gaskiya ya kama ta ka rage wannan abu da kake yi gaba ɗaya abin da kake yi is not fair".
Haɗe rai Ahmad ya ƙara yi tare da kara murtuke fuska sannan yace dashi. " waya baka izinin fitowa daga class Abdul?.
Kallon sa Abdul yayi, lokaci ɗaya ya ƙyalkyale da dariya, saida yayi mai isarsa sannan yace. "Nima da nake abokin ka baka barni bah, lallai kamm Ahmad wuyan ka ya isa yanka, amma ina fatan wata rana wata ta saukar maka da wannnan jiki dakai da kuma taurin kai.
Murmushi gefen baki Ahmad yayi yace. "Babu ita, kuma ba zata taɓa bayyana bah, banga wacce ta isa ta saukar min da izza ta bah".
Kallon sa Abdul yayi sannan yace. "Idan kuwa Allah ya bayyana ta fah?
Maida kallon sa kan Abdul Ahmad yayi sannan yace. "Duk ranar da Allah ya bayyana ta, sannan kuma naja taja magana ta ba tare da tsoro kan fuskarta bah, ni kuma nayi maka alƙawarin cewa daga ranar, duk abinda kace nayi ni kuma saina yi. Wannan alkawari na ne ".
*TOH FAN'S MEYE RA'AYIN KU GAME DA AHMARD, SHIN DUA ZATA ZO BIRNIN NE KOH A'a. TABBAS AKWAI KALLO GABA*.
COMMENTS & SHARE PLEASE 🙏🙏🙏
ALKALAMIN ✍️
A'ISHA M.B💞💞💞
(Zinariyar🪙 Jajirtattu)
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
🌹BISSMILLAHI RAHMANI RAHIM🌹
*🌸RAYUWA DA MACIJIYA* 🐍 🐍🐍
*PAID BOOK ₦400 complt*
kacal babu tsada
*9043687746 Hassana Aliyu Opay bank*
*Evidence of payment*
09130398321
FREE PAGE 1️⃣0️⃣➡️1️⃣1️⃣
WRITTEN & DIRECTED ✍️ BY A'ISHA M.B💞
(Zinariyar 🪙 Jajirtattu)
*_______________________________*
"Uhmm Ahmard kenen sarkin rigima, toh shikenen ni kuma nace maka wannan ranar saita zo, kaje ka rubuta zaka ce na faɗa maka".
"Ni abin da ma yasa kaga na fito daga class bah komai ba ne, illa kiran ka da Uncle Sharif ya ce nayi".
"Mene ne mutumin nan yaƙe buƙata ne? Na faɗa masa cewa bana son takura a rayuwata, yanzu ina zuwa gaba ɗaya zai cikani da warin baki".
Dariya Abdul yayi sannan yace dashi. "wallahi Ahmad kana da wuyar sha'ani, yanzu malamin naka kake wa wannan cin fuskar? Gaskiya kana buƙatar a saita ka ".
Fuskar Ahmad ne ya sauya daga walwala zuwa ɓacin rai, sannan ya kalli Abdul yace. "Go back to your class Abdul". Ya faɗa tare da kauda kai gefe.
"Shike nen ai zan tafi, ni na isa naja da maganar ka, kaga tafiya ta ma". Ya karashe maganar tare da barin harabar wajan.
Ganin akan da Ahmad yayi yasa shima ya nufi office din Uncle Sharif.
Ɓangaren Du'a kuwa, saida ta shirya tsaff ta haɗa gaba ɗaya kayan ta masu kyau sannan ta saka su a cikin jakar ta na saƙa, ta cinciɓe ta sannan ta fito da ita harabar ƙauyen.
Ɗaukar wayar sa Mai gari yayi tare da kiran ƙanwar sa Sakina, sannan yayi mata bayanin zuwan da Du'a zata yi gidan ta.
"Allah ya kawo ta lafiya kawai Sakina ta faɗa".
Sallama Mai gari yayi mata daga bisani ya katse wayar. Kallon Du'a yayi sannan ya mai da kallon sa ga maza biyu dake tsaye yace dasu. "Kune nake so ku raka Du'a har gidan Sakina sabo da kune ƙaƙƙarfan maza a wannan ƙauye, kuma inada tabbacin za ku ƙare ta ".
"In sha Allahu mah zamu kare ta duda cewar Allah ne mai karewa, amma muma zamu yi iya bakin ƙoƙarin mu wajan ganin babu wani abu na cutar wa ya nufi inda ta ke bah". Cewar ɗaya daga cikin mazan.
Miƙa wa Du'a kuɗaɗe dake hannun sa Mai gari yayi, Du'a ta karɓa, tana mai cewa. "Ina matuƙar godiya da bani damar zuwa birni, kuma nayi muku alƙawari bazan taɓa baku kunya bah, baza ku taɓa dana sanin bari na da kuka yi naje birni bah".
"In sha Allahu abin da ya kaini chan shi zan yi, kuma na gode da kulawar ku a gare ni ".
Ta karashe maganar tare da nufa inda Inna wuro ta ke, durkusawa tayi sannan tace."inna ina son ki saka min albarka, sannan kiyi min addu'a Allah ya bani abin da naje nema ".
Murmushi Inna wuro tayi tace. "Allah ya yi miki albarka ƴata, ya baki nasaran cim ma burin ki na alhkairy, yasa ki gane duk abin da aka koyar dake ".