Sashe 14
Rayuwa Da Macijiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ta je gaban wannan halittar sannan ta tsuguna tare da fuskantar sa. Kallon sa ta yi ido cikin ido a ta ke ta yi wani irin muguwar zabura ganin yadda sufar sa ya ke da matukar munin gaske.
Cikin daƙe wa ta kara kallon sa a karo na biyu sannan ta ce. "Wane ne kai? Me ya sa ku ka kawo ni cikin wannan baƙar dajin?"
Amsa ƙaramin halittar ya bata da cewa. "Mun kawo ki ne sabo da ki na da halaƙa da wannan dajin. ke ɗin jinin mu ce kuma kece sarauniyar wannan dajin gaba ɗaya, me ya sa ba za ki dawo ki ci gaba da mulkar dajin ki kamar yadda ki ka saba yi a da bah? bai kama ta a ce ki ci gaba da kasancewa cikin mutane wanda ke kan ki kin san da cewa ke bah jinsin su bace".
"Har yanzu ke mu ke jira don ga kujerar ki na sarauta chan yana jira ki dawo gare sa.
Koda yaushe wannan kujerar ku ka ta ke yi. dan aka yanzu ba ki da wani zabi da ya wuce ki dawo duniyar ki, domin shi ne zai zamo alhkairy a ga re ki".
A fusa ce Du'a ta miƙe tsaye sannan ta kalle shi cikin ɓaccin rai ta ce. "Karya ka ke makaryacin banza kawai, Ni ɗin mutum ce ba macijiya bah, har kai waye da za ka ce Ni ba mutum bace"
"Idan har ni ɗin macijiya ce da gaske toh me ya sa bana sauya kammani? Na ga ji da jin ire-iren waɗan nan tatsuniyoyin da ku ke yawan faɗa, wannan ya zamo na farko kuma na karshe da za ku ƙara cewa ni macijiya ce".
"Kuma shin kana da hujja akan abin da ka ke faɗa?".
Amsa aljanin ya bata da cewa. "Ba za ki san da cewa ke macijiya bace sai lokacin bayyanar baiwar ki ya yi tukun nan, kuma ba za ki ji komai a baki na bah, aka zalika hujja ma ba za ki ji daga waje na bah, amma ita asalin mahaifyar ki ta san ko mai, ita za ki je ki tambaya domin ita keda cikakkun bayanai ga me da rayuwarki".
A fusa ce Du'a ta shaƙe masa wuya tana mai cewa. "Makaryancin banza wato kana so ka shiga tsakanina da mahafiyata koh, yau bah gobe bah zan ga bayanka.
Babu zato ta ga macizai sun fara hawa jikin ta, a ta ke ta saki wani irin razannaniyar ƙara!.
Ihuuu! Maryam ta yi ganin yadda Du'a ta maƙure ta ta re da shaƙe mata wuya.
Zabura gaba ɗaya ƴan ɗaƙin suka yi, ganin yadda Du'a ta shaƙe wuyan Maryam tana surutai.
Babu ɓata lokaci kowannen su ya kai wa Maryam ɗauki. A firgice Du'a ta farka daga mafarkin da ta ke.
Da sauri ta cire hannunta daga wuyan Maryam ganin yadda ta shaƙe ta. Tari Maryam ta soma yi babu sassauci.
Ganin akan da Du'a da ƴan ɗaƙin su ka yi ya sa hankali su ya ƙara tashi!.
Da sauri Du'a ta tashi tare da nufan inda ruwa ya ke. ɗebo ruwan ta yi a cikin kofi sannan ta nufi kan Maryam da shi.
Ɗaya daga cikin matan ɗaƙin wato Khadija ce ta wafce kofin da ke hannun Du'a sannan ta yi magana cikin ɓacin rai ta ce. "Baki da hankali za ki shaƙe mata wuya? sabo da me za ki aika ta mata aka? Ki dubi yadda ki ka sa ta gigice duk sabo da ke".
"Naga alamu tun da ki ka shi go cikin makarantar nan abubuwa mara sa kyau suke faruwa. Farkon shigowa ki makarantar nan wata ta tayar da aljanu, kin ce bakya iya kwana cikin duhu sabo da kina jin tsoro, aka muka haƙura muke kwana cikin haske, yanzu kuma kin zo kin maƙure ta kina son ki kashe ta Koh? Nan gaba ma abin ba'a iya nan zai tsaya bah harda mu za ki haɗa".
Girgiza kai Du'a ta yi ta ce. "Ni samm bada sane na aikata mata akan bah, mafarki na ke yi shi ya sa ban san na shaƙe mata wuya bah".
"Ka ji munafuka algunguma, wato mafarki ki ke shi ne aka ce ki shaƙe mata wuya koh?". Cewar habiba. Sannan ta kara da cewa. "Wallahi babu tantama yarinyar nan mayya ce, in bah mayya bah mene na shaƙe mata wuya wato so ki ke ki zuƙi jininta Koh? Toh ki sa ni jinin mu ɗaci ne da shi babu wata mayya da ta isa ta ce za ta sha mana jini".
Girgiza kai Du'a ta fara yi ta ce. "Na rantse ni ba mayya bace kuma ni bana shan jini, kawai kun yi min gurguwar fahimta ne shi ya sa, amma ni samm bah mayya bace".
Ture ta khadija ta yi ta ce. "Dalla ware dangin mayu kawai mai fara ƙafa, daga yau kada mu sa ke ganin kin kusanci inda Maryam ta ke, in kuma ba aka bah, sai kin gane kuranki.
Tana kaiwa nan ta bangaje Du'a. A ta ke Du'a ta faɗi a wajan a yayin da hawaye suka fara zarya a kan ƙun cin ta. Da sauri ta ta shi tare da yin hanyar waje da gudu.
Gudu ta ke yi babu ƙagautawa sai da ta yi tafiya mai nisan gaske ba tare da tana ganin gaban ta bah, bakin bishiya ta samu ta zauna sannan ta fara ku ka.
Ku ka ta ke tamkar ranta zai futa. Ɗago idanuwanta ta yi wanda su ka yi jajir ta ce.
"Me ya sa akan ta ke faruwa dani? Mene ne tsakani na da macizai, me ya sa na ke irin waɗan nan munanan mafarkan? Shin ko dai da gaske ina da halaƙa da macizai?".
"Me ya sa ma banyi zama na a kauye bah? Da nasani ban zo birni bah na yi zama na a ƙauye domin nafi samun farin ciki a chan".
Miƙe wa tsaye ta yi tare da share hawayen ta ta ce.
"Ni wace ce? Me ya sa nake iya mu'amala da macizai bayan kuma ni ɗin mutum ce? Tabbas maganar su khadija gaskiya ne. kenen da gaske ni mayya ce? me ya sa zan kasance mayya bayan a dangi na babu mayu, toh kodai mamata mayya ce?".
Ji ta yi gaba ɗaya ku kan tsuntsaye ya gauraye wajan yayin da aka fara iska mai ƙarfi wanda ya ke haɗe da guguwa. a ta ke ta fara kalle-kalle, tare da juya wa.
Juyawar ta ke da wuya ta ga wani jibgegen baƙi maciji wanda ya zalalo da harshen sa wanda ke a tsage gida uku.
Zaro ido ta yi waje sannan ta sa ki wani irin ihuu da sauri ta fara ja da baya-baya, sannan ta fara ƙoƙarin guduwa, kafin ta yi wani yunkuri, macijin ya nannaɗe ta tare da ɗaga ta sama.
Ƙoƙarin kwace kan ta ta ke amma akan ya cutura. Rintse idanuwan ta ta yi don ta gama sallame wa cewa yau ne ranar mutuwar ta. Jin shiru babu abin da ya same ta, ya sa ta buɗe idanuwanta a hankali tare da ɗorawa akan na macijin.
Sauke ta macijin ya yi sannan ya shafa gashin kan ta da jelar sa na macijin daga bisani ya yi tafiyar sa.
Baki sa ke Du'a ta bi macijin da kallo sai da ta tabbatar idanuwanta sun daina ganin sa sannan ta ce. "Shi kuma wannan macijin daga ina ya fito? Me ya sa kuma zai zo waje na? Sannan fuskarsa ya nuna shiɗin ba ya da cutarwa".
Babu zato ta ji an dafa mata kafaɗa. A firgice ta juya da sauri ta ɗora idanuwanta akan na ta.
COMMENTS & SHARE PLS 🙏 🙏 🙏
ALKALAMIN ✍️
A'ISHA M.B💞💞💞
(Zinariyar🧝♀️ Jajirtattu)
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/D80k1puBPBn6uJhojKKhK5
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
🌹BISSMILLAHI RAHMANI RAHIM🌹
*🌸RAYUWA DA MACIJIYA* 🐍 🐍🐍
*PAID BOOK ₦400 complt*
kacal babu tsada
*9043687746 Hassana Aliyu Opay bank*
*Evidence of payment*
09130398321
*DA nayi niyar bar muku free page a aka, amma insha Allah zan kai muku shi twenty free page 🙏🙏🙏*
FREE PAGE ️1️⃣4️⃣➡️1️⃣5️⃣
WRITTEN & DIRECTED ✍️ BY A'ISHA M.B💞
(Zinariyar 🪙 Jajirtattu)
*_______________________________*
Rass gabanta ya faɗi! Yayin da jiri mai karfi ya fara ɗibanta, ta saki wani iriyar razannaniyar ƙara!. Da sauri ta fara ja da baya-baya sakamakon harba da ta yi da wata mai kama da ita sakk.
Riƙe kanta ta yi sannan ta nuna ta da ɗan yatsa a tsorace ta ce. "Wace ce ke? Me ya sa ki ke matuƙar kama da ni? Dan Allah na roƙe ki kada ki cutar da ni".
Murmushi aljanar ta yi sannan ta ce. "Ni bah cutar da ke na zo yi bah, ai idan na kwatanta taɓa lafiyar ki ni ce zan mutu bake bah. Dan aka ki tsaya ki saurari abin da zan faɗa miki". Ta faɗa tana nufar inda Du'a ta ke.
"Kada ki matso kusa da ni, bana so ki rabu dani dan Allah kada ki cutar da ni". Cewar Du'a.
Girgiza kai aljanar ta yi ta ce. "Na faɗa miki bah cutar da ke zan yi bah, ina so ne na sanar miki da wata muhimmiyar magana wacce za ta sa ki iya kare kanki a Koh ina, wanda koh mutum koh aljan bai isa ya tunkari inda ki ke da mugun nufi bah".
Kuka Du'a ta soma yi sannan ta ce. Yayin da hadari ya tashi aka fara yayyafi.
"Ni bana so, ki rabu da ni dan Allah". Ta ƙarashe maganar tare da juya wa da niyar tafiya. Babu zato taji ta yi tuntuɓe da dutse.
Luuu ta tafi tare da faɗuwa a kasan wajan. Jin takun takalmin mutun yasa aljanar ta ɓace daga farfajiyan wajan.
Karasawa wajan Maryam ta yi tare da kwallah kiran sunan Du'a. Jin shiru da ta yi ya sa hankalin ta ya yi matuƙar tashi. Da sauri ta fara waige-waige koh Allah zai sa ta ci karo da Du'a.
Cikin daƙe wa ta kara kallon sa a karo na biyu sannan ta ce. "Wane ne kai? Me ya sa ku ka kawo ni cikin wannan baƙar dajin?"
Amsa ƙaramin halittar ya bata da cewa. "Mun kawo ki ne sabo da ki na da halaƙa da wannan dajin. ke ɗin jinin mu ce kuma kece sarauniyar wannan dajin gaba ɗaya, me ya sa ba za ki dawo ki ci gaba da mulkar dajin ki kamar yadda ki ka saba yi a da bah? bai kama ta a ce ki ci gaba da kasancewa cikin mutane wanda ke kan ki kin san da cewa ke bah jinsin su bace".
"Har yanzu ke mu ke jira don ga kujerar ki na sarauta chan yana jira ki dawo gare sa.
Koda yaushe wannan kujerar ku ka ta ke yi. dan aka yanzu ba ki da wani zabi da ya wuce ki dawo duniyar ki, domin shi ne zai zamo alhkairy a ga re ki".
A fusa ce Du'a ta miƙe tsaye sannan ta kalle shi cikin ɓaccin rai ta ce. "Karya ka ke makaryacin banza kawai, Ni ɗin mutum ce ba macijiya bah, har kai waye da za ka ce Ni ba mutum bace"
"Idan har ni ɗin macijiya ce da gaske toh me ya sa bana sauya kammani? Na ga ji da jin ire-iren waɗan nan tatsuniyoyin da ku ke yawan faɗa, wannan ya zamo na farko kuma na karshe da za ku ƙara cewa ni macijiya ce".
"Kuma shin kana da hujja akan abin da ka ke faɗa?".
Amsa aljanin ya bata da cewa. "Ba za ki san da cewa ke macijiya bace sai lokacin bayyanar baiwar ki ya yi tukun nan, kuma ba za ki ji komai a baki na bah, aka zalika hujja ma ba za ki ji daga waje na bah, amma ita asalin mahaifyar ki ta san ko mai, ita za ki je ki tambaya domin ita keda cikakkun bayanai ga me da rayuwarki".
A fusa ce Du'a ta shaƙe masa wuya tana mai cewa. "Makaryancin banza wato kana so ka shiga tsakanina da mahafiyata koh, yau bah gobe bah zan ga bayanka.
Babu zato ta ga macizai sun fara hawa jikin ta, a ta ke ta saki wani irin razannaniyar ƙara!.
Ihuuu! Maryam ta yi ganin yadda Du'a ta maƙure ta ta re da shaƙe mata wuya.
Zabura gaba ɗaya ƴan ɗaƙin suka yi, ganin yadda Du'a ta shaƙe wuyan Maryam tana surutai.
Babu ɓata lokaci kowannen su ya kai wa Maryam ɗauki. A firgice Du'a ta farka daga mafarkin da ta ke.
Da sauri ta cire hannunta daga wuyan Maryam ganin yadda ta shaƙe ta. Tari Maryam ta soma yi babu sassauci.
Ganin akan da Du'a da ƴan ɗaƙin su ka yi ya sa hankali su ya ƙara tashi!.
Da sauri Du'a ta tashi tare da nufan inda ruwa ya ke. ɗebo ruwan ta yi a cikin kofi sannan ta nufi kan Maryam da shi.
Ɗaya daga cikin matan ɗaƙin wato Khadija ce ta wafce kofin da ke hannun Du'a sannan ta yi magana cikin ɓacin rai ta ce. "Baki da hankali za ki shaƙe mata wuya? sabo da me za ki aika ta mata aka? Ki dubi yadda ki ka sa ta gigice duk sabo da ke".
"Naga alamu tun da ki ka shi go cikin makarantar nan abubuwa mara sa kyau suke faruwa. Farkon shigowa ki makarantar nan wata ta tayar da aljanu, kin ce bakya iya kwana cikin duhu sabo da kina jin tsoro, aka muka haƙura muke kwana cikin haske, yanzu kuma kin zo kin maƙure ta kina son ki kashe ta Koh? Nan gaba ma abin ba'a iya nan zai tsaya bah harda mu za ki haɗa".
Girgiza kai Du'a ta yi ta ce. "Ni samm bada sane na aikata mata akan bah, mafarki na ke yi shi ya sa ban san na shaƙe mata wuya bah".
"Ka ji munafuka algunguma, wato mafarki ki ke shi ne aka ce ki shaƙe mata wuya koh?". Cewar habiba. Sannan ta kara da cewa. "Wallahi babu tantama yarinyar nan mayya ce, in bah mayya bah mene na shaƙe mata wuya wato so ki ke ki zuƙi jininta Koh? Toh ki sa ni jinin mu ɗaci ne da shi babu wata mayya da ta isa ta ce za ta sha mana jini".
Girgiza kai Du'a ta fara yi ta ce. "Na rantse ni ba mayya bace kuma ni bana shan jini, kawai kun yi min gurguwar fahimta ne shi ya sa, amma ni samm bah mayya bace".
Ture ta khadija ta yi ta ce. "Dalla ware dangin mayu kawai mai fara ƙafa, daga yau kada mu sa ke ganin kin kusanci inda Maryam ta ke, in kuma ba aka bah, sai kin gane kuranki.
Tana kaiwa nan ta bangaje Du'a. A ta ke Du'a ta faɗi a wajan a yayin da hawaye suka fara zarya a kan ƙun cin ta. Da sauri ta ta shi tare da yin hanyar waje da gudu.
Gudu ta ke yi babu ƙagautawa sai da ta yi tafiya mai nisan gaske ba tare da tana ganin gaban ta bah, bakin bishiya ta samu ta zauna sannan ta fara ku ka.
Ku ka ta ke tamkar ranta zai futa. Ɗago idanuwanta ta yi wanda su ka yi jajir ta ce.
"Me ya sa akan ta ke faruwa dani? Mene ne tsakani na da macizai, me ya sa na ke irin waɗan nan munanan mafarkan? Shin ko dai da gaske ina da halaƙa da macizai?".
"Me ya sa ma banyi zama na a kauye bah? Da nasani ban zo birni bah na yi zama na a ƙauye domin nafi samun farin ciki a chan".
Miƙe wa tsaye ta yi tare da share hawayen ta ta ce.
"Ni wace ce? Me ya sa nake iya mu'amala da macizai bayan kuma ni ɗin mutum ce? Tabbas maganar su khadija gaskiya ne. kenen da gaske ni mayya ce? me ya sa zan kasance mayya bayan a dangi na babu mayu, toh kodai mamata mayya ce?".
Ji ta yi gaba ɗaya ku kan tsuntsaye ya gauraye wajan yayin da aka fara iska mai ƙarfi wanda ya ke haɗe da guguwa. a ta ke ta fara kalle-kalle, tare da juya wa.
Juyawar ta ke da wuya ta ga wani jibgegen baƙi maciji wanda ya zalalo da harshen sa wanda ke a tsage gida uku.
Zaro ido ta yi waje sannan ta sa ki wani irin ihuu da sauri ta fara ja da baya-baya, sannan ta fara ƙoƙarin guduwa, kafin ta yi wani yunkuri, macijin ya nannaɗe ta tare da ɗaga ta sama.
Ƙoƙarin kwace kan ta ta ke amma akan ya cutura. Rintse idanuwan ta ta yi don ta gama sallame wa cewa yau ne ranar mutuwar ta. Jin shiru babu abin da ya same ta, ya sa ta buɗe idanuwanta a hankali tare da ɗorawa akan na macijin.
Sauke ta macijin ya yi sannan ya shafa gashin kan ta da jelar sa na macijin daga bisani ya yi tafiyar sa.
Baki sa ke Du'a ta bi macijin da kallo sai da ta tabbatar idanuwanta sun daina ganin sa sannan ta ce. "Shi kuma wannan macijin daga ina ya fito? Me ya sa kuma zai zo waje na? Sannan fuskarsa ya nuna shiɗin ba ya da cutarwa".
Babu zato ta ji an dafa mata kafaɗa. A firgice ta juya da sauri ta ɗora idanuwanta akan na ta.
COMMENTS & SHARE PLS 🙏 🙏 🙏
ALKALAMIN ✍️
A'ISHA M.B💞💞💞
(Zinariyar🧝♀️ Jajirtattu)
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/D80k1puBPBn6uJhojKKhK5
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
🌹BISSMILLAHI RAHMANI RAHIM🌹
*🌸RAYUWA DA MACIJIYA* 🐍 🐍🐍
*PAID BOOK ₦400 complt*
kacal babu tsada
*9043687746 Hassana Aliyu Opay bank*
*Evidence of payment*
09130398321
*DA nayi niyar bar muku free page a aka, amma insha Allah zan kai muku shi twenty free page 🙏🙏🙏*
FREE PAGE ️1️⃣4️⃣➡️1️⃣5️⃣
WRITTEN & DIRECTED ✍️ BY A'ISHA M.B💞
(Zinariyar 🪙 Jajirtattu)
*_______________________________*
Rass gabanta ya faɗi! Yayin da jiri mai karfi ya fara ɗibanta, ta saki wani iriyar razannaniyar ƙara!. Da sauri ta fara ja da baya-baya sakamakon harba da ta yi da wata mai kama da ita sakk.
Riƙe kanta ta yi sannan ta nuna ta da ɗan yatsa a tsorace ta ce. "Wace ce ke? Me ya sa ki ke matuƙar kama da ni? Dan Allah na roƙe ki kada ki cutar da ni".
Murmushi aljanar ta yi sannan ta ce. "Ni bah cutar da ke na zo yi bah, ai idan na kwatanta taɓa lafiyar ki ni ce zan mutu bake bah. Dan aka ki tsaya ki saurari abin da zan faɗa miki". Ta faɗa tana nufar inda Du'a ta ke.
"Kada ki matso kusa da ni, bana so ki rabu dani dan Allah kada ki cutar da ni". Cewar Du'a.
Girgiza kai aljanar ta yi ta ce. "Na faɗa miki bah cutar da ke zan yi bah, ina so ne na sanar miki da wata muhimmiyar magana wacce za ta sa ki iya kare kanki a Koh ina, wanda koh mutum koh aljan bai isa ya tunkari inda ki ke da mugun nufi bah".
Kuka Du'a ta soma yi sannan ta ce. Yayin da hadari ya tashi aka fara yayyafi.
"Ni bana so, ki rabu da ni dan Allah". Ta ƙarashe maganar tare da juya wa da niyar tafiya. Babu zato taji ta yi tuntuɓe da dutse.
Luuu ta tafi tare da faɗuwa a kasan wajan. Jin takun takalmin mutun yasa aljanar ta ɓace daga farfajiyan wajan.
Karasawa wajan Maryam ta yi tare da kwallah kiran sunan Du'a. Jin shiru da ta yi ya sa hankalin ta ya yi matuƙar tashi. Da sauri ta fara waige-waige koh Allah zai sa ta ci karo da Du'a.