Sashe 11
Rayuwa Da Macijiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Toh faɗa min ta ya ya ba za su kalle ki bah? Nida bani da kyau gashi nan babu ma wanda ta ke kallona sabo da bana gaban ta, kawai ki kwanta kiyi bacci ki daina waɗan nan saƙe-saƙen a ranki".
"Na ji shi kenan zan kwanta" cewar Du'a.
Sai da Maryam ta rabbatar kowa ya gama uzurin sa sannan ta kai hannunta kan fitila domin kashe hasken ɗaƙin.
Ganin aka da Du'a ta yi ya sa ta saurin riƙe hannun Maryam damuwa lulluɓe kan fuskarta.
Mai da kallonta Maryam ta yi kan Du'a sannan ta ce. "Mene ne haka kuma Du'a? Me yasa kika riƙe min hannu lokaci ɗaya?".
Girgiza kai Du'a ta yi sannan ta ce. "Dan Allah Maryam kada ki kashe fitilan nan, wallahi ina matukar tsoron duhu, idan kika kashe zan iya shiga wani hali wanda ke kanki saikin zo kina da na sani ".
"Bana son duhu maryam ki bar wutan a kunne dan Allah".
Ɗaya daga cikin yan ɗaƙin ne ta kalli Du'a ta ce. "Aba baiwar Allah, ta ya ya zaki ce kada a kashe hasken wuta. Toh mudai sabo da ke ba zamu iya kwana cikin haske bah gaskiya".
"Haka ne Du'a, maganarta gaskiya ne, bai kamata a ce mun kwana cikin haske bah gaskiya, sabo da babu ma kyau kwana da haske, sai dai fa kiyi haƙuri, ki lallaɓa ki kwanta a aka". Maryam ta ƙarashe maganar tare da kashe fitilan ɗaƙin.
Cun kushewa waje guda Du'a ta yi yayin da zuciyarta ya tsananta faɗuwa. Ƙaƙƙarwa jikin ta ya soma yi, yayin da haƙoranta na dukan na sama da ƙasa.
A ta ke hawaye suka fara zarya akan fuskarta, babu zato ƴan ɗaƙin suka ji ƙaran tsawa da walkiya. Mamaki ne ya kama su sabo da a sanin su dai wannan lokaci bana damuna bane, amma kuma alamu sun nuna kamar za'a yi ruwan sama ne.
gurnanin Du'a Maryam ta faraji ƙasa-ƙasa, saurin kunna fitila Maryam ta yi tsreda mai da kallonta kan Du'a.
Rass ta ji gabanta ya faɗi! Cikin tashin hankali ta nufi inda Du'a ta ke ganin yadda gaba ɗaya ta rikice numfashinta na neman sarƙewa.
Tashi suma sauran ƴan ɗaƙin suka yi tare da tallafawa Maryam ta ɗago Du'a. Ganin tadda idanuwan Du'a ke jujjuyawa yasa gaba ɗaya tsoro ya baibaye zuciyoyin su.
Saurin miƙe wa ɗaya daga cikin matan ɗaƙin ta yi, sannan ta nufi inda bokitin ruwa ya ke. Ɗaukar kofi ta yi sannan ta ɗebi ruwa kaɗan a cikin kofi ta nufi inda su Du'a suke.
A hankali ta fara shafa mata fuskarta da ruwan koh Allah zai sa ta dawo dai-dai, amma kamar ma abin da ɗa ƙaruwa ya ke.
"Na shiga uku ni Maryam!, dama na sani ban kashe fitilan nan bah, yanzu mai zamu yi ta dawo dai-dai?".
"Ɗaya daga cikin ƴan ɗaƙin ne ta kalli Maryam ta ce. "Ki kwantar da hankalin ki wannan abin da ke damunta nasan ba zai wuce shafar aljanu bane, dan aka kawai mafita ɗaya ce, shi ne muyi mata ruƙiya koh Allah zai sa su lafa".
"A'a ƴar uwata bata da aljanu koh kaɗan, bana so ki kara ce mata tanada aljanu ".
Tana kaiwa nan ta miƙe da zimmar fita don neman wa kansu mafita.
Ji ta yi an riƙe mata hannu, waigawa ta yi tare da ɗora idanuwan ta kan nata. Baki na rawa Du'a ta ce. "Kada ku tayar da hankulan ku a kaina, wannan bah sabon abu bane, bah yau ne karo na farko dana fara shiga irin wanann halin bah, zan dawo dai-dai nan bada jimawa, kudai kawai ku kwanta kuyi bacci nasan ta yadda nake dawo da kaina dai-dai".
"Kin tabbatar zaki dawo dai-dai ba sai mun nemi mafita bah?". Cewar Maryam.
"Kwarai ina da tabbaci akan maganar dana faɗa, kawai kuyi abin da nace".
Jin hakan da suka yi ya sa gaba ɗayansu kwanciya cike da fargaban kada wani abu ya samu Du'a.
"Mene ne ya faru Inna wuro? Ya naga hankalin ki a tashe?". Cewar mai gari .
Amsa Inna wuro ta bashi da cewa. "Gaba ɗaya hankali na ya'ƙi kwanciya zuwa birnin da Du'a ta yi, tun ɗazu gabana yake ta faɗuwa, kuma bansan dalilin akan bah".
"Kuma jikina yana bani cewa Du'a na cikin halin tsaka mai wuya wanda babu wanda zai iya taimaka mata bayan mu da muka san duk matsalolin da ke damunta, ina tsoron kada wani abu ya faru da ita".
Murmushi Mai gari ya yi sannan ya ce. "Babu abin da zai faru in banda alhkairy, dan Allah ki daina irin wannan saƙe_saƙen a ranki, Allah shi ne mai karewa, kuma ina da tabbacin cewa Allah zai kare ta domin tana tareda albarkar iyaye da kuma albarkar mutanen kauyen nan".
"Maza kije ki kwanta dare ya yi, in sha Allahu ma babu abin da zai same ta ƙunshi?.
"Na ji shi kenan Mai gari na gode, ni yanzu zan koma ciki, da safe zamu ci gaba da yiwa mahaifiyarta magani sabo da na fara ganin sauyi a tattare da jikinta, alamu na nuna cewa nan kusa zata tashi".
"Masha Allah". Mai gari ya faɗa sannan ya ce. "Allah yasa akan, ubangiji ya saka ta farfaɗo nan kusa, domin yarta na matuƙar buƙatar ta".
Washe gari sa sassafe jikin Du'a ya yi sauƙi, harta shirya zata tafi aji domin daukar darasi. Kallonta Maryam ta yi ta ce. "Du'a kamar ba keba wallahi, kinga yadda kika bamu tsoro a jiyan nan".
Mai da kallonta Du'a ta yi kan Maryam ta ce. "Kinga dan Allah abar wannan maganar, ki tawo muyi sauri mu tafi aji sabo da kada mu makara".
Murmushi Maryam ta yi ta ce. "Ke in banda abinki wazai yi miki lecture ƙarfe shida na safe, koh mune ƴan hallazi boko ai sai akan, gaggawan me kike? Ki bari bakwai ta yi tukun nan sai mu tafi ".
Ɗaukar jakarta na saƙa Du'a ta yi sannan ta ce. "Kinga tafiyata, ni bazan iya jiran har ƙarfe bakwai ya yi bah, sabo da ina so naje na kofi rubutun da aka yi bana nan".
Dakatar da ita Maryam ta yi da faɗin toh idan ma za kije, sai ki tafi da wannan jakar dan Allah, ai saiki sa a raina mu. Kalli fah jakar gaba ɗaya ta yi muni da yawa gashi kuma saƙa ta aka yi, kawai ki ɗau ɗaya daga cikin jakunkuna na ki tafi dashi".
Girgiza kai kawai Du'a ta yi sannan ta ce. "Babu wanda ya ajiye ni a makarantar nan, ni karatu nazo yi bah gayu bah, duk abin da nake dashi toh shi zan saka, idan kuwa bani dashi toh bazan takura wa kaina don mallakar abin da banda shi bah ".
"Idan ma kallona za suyi koh zagi koh akasin aka toh sun daɗe basu yi bah. Ni kinga tafiyata sai kin tawo". Tana kaiwa nan ta fice daga ɗaƙin.
Ɗaukar jakarta Maryam ta yi tare da bin bayanta da sauri.
Tafiya mai nisa suka yi kafin daga bisani suka isa wajan department ɗin su.
Shiga ciki suka yi suka tarar babu kowa a cikin ajin. chan sama Du'a ta nufa tare da ajiye jakarta akan kujera sannan ita ma ta zauna akan kujerar da ta ke ganin shi yafi cancan ta ta zauna.
Zuwa Maryam ta yi kusa da ita sannan ta ce. "Du'a me zai hana ki samu wani kujeran ki zauna, wannan kujerar da kika zauna akai, na su Jennifer ne kuma babu wanda ya ke zama in banda Jennifer".
"Dan Allah ki nemi wani ki zauna". Murmushin takaici Du'a ta saki sannan ta kalleta ta ce.
"Ni dai dana zo wajan nan banga inda aka rubuta cewa iya Jennifer ce kawai ke da ikon zama akan wannan kujerar bah, shin kujerar daga gidan su ta tawo dashi koh me? Koh an rubuta a jikin kujerar cewa kada wanda ya zauna a kan wannwn kujeran, dan aka dan Allah ki rabu dani ".
Shiru Maryam ta yi mata sannan itama ta samu guri ta zauna. A hankali ɗalibai suka fara shigowa cikin aji, babu bata lokaci ajin gaba ɗaya ya cika, yayin da suka dinga bin Du'a da kallo.
Chan Maryam ta hango tawowar su Jennifer daga windon ajin. Da sauri ta taɓa Du'a Tare da faɗin. "Du'a ki tashi gatanan zuwa fah, dan Allah ki tashi kada tazo ta tarar dake a kan kujerar zamanta".
"Murmushi Du'a ta yi wanda ya sanya dimple ɗinta lotsawa, sannan ta ce. "Allah ya kawo ta lafiya, wallahi daɗi na dake Maryam bakida jarumta, samm bakisan darajar ki ta mace bah, ta ya ya wata ɗaliba zata zo tana tsorata ki, kuma ke.....
Maganar ta ne ya tsaya chak jin muryar Jennifer na faɗin. "Waya baki izinin zama a waje na, kinsan kuwa wace ce ni a makarantar nan, toh maza- maza ki tashi kafin na nuna miki ɗanyen kaina".
Miƙe wa Du'a ta yi murmushi ɗauke kan fuskarta ta ce. "Keda wannan bahamagen wanda kuke kira shugaban ɗalibai baku da maraba, shima aka ya ke kuri amma banga har yanzu ya aiwatar da abin da ya ce bah".
"Kuma kema aka, dan aka ki samu wani gurin ki zauna, dan kuwa wannan gurin karfi ya cinye".
Ƙoƙarin magana Jennifer ke yi suka ji shigowar lectura, harara Jennifer ta watsa mata sannan ta samu wani kujerar ta zauna akai.
Gaishe sa gaba ɗaya ɗaliban suka yi, daga bisani kuma lecturan ya fara koyar dasu darasi.
Sosai Du'a ke fahimtar darasin da ake koyarwa, duda cewar bah duka abubuwan ta ke fahimta.
A hankali ya sanya kafufawansa a cikin ajin. Ɗaliban ajin na ganin sa gaba ɗaya suka mimmiƙe, tare da gaishe sa.
Banda Du'a wacce ke zaune kamar bata san da shigowar sa bah.
Ran Ahmad ne ya soma ɓaci, ganin gaba ɗaya ta yi kamar bata san da shigowar sa ajin bah. Gyaran murya ya yi sannan ya ce.
Wace ce Du'a a wannan ajin? Jin ya ambaci sunan ta yasata ɗago da kanta ta ce. "Nice nan fatan dai komai lafiya?".
"Kallonta lecturan ajin ya yi, mamaki ɗauke akan fuskarsa ya ce. "Ke baki ga shugaban ɗalibai bane, ba zaki iya tashi ki gaida shi bah, baki ga kowa ya tashi bane?".
"Na ji shi kenan zan kwanta" cewar Du'a.
Sai da Maryam ta rabbatar kowa ya gama uzurin sa sannan ta kai hannunta kan fitila domin kashe hasken ɗaƙin.
Ganin aka da Du'a ta yi ya sa ta saurin riƙe hannun Maryam damuwa lulluɓe kan fuskarta.
Mai da kallonta Maryam ta yi kan Du'a sannan ta ce. "Mene ne haka kuma Du'a? Me yasa kika riƙe min hannu lokaci ɗaya?".
Girgiza kai Du'a ta yi sannan ta ce. "Dan Allah Maryam kada ki kashe fitilan nan, wallahi ina matukar tsoron duhu, idan kika kashe zan iya shiga wani hali wanda ke kanki saikin zo kina da na sani ".
"Bana son duhu maryam ki bar wutan a kunne dan Allah".
Ɗaya daga cikin yan ɗaƙin ne ta kalli Du'a ta ce. "Aba baiwar Allah, ta ya ya zaki ce kada a kashe hasken wuta. Toh mudai sabo da ke ba zamu iya kwana cikin haske bah gaskiya".
"Haka ne Du'a, maganarta gaskiya ne, bai kamata a ce mun kwana cikin haske bah gaskiya, sabo da babu ma kyau kwana da haske, sai dai fa kiyi haƙuri, ki lallaɓa ki kwanta a aka". Maryam ta ƙarashe maganar tare da kashe fitilan ɗaƙin.
Cun kushewa waje guda Du'a ta yi yayin da zuciyarta ya tsananta faɗuwa. Ƙaƙƙarwa jikin ta ya soma yi, yayin da haƙoranta na dukan na sama da ƙasa.
A ta ke hawaye suka fara zarya akan fuskarta, babu zato ƴan ɗaƙin suka ji ƙaran tsawa da walkiya. Mamaki ne ya kama su sabo da a sanin su dai wannan lokaci bana damuna bane, amma kuma alamu sun nuna kamar za'a yi ruwan sama ne.
gurnanin Du'a Maryam ta faraji ƙasa-ƙasa, saurin kunna fitila Maryam ta yi tsreda mai da kallonta kan Du'a.
Rass ta ji gabanta ya faɗi! Cikin tashin hankali ta nufi inda Du'a ta ke ganin yadda gaba ɗaya ta rikice numfashinta na neman sarƙewa.
Tashi suma sauran ƴan ɗaƙin suka yi tare da tallafawa Maryam ta ɗago Du'a. Ganin tadda idanuwan Du'a ke jujjuyawa yasa gaba ɗaya tsoro ya baibaye zuciyoyin su.
Saurin miƙe wa ɗaya daga cikin matan ɗaƙin ta yi, sannan ta nufi inda bokitin ruwa ya ke. Ɗaukar kofi ta yi sannan ta ɗebi ruwa kaɗan a cikin kofi ta nufi inda su Du'a suke.
A hankali ta fara shafa mata fuskarta da ruwan koh Allah zai sa ta dawo dai-dai, amma kamar ma abin da ɗa ƙaruwa ya ke.
"Na shiga uku ni Maryam!, dama na sani ban kashe fitilan nan bah, yanzu mai zamu yi ta dawo dai-dai?".
"Ɗaya daga cikin ƴan ɗaƙin ne ta kalli Maryam ta ce. "Ki kwantar da hankalin ki wannan abin da ke damunta nasan ba zai wuce shafar aljanu bane, dan aka kawai mafita ɗaya ce, shi ne muyi mata ruƙiya koh Allah zai sa su lafa".
"A'a ƴar uwata bata da aljanu koh kaɗan, bana so ki kara ce mata tanada aljanu ".
Tana kaiwa nan ta miƙe da zimmar fita don neman wa kansu mafita.
Ji ta yi an riƙe mata hannu, waigawa ta yi tare da ɗora idanuwan ta kan nata. Baki na rawa Du'a ta ce. "Kada ku tayar da hankulan ku a kaina, wannan bah sabon abu bane, bah yau ne karo na farko dana fara shiga irin wanann halin bah, zan dawo dai-dai nan bada jimawa, kudai kawai ku kwanta kuyi bacci nasan ta yadda nake dawo da kaina dai-dai".
"Kin tabbatar zaki dawo dai-dai ba sai mun nemi mafita bah?". Cewar Maryam.
"Kwarai ina da tabbaci akan maganar dana faɗa, kawai kuyi abin da nace".
Jin hakan da suka yi ya sa gaba ɗayansu kwanciya cike da fargaban kada wani abu ya samu Du'a.
"Mene ne ya faru Inna wuro? Ya naga hankalin ki a tashe?". Cewar mai gari .
Amsa Inna wuro ta bashi da cewa. "Gaba ɗaya hankali na ya'ƙi kwanciya zuwa birnin da Du'a ta yi, tun ɗazu gabana yake ta faɗuwa, kuma bansan dalilin akan bah".
"Kuma jikina yana bani cewa Du'a na cikin halin tsaka mai wuya wanda babu wanda zai iya taimaka mata bayan mu da muka san duk matsalolin da ke damunta, ina tsoron kada wani abu ya faru da ita".
Murmushi Mai gari ya yi sannan ya ce. "Babu abin da zai faru in banda alhkairy, dan Allah ki daina irin wannan saƙe_saƙen a ranki, Allah shi ne mai karewa, kuma ina da tabbacin cewa Allah zai kare ta domin tana tareda albarkar iyaye da kuma albarkar mutanen kauyen nan".
"Maza kije ki kwanta dare ya yi, in sha Allahu ma babu abin da zai same ta ƙunshi?.
"Na ji shi kenan Mai gari na gode, ni yanzu zan koma ciki, da safe zamu ci gaba da yiwa mahaifiyarta magani sabo da na fara ganin sauyi a tattare da jikinta, alamu na nuna cewa nan kusa zata tashi".
"Masha Allah". Mai gari ya faɗa sannan ya ce. "Allah yasa akan, ubangiji ya saka ta farfaɗo nan kusa, domin yarta na matuƙar buƙatar ta".
Washe gari sa sassafe jikin Du'a ya yi sauƙi, harta shirya zata tafi aji domin daukar darasi. Kallonta Maryam ta yi ta ce. "Du'a kamar ba keba wallahi, kinga yadda kika bamu tsoro a jiyan nan".
Mai da kallonta Du'a ta yi kan Maryam ta ce. "Kinga dan Allah abar wannan maganar, ki tawo muyi sauri mu tafi aji sabo da kada mu makara".
Murmushi Maryam ta yi ta ce. "Ke in banda abinki wazai yi miki lecture ƙarfe shida na safe, koh mune ƴan hallazi boko ai sai akan, gaggawan me kike? Ki bari bakwai ta yi tukun nan sai mu tafi ".
Ɗaukar jakarta na saƙa Du'a ta yi sannan ta ce. "Kinga tafiyata, ni bazan iya jiran har ƙarfe bakwai ya yi bah, sabo da ina so naje na kofi rubutun da aka yi bana nan".
Dakatar da ita Maryam ta yi da faɗin toh idan ma za kije, sai ki tafi da wannan jakar dan Allah, ai saiki sa a raina mu. Kalli fah jakar gaba ɗaya ta yi muni da yawa gashi kuma saƙa ta aka yi, kawai ki ɗau ɗaya daga cikin jakunkuna na ki tafi dashi".
Girgiza kai kawai Du'a ta yi sannan ta ce. "Babu wanda ya ajiye ni a makarantar nan, ni karatu nazo yi bah gayu bah, duk abin da nake dashi toh shi zan saka, idan kuwa bani dashi toh bazan takura wa kaina don mallakar abin da banda shi bah ".
"Idan ma kallona za suyi koh zagi koh akasin aka toh sun daɗe basu yi bah. Ni kinga tafiyata sai kin tawo". Tana kaiwa nan ta fice daga ɗaƙin.
Ɗaukar jakarta Maryam ta yi tare da bin bayanta da sauri.
Tafiya mai nisa suka yi kafin daga bisani suka isa wajan department ɗin su.
Shiga ciki suka yi suka tarar babu kowa a cikin ajin. chan sama Du'a ta nufa tare da ajiye jakarta akan kujera sannan ita ma ta zauna akan kujerar da ta ke ganin shi yafi cancan ta ta zauna.
Zuwa Maryam ta yi kusa da ita sannan ta ce. "Du'a me zai hana ki samu wani kujeran ki zauna, wannan kujerar da kika zauna akai, na su Jennifer ne kuma babu wanda ya ke zama in banda Jennifer".
"Dan Allah ki nemi wani ki zauna". Murmushin takaici Du'a ta saki sannan ta kalleta ta ce.
"Ni dai dana zo wajan nan banga inda aka rubuta cewa iya Jennifer ce kawai ke da ikon zama akan wannan kujerar bah, shin kujerar daga gidan su ta tawo dashi koh me? Koh an rubuta a jikin kujerar cewa kada wanda ya zauna a kan wannwn kujeran, dan aka dan Allah ki rabu dani ".
Shiru Maryam ta yi mata sannan itama ta samu guri ta zauna. A hankali ɗalibai suka fara shigowa cikin aji, babu bata lokaci ajin gaba ɗaya ya cika, yayin da suka dinga bin Du'a da kallo.
Chan Maryam ta hango tawowar su Jennifer daga windon ajin. Da sauri ta taɓa Du'a Tare da faɗin. "Du'a ki tashi gatanan zuwa fah, dan Allah ki tashi kada tazo ta tarar dake a kan kujerar zamanta".
"Murmushi Du'a ta yi wanda ya sanya dimple ɗinta lotsawa, sannan ta ce. "Allah ya kawo ta lafiya, wallahi daɗi na dake Maryam bakida jarumta, samm bakisan darajar ki ta mace bah, ta ya ya wata ɗaliba zata zo tana tsorata ki, kuma ke.....
Maganar ta ne ya tsaya chak jin muryar Jennifer na faɗin. "Waya baki izinin zama a waje na, kinsan kuwa wace ce ni a makarantar nan, toh maza- maza ki tashi kafin na nuna miki ɗanyen kaina".
Miƙe wa Du'a ta yi murmushi ɗauke kan fuskarta ta ce. "Keda wannan bahamagen wanda kuke kira shugaban ɗalibai baku da maraba, shima aka ya ke kuri amma banga har yanzu ya aiwatar da abin da ya ce bah".
"Kuma kema aka, dan aka ki samu wani gurin ki zauna, dan kuwa wannan gurin karfi ya cinye".
Ƙoƙarin magana Jennifer ke yi suka ji shigowar lectura, harara Jennifer ta watsa mata sannan ta samu wani kujerar ta zauna akai.
Gaishe sa gaba ɗaya ɗaliban suka yi, daga bisani kuma lecturan ya fara koyar dasu darasi.
Sosai Du'a ke fahimtar darasin da ake koyarwa, duda cewar bah duka abubuwan ta ke fahimta.
A hankali ya sanya kafufawansa a cikin ajin. Ɗaliban ajin na ganin sa gaba ɗaya suka mimmiƙe, tare da gaishe sa.
Banda Du'a wacce ke zaune kamar bata san da shigowar sa bah.
Ran Ahmad ne ya soma ɓaci, ganin gaba ɗaya ta yi kamar bata san da shigowar sa ajin bah. Gyaran murya ya yi sannan ya ce.
Wace ce Du'a a wannan ajin? Jin ya ambaci sunan ta yasata ɗago da kanta ta ce. "Nice nan fatan dai komai lafiya?".
"Kallonta lecturan ajin ya yi, mamaki ɗauke akan fuskarsa ya ce. "Ke baki ga shugaban ɗalibai bane, ba zaki iya tashi ki gaida shi bah, baki ga kowa ya tashi bane?".