← Book details Mi Ke Faruwa Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 51 OF 60

Sashe 51

Mi Ke Faruwa Complete Hausa Novel · about 7 min read

Kallon fuskarta yakeyi,ji yake tamkar ya bude kirjinsa ya sakata ciki,yace beauty kinji jiki,hankalina ya tashi sai zuciyata take sanar dani kamar zaki mutu ne tunda naga Allah ya kawo mana da sauki kila gobe na juya dama ina tsakiyar ayyuka,nan da wata uku zan gama in dawo mu zauna tare.tace yanzun ba zaka tsaya ayi suna ba?Sallamar su anty Salma ce ta katsesu,suka shigo suna faman taba baki,anty Fulera tana dauke da yaro,anty Fatima ce ta soma cewa,maijego kin tashi?Ai nazata bazaki iya tashi yanzun ba, saboda tsabar ragwanta. anty Salma tace gaskiya raguwa ce. Yrm yace kinfa san tun shekaran jiya take aikin abu daya,gaskiya tayi kokari,ni likitar cema naga alamar kamar bata san aikinta ba.suka ce ba wani nan ragwanta ne,Bily ta nuna ita dai tana jinsu yace to shikenan ku barta ta huta,suka mika masa yaron ya amsa yana kallon fuskarsa,sai yaji yaron ya burgesa,tunda ya amshi yaron shi take kallo ta gani shin yaya fuskarsa zata nuna,ga mamakinta sai taga yayi murmushi tare da cewa,yana da kyau bebyn,ta kalli su anty Fulera ta sunkuyar da kai,har suna hada baki gurin cewa munafunci in zakiyi magana yi mu kinga fitarmu,abinda haihuwarma kinyi kikayi kin tsaya sai yazo suka fita.Yrm yace,sun cika hayaniya,ya mika mata yaron yayi gashi ki ganshi ta girgiza kai,yayi dan murmushi yace,baki sonsa ne?Ta kallesa tana dan murmushi,sannan ta kalli yaron tace kai kana sonsa?Ya dago yaron zuwa bakinsa ya sumbacesa agoshi ina sonsa yanzun yana da kyau,tace kama da kai yayi?Yasa matashi a cinya kallesa ki gani,ta zata axuciya tace hasbunallahu wani'imal wakil,ya dubeta tace tsarki ya tabbata ga Ubangijin daya bamu wannan yaron,‘yar dariya yayi kin rude ko?Likitar ce ta shigo ta dubata sannan tabasu sallama tana tsokanar Yrm.yaso tafiya washegari, amma beauty da yaronta suna daukar hankalinsa har ya kara kwana,dazai tafi hadasu yayi ya rungume wayarsa ya fito da ita abin mamaki yana ta daukar hoton Bily da bebyn ta Lallai abin mamaki ne domin in kaga Yrm yana daukar hoto cikin waya to wani abu ne mai mahimmanci daya danganci aikinsa bazaka samu hotunan banza cikin wayarsa ba,domin bashi da lokacin zaman kallon hoto,tsiraici a hoto baya burgesa,yafi son ya gansa muraran.bayan ya gama yana bakin gadonsa itama ta zauna,idanunsa suna kan jaririn yace beauty ji nake tamkar kada na tafi, ya juyo da dubansa gareta yana kallon tsakiyar idanunta,nazo da sha‘awarki zan koma da abuna.ta matso ta kama tafukan hannunsa ta matsa,abin ya ratsasa har ya lumshe idanu tare da jn numfashi,tace daba don ina cikin biki ba,ko ban warke ba zan baka kaina har sai ka gaji,amma kada ka damu zan dinga zuwa maka cikin mafarki.ya tallabo fuskarta ya soma kissing dinta baki cikin baki,kukan yaron ne ya dawo dasu,shine ya rigata dauko yaron ya mika mata tasa shi a kafada yace no bashi nono in gani zama kiyi kyau da shayarwa?Tayi dan murmushi,ta soma kici- kicin ciro nono yana taimaka mata,yaron ya kama yana sha,Yrm ya tsura ma nonon idanu,sun cika sun kara girma, sannan basu kwanta ba,ya lura da kasan nonon yana da fadi,lallai ya taka sa‘a wannan baya faduwa komai tsufa,domin da irin masu faduwan ne ma gareta da sai yayi mata gyaransu sun mike.ya matso ya rataya hannunsa akafadarta ya saita wayarsa ya daukesu hoto su biyu ne suka fito don yaron yana cinyarta yana shan nono. Kwankwasa kofar ce ta dawo dasu daga shirman hotunan da sukeyi,Yrm ya bude kofar anty Saliha ce tace ina maijegon tun dazun nazo da baki ‘yan barka suna can a zaune tazo nan ta nane inba zata samu zuwa su gaisa ba to ta bani yaron.cikin fushi take maganar,yace haba anty tana zuwa muna sallama ne, ta juya fuu, yace taso kina da baki ni dai saura minti kalilan jirgin Lagos ya tashi,suka kalli juna tace sai munyi waya,yace to,sannan ya shafa kan yaron tare da sumbatar lebunanta sannan ta fita.yana rike da kofarsa yana kallonsu har ta sauka daga falon,yayi ajiyar zuciya ya koma yana hada shirginsa.Koda ta isa dakinta haka anty Saliha tayi ta mata masifa agaban dangin mijinta,wai ita ‘yar dadi miji,tabi ta like masa menene-menene, dhiru kawai tayi mata hardai suka fita haka akaci gaba da shagalin har zuwa ranar suna,inda yaro yaci sunan mai martaba,tun ana gobe suna ‘yan Zaria suka iso,Mansu kuwa tun kwana hudu da haihuwa ta iso.anyi suna irin na ‘yan gata,kyautuka dai maijego ta samu,kaya kuwa tasa har ta gaji,har washegarin suna jama‘a ce.sai da gari ya kara wayewa sannan Mansu ta tafi,bayan sun kammala komai ta bata kudade tasa mata cikin account dinta,don ita bazata samu fita zuwa banki ba.mai martaba doki yava takwaransa,Yrm yana kwance yana kallon hotunansu baya gajiya da kallon hotunan,wasu abokan course dinsa sunsha mamakin ganinsa yana kallon hoto harma suka tayasa kallo,sai gashi Yrm mai boye cewa yana da mata shine mai fadin matarsa ce da dansa,sun rude wanda har yaji haushin kansa me yasa ya nuna matarsa?Murna suka tayasa kan cewa yayi matukar dacen family koda yaushe Yrm yana nane da wayarsa,jira yake ya samu dan sarari zai kira beautynsa,waya ga ba sabon ba,su Yrm an shiga tarkon so sai dai shifa har yanzu bai san wai son matarsa yake ba kuma bai samu wanda zai sanar dashi ba.nata bangaren kuwa ba don har yau Yrm baice mata I love you ba data ce sonta yakeyi,koda bata san yaya so yake ba ai tana kallon fina-finai tana kuma karance-karance yanda Yrm ke nuna mata yasa ta bashi wata daraja cikin ranta.ita da Yrm yanzun kullum suna cikin lissafin kwanakin da suka rage masa,sannan anan gefen tana shirya masa kanta tana son ta tare shine yanda zai san tana da banbanci,sannan yasan har yanzu itace din dai,shiko nasa gefen tsaraba ce yake ta jibgo mata ita da danta,duk abinda ya gani sai zuciyarsa tace beauty zata so wannan,sai kawai ya loda in ma na yara ne sai yace kai bari in sai ma son,haka yake kiran yaron (son)wata rana kuma yace(my friend)wai yaron abokinsa ne tunda wai kwata-kwata da shekara nawa ya girmesa?Sai Bily tayi dariya.
[2/19, 10:08 AM] ‪+234 803 225 4928‬: 🏵MEKE FARUWA 85🏵

Tunda Yarima yace ma Bily beauty cikin satin nan zan diro,amma ba zance miki ga rana ba,ta kasa zaune ta kasa tsaye, harma su Umma sukai ta mata dariya.yau ta shirya wannan tayi wancan da kanta take shiga kitchen amma shiru sai kiga har dare babu labari,yau kam tasha alwashin ba zatayi komai ba,tana falon Umma bayan sallar la‘asar, Umma tana zaune kan kujera yayinda ta dora kafafuwanta kan tuf-tuf.yallabai wato jaririnsu Bily yana kan cinyarta,Bily tana zaune kasa kusa da kafafun Umma tana shafa mata maganin ciwon kafa,tare da dan mammatsa mata kafar Umma tace,‘yata yau baza‘ayi wa ubannawa girkin ba?Cike da tsokana tayi maganar,Bily tace,na gaji Umma,babankin nan ja min rai kurum yakeyi bawani zuwan da zaiyi.Umma tace,muma kinga ai munci girki kwana biyu, dama haka kika iya girki?Kafin Bily tace wani abu sai sukaji sallamar Yarima da wannan muryar tasa ta kasaita. Zaraf Bily ta mike tsaye tare da cewa, dama kana hanya? Shiko kallonsu yakeyi ransa yayi fari kar yanda ya samesu yaji dadi,Bily ji tayi tamkar ta rungumesa,shiko ita ya nufo sai tayi maza ta zauna ya kalli Umma yana dariya,sannan yasa hannu ya dauki dansa yana cewa, Umma son yayi girma fa,kuma ya kara kyau, gaskiya beauty ta iya haihuwa.Umma tayi dariya sannan tace, shirmen kan nan yana nan dai babana?To kaki sanar damu ranar dawowarka, kullum sai Bily tayi maka shiri na musamman in baka dawo ba mu da ‘yan gida kakarmu ta yanke saka sai mu kwashi gara, yace Allah sarki beauty yau dai gani ta dan harare sa cikin wasa tace,yau kam sai dai aci na gida nan ya gaida Umma sannan ya nufi sasansu Bily ta zauna zata cigaba da shafa ma Umma kafa tace a‘a-a‘a na yafe jeki gurin mijinki,haka ta bishi. Ai suna shiga falon farko ya ajiye(son)kan kujera ya jawota zuwa kirjinsa,wata irin ajiyar zuciya ya saki, jinsa yake tamkar an masa gafara,yace I miss you beauty,sannan ya lalubi bakinta.sun jima sannan suka dauki dansu zuwa sasansu. Nan ma da suka shiga ya kara jawo ta jikinshi ya tura hannuwan shi cikin rigar ta yana wani sansanar kamshin ta ta dan ture shi abban son kaki bari nayi maka sannu da zuwa ma ya dan tsotsi bakin ta toh ai beauty wannan ita ce sannu da zuwan ko? Ko akwai wanda yafi wannan ya kara shige mata dole ta hakura saida ya ja ta suka lula duniyar da suka kwana biyu basu je ba sannan suka yi wanka ta kawo mashi abinci yana ci yana kallonta yana jin nishadi da farin cikin dawowarsa wurin kyawawan iyalansa.
Chapter 51 · 0% Book details