← Book details Mi Ke Faruwa Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 60

Sashe 3

Mi Ke Faruwa Complete Hausa Novel · about 7 min read

Sana'o'i ta ringa yi sbulu, omo, manja,mangyada, lallai ana shan wahala da rayuwa,haka nan tayi ta kula da yaranta har suka soma tasawa. wata karamar sallah tazo nan ta shirya ita da yaranta, don zuwa bauchi, Bilkisu yarinya mai kyau da shiga zuci, lokacin shekarunta biyar, kawunta Aminu ya tafi da ita kallon hawan sallah, tana sha'awar kallon hawa ko a zariya tana son zuwa amma Mamanmu bata bari haka suke ce ma fatima, ba wanda ya burge Bilkisu gurin kallon hawan nan kamar wani dan yaron sarki ba zai fi shekara biyar ba tsaran ta kenan, an mishi nadi shima cikin wata alkyabba bayan shi runduna ce guda, yaron yana ta daga ma mutane hannu, itama sai daga hannu take tana mishi bye-bye, ai ko kullum bata da labari sai na Yarima. haka kawunta ya ce mata sunanshi har suka bar bauchi suka dawo zariya lbrin yarima take yi haka nan kuma sai ta shiga yin mafarkin yarima. kullum ta kwanta sai tace tayi mafarki sun wasa da yarima har abin ya ishi mamanmu tace kada in kuma jin zance yariman nan,
don haka ko tayi sai tayi shiru. kowane sassa zundenta suke wai ta ki dora ma yara talla gata da ya'ya mata, in ta tashi aurar da su saga ni me zata kai ma ya'ya daki? sam wannan bai damu mamanmu ba ita dai burinta shine taga 'ya'yanta sun samu tarbiya tare da kulawa. Bilkisu yarinya ce mai tsananin hakuri da zurfin ciki, tana da kwazon karatu da son karatu, sabanin Sakina mai fada da kin raini don haka duk kishiyoyin mamanmu ta tsane su matuka, Maryam ko sai dai fushi da miskilanci. Asma'u auta itama akwai tsiwa tun tana karamarta, yanda yayyinu suk dukan Bilkisu sai dai ta yi kuka. Asma'u kam bata raga ma abokan goyonta shi yasa rigima kullum. Salame ta shiga dakin karima tana fadin ke 'yar gari king uwar mata? Me tayi? In ji karima bayan ta bada dukkan hnkalinta, Yau kuma takalma silifas sababbi ta sai musu. kan ta yi magana sai ga Ladiyo, kunga uwar mata? A gindinsu zata kare an siyo musu silifa. Karima taja tsaki ai ta haifar ma kanta wahala mata kai ta musu bauta ko gidan Miji suka je ba ka huta ba, mu ko masu mazan da farko in sun kawo karfi sai dai mu kwanta su mana su ma kannansu matan. salame ta ce ai Allah ya taimake mu da muka fara da maza. Ladiyo ta ce ni duk ba wannan ya dame ni ba, irin in ma kalli Bilkisun nan yarinya kyau tamkar aljana? salame ta ce kuma tafi sonta ba, tsorona daya kada wani mai halin ya aure t. Ladiyo tace kada nima ina wannan tunanin amma ga shawara ta rada musu wata magana a kunnuwansu, suka saki dariya tare da fadin kin kawo shawara. Bilkisu da kannanta cikin kayan islamiya suka nufi islamiyya, sai da ta raka kannanta kofar ajinsu Sakina da mami, sannan ta tafi ajinsu, duk malaman makarantar sun son Bilkisu saboda kokarinta tare da hazaka ga ladabi ga kuma tsafta duk da cewa kayan makarantar tasu sun tsufa amma tsaf suke a wanke. ta shiga suka soma karatu, basu dade ba wani malami ya shiga da wata yarinya sabuwar zuwa ce, duk ba zata fi Bilkisu ba, ta shigo tana yan kalle-kalle alamun bakunta Bilkisu ta kalle ta cike da murmushi,
[2/19, 9:56 AM] ‪+234 803 225 4928‬: 🏵MEKE FARUWA 07 🏵

don haka sai ta je ta zauna kusa da bilkisu. Bayan sun tashi sun fita bilkisu tace yaya sununki? Ta ce Mansura Sadik, ke fa? Ta ce ni sunana B M S, da fatan zamu zama kawaye? Mansura cikin murna ta ce. Insha Allahu. Ta debo kannanta itama da kaninta Abba ta dakko shi daga ajin da aka kaishi suka jero suna hira. Gidan su Mansura ba shi da nisa da islamiya, don haka Mansura ta roki Bilkisu ta shigo ta gaida Ummanta, jikin Bilkisu yayi sanyi da ganin daular da su Mansura suke ciki, lallai Mansura ba abokiyar yinta bace, domin an ce kwarya ta bi kwary. hajiya mero mahaifyar mansura nurse ce mahaifinta kuwa ma'aikaci ne a {G T Bank} da ke kaduna.
makarantar bokonsu ta kudi ce mai tsada, haka ne yasa Bilkisu dan Jan jiki da Mansura, amma Mansura sai ta kara shige ma Bilkisu ta ki sai wata rana bata da lafiya don haka bata samu zuwa islamiyya ba hankalin Mansura ya tashi don haka kuwa ana tashi ta bi su Sakina don ta dubo Bilkisu. Sam Mansura bata damu da yanda taga gidan su Bilkisu ba, har ma da ta samu Mamanmu ta gama tuwo sai da taci, hakan ya sanyaya zuciyar Bilkisu don tana son Mansura musamman ma da ya ke Mansura iyayanta sun kasance yan gombe, tana ganin gombe da Bauchi kamar daya ne gunta tana son yan Bauchi dangin uwa masu sonta, tana ganin kamar bata da masu sonta sai yan Bauchi shi yasa duk inda ta ga yan Bauchi tana girmamamasu, Mansura tana da son tuwo don haka sai ta samu gurin zuwa.

Ko Bilkisu bata nan Mansura tana zuwa gurin Mamanmu jin ta take tamkar mahifiyarta waton Ummanta suka niyan gidan sai suka tsiri sakin habaici, Bilkisu ma nan ta saki jiki da Umma Umma da Mamanmu suka zama kawaye, haka ya sosa ran su Ladiyo musamman da suka ga tana basu kayan sawa zuwa dan abin marmari.

Bilkisu tana zaune ciki wani ciyayi mai kama da cafet guri sanyi da iska yanda yake Kore fatau ya bata sha'awa ga fararan tattabaru suna tashi wasu suna sauka. Can daga nesa sosai take hango dan matashin yaron tasaranta bisa kan doki yana isowa gurinta ya tsaya cike jin kai. Yace ke wa ya kawo ki gonata?

Ta dube shi nan ne gonarka? Kafin ya bata amsa sai ga wasu mutane su biyu suka kama mishi linzamin doki ya sauka, sannan ya isa wata kujera dake can gefe irin ta sarakannan ya zauna sai ga wasu mutane cikin jaja yan kaya sun tsaya a bayanshi, can kuma sai yace na sallame Ku. Suna tafiya ya dawo gurin Bilkisu ya zauna kusa da ita ke yar sakin wane lardi ne? Ta dube shi ba ni da alaka da sarauta. Ta bashi amsa, yace kin sanni? Ta dube shi cike da mamaki kai ba ka da gane mutane so nawa muna wasa da kai? Firgigita ta farka daga bacci yau mafarkinta ba irin na sauran ranaku ba ne, domin sauran ranakun tafi mafarkin suna wasan kwallon kafa, ko na raga koma na tebur, suna hira sosai, amma ya kan nuna bai ma Santa ba ne, tayi murmushi, tun tana yar shekara shidda take mafarkin Yarima gashi yanzun tana shekarar karshe a primary shekarar haihuwa kuwa sha daya su Bilkisu an soma zama yammata, kyanta kullum karuwa yake yi.
Hankalin mamanmu ya tashi domin ba ta da kudin da zata yi ma Bilkisu hidima dan zuwa secondary, duk da cewa ta ci domin makarantun gwamantin ma wannan zamanin sai kana da hali. Da kanta taje makarantar da Bilkisun ta ci sun mata lissafin tun daga rijista zuwa uniform da takardu dubu takwas har da dori. Hankalinta ya tashi bata da inda zata samo kudin nan, gidan hajara kawarta ta shiga don yin shawara, hajara ta bata shawarar me zai hana Bilkisu ta yi aikin gida ko na wata uku ne, in yaso sai ta shiga a zango na biyu tun da an amso form. Mamanmu jarumar uwa ce wacce samun kamarta sai an tona, tsamaranta cewa zata zamar wa ya'yanta uwa kuma uba, don haka ta ce ma hajara ni zan yi aikin da kaina wa ki ke ganin zan samu ya nemo min aiki? Hajara ta ce kada ki damu akwai mata masu hali da suke zuwa gurin malam zan dinga musu magana har a dace, shin maigidan naku zai barki?
[2/19, 9:56 AM] ‪+234 803 225 4928‬: 🏵MEKE FARUWA 08 🏵
Chapter 3 · 0% Book details