Sashe 14
Mi Ke Faruwa Complete Hausa Novel · about 6 min read
Ga kujeru na alfarma kusan gefe uku kowacce da kalarta kuma ta dace da gefen da aka jera su, wata Dattijuwa ta nufo su da fara'a tana cewa Aa umar farooq kune a gidan ina gajiya?yace babu gajiya hajjo umma tana ciki kuwa?Tana nan bari ayi muku iso,ta fito tace gata nan zuwa, sai nan ta shiga gyara mata inda zata zauna,ma'ana ta shiga kakakabe kujerar duk da ba ko kura akanta,kyakkyawar mace ta fito sanye cikin wani leshi na alfarma, gwala-gwalai ne suke kyalli a yatsunta a hannun da na kafa, zuwa wuyanta. Tunda ta fito take kallon bilkisu a zuciyarta kuwa fadi take masha Allah, ta zauna kan kujerar ta dubi farooq da suka zube kan carpet tace idonka kenan ko farooq?Yayi murmushi yace ayimin afuwa umma, ta dubi su mansura tabe to wace ce matar taka cikinsu ko dukansu ne?Yana 'yar dariya ya nuna mansura sannan ya mika mata dady,kiyi hakuri umma ko gombe ma ina dadewa ban zo ba,saboda yanayin aiki wannan karon ma dan hutu ne muka samu,shi ne muka zo gaishe ku, tace to mungode Allah yayi albarka,
.ta nuna Bikisu wadda kanta ke sunkuye tace wannan fa?Bata san me yasa yarinyar ta tsaya mata a zuciya ba,farooq ne yayi magana,kawar mansura ce itama ta biyo mune tayi gaisuwa,umma tace mungode kwarai amma tana da aure ne?Yace tukunna dai tace to Allah yabaki miji na gari,shi da mansu suka ce amin, tace umman taka fa? Tana gaishe ki su sumayya ma ina ga yau za su zo,yaya gurin su anty salma su Aisha?Ta ce duk suna lfy sai gobe zasu zo gaida mai martaba,yace sai dai a gaishe su dan gobe zamu juya Modibbo ma mutane sun mishi yawa bai san ma munzo nan ba,tace yau kam Modibbo ai har dare amsar gaisuwa zai dinga yi.yanzun nan ma nake ma takwaranshi magana yazo yaje ya gaida shi tunda kwana uku zuwa hudu zai yi ya tafi farooq yace Al'amin yazo ne? Tace jiya me martaba yace mishi yazo gida yayi salla farooq yace ya fito ne?Yaushe rabon da mu hadu anfi shekara7,Umma tace kai dashi duk ba masu son zumunci bane bari in kira muku shi ku gaisa,
Dai dai nan wasu 'yanmata su biyu suka soma jere kayan ciye-ciye da shaye-shaye a gaban su mansura da farooq. Bilkisu gabanta ya tsananta faduwa kanta kuma yana kasa wasa take da zoben dake karamin yatsanta, umma ta kira layin Yarima tace babana ga yayanka ummar faruk kazo ku gaisa yace to su dan jira shi zai yi wanka, tace babana kayi sauri na sanka fa,yace to su ka ci gaba da hira tare da 'yan ciye-ciye, bilkisu kam kasa cin komai tayi kuma sai ta samu kanta da matsanancin jin nauyin umma,kula da hakan da umman tayi na kin ki cin komai da bilkisun tayi ne yasa tace ke kin ki cin komai saboda me?Ta dubi umman cikin jin kunya tare da dan murmushi,ta ce na koshi ne.Umma tace ka'idar gidan nan in ka shigo sai kaci abincin gidan,tasa hannu ta dauki yankakken apple ta saka abaki,tana taunawa a hankali idanun umma na kanta yarinyar sha'awa take bata,ta dubi mansura, yaya sunan kawar taki ne?Mansura tace sunanta bilkisu a ranta tace ta ci sunanta,Bilkisu maigadon zinari..
Kamshin data ji ne yasa gabanta ya tsananta faduwa menene take jine kodai mafarkin tane na yau da kullum?Muryar nan ta Yarima ta jiyo mai cike da kasaita da son girma, ya dubi farooq cike da sakin fuska yace,yayana sannu da zuwa,ashe da rabon zamu gaisa ne, farooq ya mike tare da mika mishi hannu,suka yi musabaha yana tambayar farooq iyali ya nuna mansura yace gata nan,ya dubi dady dake wasa kusa da umma, yaronka ne wannan? Yace eh Yarima ya tsugunna kusa da daddy yace Hello handsome, mansura tace ina yini, ya zuba manyan idanunshi kan fuskarta, yace lafiya yaya boy da yayana tace lfy,Bilkisu kam ta kasa dago ido ta kalli Yarima ganinta irin mafarkin da ta saba yi ne,mansu ta tabata tare da yi mata alama da ido wai su gaisa da Yarima, ta dago ta dube shi dai dai sanda ya zubo nashi idon kanta miyan bakinta ya kafe,ta kasa motsa lebanta ma bare ta iya furta wani abu,shi dai ya kauda kanshi amma zuciyarshi cike da mamaki,kyawunta tafi kama da larabawan gabas ta tsakiya,
Fiye da yan nigeria ta kuma kallonshi tana son ta tabbatar da cewa ba mafarki take yi ba,don haka tace Yarima! Ya kalle ta da sauri tayi dan murmushi har yanzun baka huce ba kenan?Cikin mamaki ya dube ta,a ina ki ka sanni ni?Ta dubi mansura sai kuma tayi shiru. Farooq yace cikin mamaki,kin san shi ne Bily?Tace tunda bai gane ni ba bar shi kawai,shiru Yariman yayi yana son tuna inda ya santa,umma cikin dan murmushi tace babana baka santa ba? Ya mike tare da fadin ban taba ganinta bafa, cike da rainin wayo ya fada,har ma su mansura da umma basu ji dadin yanda yayi ba,musamman mansura da tasan cewa Bilkisu ba ta da son magana da maza to ko shi ne Yariman mafarkinta?Shi ko ciki ya koma bilkisu ta bishi da kallo,Yariman mafarkinta ne tabbas, meyasa bai gane taba? Shin ko shi ba ya mafarkinta ne?Abokin wasanta tun suna yara? Suyi fada suyi wasa.
[2/19, 9:57 AM] +234 803 225 4928: 🏵MEKE FARUWA 25🏵
Har suka koma gidan Modibbo mamakin Yarima tayi tana kwance a kan katifa a masaukinsu, Mansura ta dafata Bily a ina ki ka San Yarima? Cike da nadamar yi mishi magana ta ce shi ne Yariman mafarkina, tun muna yara amma dubi yanda yayi min, ba laifinshi ba ne ni ce da na mishi magana, Mansura ta dan yi murmushi kin manta ne cikin mafarki ne? Kin manta cewa mafarki ba gaskiya ba ne? Sam Bilkisu ta manta da wannan batun har ma ta ji haushin kanta game da maganar da ta mishi, tayi data sani sannan ta cika da al'ajabin ganin Yarima yanda ta San shi a mafarki haka yake.
Farooq ne zaune gaban tsohon suna tattaunawa cikin nisan dare, ya sanar mishi da Abu buwa masu yawa game da Bilkisu kuma tsohon ya yi mishi alkawarin ganawa da ita, da safe bayan yayi istihara kan lamarinta, hakan ce ta kasance da safe inda ya gana da Bilkisu ya yi mata yan tambayoyi domin yaga Lamari da yawa cikin al'amuranta, ya dube ta jikata ki kanyi mafarki ne haka ko na ruwa ko na gini ko na wani mutum? Tace eh to na kan yi mafarkin wani tun ina yarinya kuma har yanzu ina yi sai dai in ban kwanta ba, ya dube ta kamar ya ya kike yi? Tace ina mafarkin shi wani dan sarki ne, muna wasa kuma yana yawan ce min in je in nemi tarihinsa, tsohon ya kalle ta na tsawon lokaci tamkar me son ya karanci wani Abu a fuskarta, sannan yace Bilkisu In'sha Allah za ki yi aure, kuma a yanda na fahimci al'amaran mijin naki zai kasance wani ne ma'ana babban mutum ne, kuma lokacin ya kusa sai dai naga rigingimu da yawa kici gaba da addu'a nima zan taya ki, kanta a kasa tace In'sha Allah zan dinga yi zuciyar ta kam tab da tunanin wai ta kusa aure? Kuma mijin dan babban gida ne?
.ta nuna Bikisu wadda kanta ke sunkuye tace wannan fa?Bata san me yasa yarinyar ta tsaya mata a zuciya ba,farooq ne yayi magana,kawar mansura ce itama ta biyo mune tayi gaisuwa,umma tace mungode kwarai amma tana da aure ne?Yace tukunna dai tace to Allah yabaki miji na gari,shi da mansu suka ce amin, tace umman taka fa? Tana gaishe ki su sumayya ma ina ga yau za su zo,yaya gurin su anty salma su Aisha?Ta ce duk suna lfy sai gobe zasu zo gaida mai martaba,yace sai dai a gaishe su dan gobe zamu juya Modibbo ma mutane sun mishi yawa bai san ma munzo nan ba,tace yau kam Modibbo ai har dare amsar gaisuwa zai dinga yi.yanzun nan ma nake ma takwaranshi magana yazo yaje ya gaida shi tunda kwana uku zuwa hudu zai yi ya tafi farooq yace Al'amin yazo ne? Tace jiya me martaba yace mishi yazo gida yayi salla farooq yace ya fito ne?Yaushe rabon da mu hadu anfi shekara7,Umma tace kai dashi duk ba masu son zumunci bane bari in kira muku shi ku gaisa,
Dai dai nan wasu 'yanmata su biyu suka soma jere kayan ciye-ciye da shaye-shaye a gaban su mansura da farooq. Bilkisu gabanta ya tsananta faduwa kanta kuma yana kasa wasa take da zoben dake karamin yatsanta, umma ta kira layin Yarima tace babana ga yayanka ummar faruk kazo ku gaisa yace to su dan jira shi zai yi wanka, tace babana kayi sauri na sanka fa,yace to su ka ci gaba da hira tare da 'yan ciye-ciye, bilkisu kam kasa cin komai tayi kuma sai ta samu kanta da matsanancin jin nauyin umma,kula da hakan da umman tayi na kin ki cin komai da bilkisun tayi ne yasa tace ke kin ki cin komai saboda me?Ta dubi umman cikin jin kunya tare da dan murmushi,ta ce na koshi ne.Umma tace ka'idar gidan nan in ka shigo sai kaci abincin gidan,tasa hannu ta dauki yankakken apple ta saka abaki,tana taunawa a hankali idanun umma na kanta yarinyar sha'awa take bata,ta dubi mansura, yaya sunan kawar taki ne?Mansura tace sunanta bilkisu a ranta tace ta ci sunanta,Bilkisu maigadon zinari..
Kamshin data ji ne yasa gabanta ya tsananta faduwa menene take jine kodai mafarkin tane na yau da kullum?Muryar nan ta Yarima ta jiyo mai cike da kasaita da son girma, ya dubi farooq cike da sakin fuska yace,yayana sannu da zuwa,ashe da rabon zamu gaisa ne, farooq ya mike tare da mika mishi hannu,suka yi musabaha yana tambayar farooq iyali ya nuna mansura yace gata nan,ya dubi dady dake wasa kusa da umma, yaronka ne wannan? Yace eh Yarima ya tsugunna kusa da daddy yace Hello handsome, mansura tace ina yini, ya zuba manyan idanunshi kan fuskarta, yace lafiya yaya boy da yayana tace lfy,Bilkisu kam ta kasa dago ido ta kalli Yarima ganinta irin mafarkin da ta saba yi ne,mansu ta tabata tare da yi mata alama da ido wai su gaisa da Yarima, ta dago ta dube shi dai dai sanda ya zubo nashi idon kanta miyan bakinta ya kafe,ta kasa motsa lebanta ma bare ta iya furta wani abu,shi dai ya kauda kanshi amma zuciyarshi cike da mamaki,kyawunta tafi kama da larabawan gabas ta tsakiya,
Fiye da yan nigeria ta kuma kallonshi tana son ta tabbatar da cewa ba mafarki take yi ba,don haka tace Yarima! Ya kalle ta da sauri tayi dan murmushi har yanzun baka huce ba kenan?Cikin mamaki ya dube ta,a ina ki ka sanni ni?Ta dubi mansura sai kuma tayi shiru. Farooq yace cikin mamaki,kin san shi ne Bily?Tace tunda bai gane ni ba bar shi kawai,shiru Yariman yayi yana son tuna inda ya santa,umma cikin dan murmushi tace babana baka santa ba? Ya mike tare da fadin ban taba ganinta bafa, cike da rainin wayo ya fada,har ma su mansura da umma basu ji dadin yanda yayi ba,musamman mansura da tasan cewa Bilkisu ba ta da son magana da maza to ko shi ne Yariman mafarkinta?Shi ko ciki ya koma bilkisu ta bishi da kallo,Yariman mafarkinta ne tabbas, meyasa bai gane taba? Shin ko shi ba ya mafarkinta ne?Abokin wasanta tun suna yara? Suyi fada suyi wasa.
[2/19, 9:57 AM] +234 803 225 4928: 🏵MEKE FARUWA 25🏵
Har suka koma gidan Modibbo mamakin Yarima tayi tana kwance a kan katifa a masaukinsu, Mansura ta dafata Bily a ina ki ka San Yarima? Cike da nadamar yi mishi magana ta ce shi ne Yariman mafarkina, tun muna yara amma dubi yanda yayi min, ba laifinshi ba ne ni ce da na mishi magana, Mansura ta dan yi murmushi kin manta ne cikin mafarki ne? Kin manta cewa mafarki ba gaskiya ba ne? Sam Bilkisu ta manta da wannan batun har ma ta ji haushin kanta game da maganar da ta mishi, tayi data sani sannan ta cika da al'ajabin ganin Yarima yanda ta San shi a mafarki haka yake.
Farooq ne zaune gaban tsohon suna tattaunawa cikin nisan dare, ya sanar mishi da Abu buwa masu yawa game da Bilkisu kuma tsohon ya yi mishi alkawarin ganawa da ita, da safe bayan yayi istihara kan lamarinta, hakan ce ta kasance da safe inda ya gana da Bilkisu ya yi mata yan tambayoyi domin yaga Lamari da yawa cikin al'amuranta, ya dube ta jikata ki kanyi mafarki ne haka ko na ruwa ko na gini ko na wani mutum? Tace eh to na kan yi mafarkin wani tun ina yarinya kuma har yanzu ina yi sai dai in ban kwanta ba, ya dube ta kamar ya ya kike yi? Tace ina mafarkin shi wani dan sarki ne, muna wasa kuma yana yawan ce min in je in nemi tarihinsa, tsohon ya kalle ta na tsawon lokaci tamkar me son ya karanci wani Abu a fuskarta, sannan yace Bilkisu In'sha Allah za ki yi aure, kuma a yanda na fahimci al'amaran mijin naki zai kasance wani ne ma'ana babban mutum ne, kuma lokacin ya kusa sai dai naga rigingimu da yawa kici gaba da addu'a nima zan taya ki, kanta a kasa tace In'sha Allah zan dinga yi zuciyar ta kam tab da tunanin wai ta kusa aure? Kuma mijin dan babban gida ne?