Sashe 4
Masarautar Mu Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Wajejen karfe takwas suka fara shigowa mazansu da matansu iyalin Mai Askira. Yaa Maira ce karshen shigowa har da bawan Allah Ashgar wanda bai san me ake yi ba shi dai an kira shi kuma ya zo.
Babban falon saukar bakin Fulani na musamman aka bude musu, kuyangin Fulani sai shige da fice suke suna shirya abinci na alfarma. Sai hirarrakinsu ke tashi cikin kasaita da taushin murya kamar ba magana ke tashi a falon ba sabida yadda suke yin ta cikin nutsuwa da salama. Sassan Fulani Bilkisu ya game da kamshin turaruka na alfarma, wannan na wane wannan. Ya kuma cakude da na wuta irin nasu na barebarin usli, ga sanyi da rabar iya kwandishan na ratsa su.
Ba jimawa Fulanin Askirama ta shigo cikin falon, as usual cikin kwalliya ta alfarma, ta fi kowacce iya tsara kwalliya cikin matan Mai Askira kamar yadda duk ta fi su kuruciya da daukar ido. Da faraa sosai wadda ta fiddo hakoran Makkanta na danyen gold guda biyu ta ke musu barka da zuwa. Ta dubi Mairam-Murjanatu cikin jin dadi ta ce,
Har da mutanen Istanbul? Lallai kuna ji da wannan yar kanwa taku, ga shi ta shige daki ta rufe balle ku gaisa.
Ya Maira ta ce, Kyale Saadatu kin ji? Kunya ce irin ta Baggara, me ake da amaryar da babu kunya? We really appreciate, muna nan tare har abada ai.
Mairam Murjanatu ta muskuta cikin lallausar royal chair three seater da take zaune a kai, ta ce,
Shin wane shiri ki ka yi Fulani game da biki ki gaya mana mu ji?
Fulani ta yi dan murmushi ta ce, Ban shirya komai ba. Na bar muku wuka da nama, ku ne Yayyenta kuma surukanta. Ni ina gefe yar kallo ce.
Yaa Maira ta ce, To madallah da wannan girma da anka ba mu, mu kuma za mu shirya mashahurin biki na alada, wanda za a dade baa manta a masarautar nan ba. Za mu huce na auren farko da ba mu samu yi ba.
Daga nan Fulani ta yi umarni a zo a yi serving dinsu abinci.
Sun dade suna tsare-tsare da shirye-shiryen yadda abubuwa za su gudana a junansu, bayan sun gama cin abinci. Fulani ba ta saka musu baki sai dai ta raka da eh ko aah.
Yaa Maira ta dubi kannenta su Murjanatu ta ce.
“Kamar yadda kuka riga kuka sani a aladar bikin gidan nan za mu fara da sakun lalle ranar laraba, alhamis za mu yi nakiya, jumaa wushe-wushe, ranar asabar ake daurin aure, to tunda an riga an daura ba shiri, to a ranar ne za mu yi kelatul (wanke kai da kitso na amarya), sannan mu yi Biji Ginata (ana shimfida tabarmi ne a ranar a ajiye amarya ana kida ana wakoki bayan an yi mata kwalliyar masarauta.
Ranar lahadi za mu yi kaulu na amarya da ango da safe (kaulu shi ne, zaa ajiye miyar yauki a gaban amarya bayan an mata kitso da kwalliya, Baaba za su goyo amarya (sisters din Maimartaba su ne Baaba) su kai ta wajen Kaulu, yan uwa da iyaye su dinga dibar wannan miyar yaukin suna shafa mata. Da daya da daya kowa zai zo yana shafa mata yana ajiye wa amarya kyauta, wasu har gold suke badawa, wasu iphone ko mota ya danganta da mukamin mutum a masarautar, wasu kuma kyautar kudade suke yi, kaulu kenan.
Da yammacin lahadi kuma za mu yi ‘dubdo’, wato wunin biki a gidan amarya bayan an kai ta ranar asabar da daddare (a wannan ranar yan uwa da iyaye za a wuni ana shige da fice a gidan amarya.
Ke kuma Fulanin Maimartaba ke ce da alhakin yin Miskero (abincin da ake kai wa gidan amarya ranar wunin) wanda jamaa da ke shiga da fita a gidan za su ci.
Sannan a satin bikin gabadaya har ila yau ke za ki dinga ciyar da amarya da ango abinci mai kyau. Har zuwa ranar da za a kai amarya, wato asabar.
Idan asabar ta zagayo kuma ana ‘tulur’, wato sati daya da kai amarya, ranar ne ke da kawayenki (Fulani Bilkisu) da yan uwan amarya za ku je gidan amarya, mu kuma za mu yi mata kwalliya, sai a saka mata muciya a hannu, a ranar za ta fara girki kenan, ana wakoki da raye-raye, a ci a sha, to daga nan biki ya kare.
Ranar asabar kuma za mu kawo lefe.
Fulani ta ce, Turkashi, wani aiki sai Amale, bikin Kanuri sai Askira! Allah ya sa muna da rabon gani.
Aka yi adduoi aka shafa, bayan mazan ma sun yi nasu tsare tsaren, sannan duk suka fara watsewa. Amma sai da daya daga cikin kannen Yarima da ake kira Houdda yar dakin Yakirjinoma ta je har kofar dakin Saade ta yi magana ta hudar kofar dakin tamkar mai yin waka cikin harshen Kanuri.
Ki gama boyon amarya, kin riga kin zo hannu, da sannu za mu yi miki kaulu, kelatul, biji ginata da tulur, sannan mu damka wa Yarima ke.
Murjanatu ta zuba mata duka a baya [dundu], ta ce, Houdda kar da ki tsoratata ta kara kunshewa a daki duk zafin nan da ake yi, in kika firgita masa amarya ke da shi ne, kin fi kowa sanin halin sa.
Saade da ke cikin daki duk tana jinsu ba ta san sanda ta fashe da kuka ba..
Da gaske dai ya tabbata an yi mata auren kenan, this is the reality da take ta kokawa da zuciyar ta wajen yarda da shi. Take yaudarar kanta da kanta da cewa mafarki ne. Iyalin Askirama bazasu bata lokacin su su zo har da na wata kasa ba idan ba gaskiya bane. [They are very serious people] a sanin data yi musu. Auren kuma ba da kowa ba sai UNCLE YAREEMA! Yariman da ta yi wa farin sani, uban dakinta mijin Aisha-Sultana. Yanzu ya tashi daga mijin Sultana ita kadai, ya koma mijinsu su biyu. Da wane karfin zuciya za ta iya karbar wannan sauyin rayuwar na bagatatan da ya zo mata rana daya?
Ta tura kanta karkashin filo tana ta kuka, wani irin kuka wanda tun lokacin da Fulani ta sanar da ita zancen auren ba ta yi shi ba sai yanzu. Yanzu data ji ana shirye-shiryen biki kain da nain daga kowanne bangare.
Daga bakin kofa ta ji ana sallama da wata irin murya cike da doki da zakuwa ga son ta bude. Muryar da ba za ta taba mantawa ba. Ko mutuwa ta yi ta dawo bazata kasa shaida muryar Hanne ba, Hannenta, Hannen Tsanyawa! Diyar Innar Hanne da Baba Saleh.
Ai ba ta san lokacin da ta isa ga kofa ta bude ta da sauri ba.
Hanne da Saade aka tsaya ana kallon-kallo, kafin su runtuma da gudu su rungume juna tsam tsam.
Cikin yan kallon sakanni da suka yi wa juna, kowacce ta karanto irin sauyin rayuwar da ke tare da yar uwarta. Bi maana, Hanne ta gano tarin sauyi na ci gaba da nasarar rayuwa a tare da Saadenta, domin inda a hanya ta ganta ba za ta gane ta ba, to dadin abun mahaifiyarta Fulani ce da kanta ta tabbatar mata Saade na cikin dakin nan a kwance, in ta yi magana ta ji ita ce za ta bude mata.
A yayin da Saade ta hango tarin nakasu da koma baya a rayuwar Hannenta, ta zama kamar mai shekaru arbain bayan ko ashirin ba su rufa ba. Ta yi baki; ta rame; ga goyon wani katon yaro a bayanta wanda da gani ka san ya wuce goyo domin har rinjayarta yake. Saade ta soma kokarin kwanto dan daga bayanta don Hanne ta ji dadin zama, suka karasa bakin gado suka zauna suna hawaye.
Ina Baba Saleh?
Babban falon saukar bakin Fulani na musamman aka bude musu, kuyangin Fulani sai shige da fice suke suna shirya abinci na alfarma. Sai hirarrakinsu ke tashi cikin kasaita da taushin murya kamar ba magana ke tashi a falon ba sabida yadda suke yin ta cikin nutsuwa da salama. Sassan Fulani Bilkisu ya game da kamshin turaruka na alfarma, wannan na wane wannan. Ya kuma cakude da na wuta irin nasu na barebarin usli, ga sanyi da rabar iya kwandishan na ratsa su.
Ba jimawa Fulanin Askirama ta shigo cikin falon, as usual cikin kwalliya ta alfarma, ta fi kowacce iya tsara kwalliya cikin matan Mai Askira kamar yadda duk ta fi su kuruciya da daukar ido. Da faraa sosai wadda ta fiddo hakoran Makkanta na danyen gold guda biyu ta ke musu barka da zuwa. Ta dubi Mairam-Murjanatu cikin jin dadi ta ce,
Har da mutanen Istanbul? Lallai kuna ji da wannan yar kanwa taku, ga shi ta shige daki ta rufe balle ku gaisa.
Ya Maira ta ce, Kyale Saadatu kin ji? Kunya ce irin ta Baggara, me ake da amaryar da babu kunya? We really appreciate, muna nan tare har abada ai.
Mairam Murjanatu ta muskuta cikin lallausar royal chair three seater da take zaune a kai, ta ce,
Shin wane shiri ki ka yi Fulani game da biki ki gaya mana mu ji?
Fulani ta yi dan murmushi ta ce, Ban shirya komai ba. Na bar muku wuka da nama, ku ne Yayyenta kuma surukanta. Ni ina gefe yar kallo ce.
Yaa Maira ta ce, To madallah da wannan girma da anka ba mu, mu kuma za mu shirya mashahurin biki na alada, wanda za a dade baa manta a masarautar nan ba. Za mu huce na auren farko da ba mu samu yi ba.
Daga nan Fulani ta yi umarni a zo a yi serving dinsu abinci.
Sun dade suna tsare-tsare da shirye-shiryen yadda abubuwa za su gudana a junansu, bayan sun gama cin abinci. Fulani ba ta saka musu baki sai dai ta raka da eh ko aah.
Yaa Maira ta dubi kannenta su Murjanatu ta ce.
“Kamar yadda kuka riga kuka sani a aladar bikin gidan nan za mu fara da sakun lalle ranar laraba, alhamis za mu yi nakiya, jumaa wushe-wushe, ranar asabar ake daurin aure, to tunda an riga an daura ba shiri, to a ranar ne za mu yi kelatul (wanke kai da kitso na amarya), sannan mu yi Biji Ginata (ana shimfida tabarmi ne a ranar a ajiye amarya ana kida ana wakoki bayan an yi mata kwalliyar masarauta.
Ranar lahadi za mu yi kaulu na amarya da ango da safe (kaulu shi ne, zaa ajiye miyar yauki a gaban amarya bayan an mata kitso da kwalliya, Baaba za su goyo amarya (sisters din Maimartaba su ne Baaba) su kai ta wajen Kaulu, yan uwa da iyaye su dinga dibar wannan miyar yaukin suna shafa mata. Da daya da daya kowa zai zo yana shafa mata yana ajiye wa amarya kyauta, wasu har gold suke badawa, wasu iphone ko mota ya danganta da mukamin mutum a masarautar, wasu kuma kyautar kudade suke yi, kaulu kenan.
Da yammacin lahadi kuma za mu yi ‘dubdo’, wato wunin biki a gidan amarya bayan an kai ta ranar asabar da daddare (a wannan ranar yan uwa da iyaye za a wuni ana shige da fice a gidan amarya.
Ke kuma Fulanin Maimartaba ke ce da alhakin yin Miskero (abincin da ake kai wa gidan amarya ranar wunin) wanda jamaa da ke shiga da fita a gidan za su ci.
Sannan a satin bikin gabadaya har ila yau ke za ki dinga ciyar da amarya da ango abinci mai kyau. Har zuwa ranar da za a kai amarya, wato asabar.
Idan asabar ta zagayo kuma ana ‘tulur’, wato sati daya da kai amarya, ranar ne ke da kawayenki (Fulani Bilkisu) da yan uwan amarya za ku je gidan amarya, mu kuma za mu yi mata kwalliya, sai a saka mata muciya a hannu, a ranar za ta fara girki kenan, ana wakoki da raye-raye, a ci a sha, to daga nan biki ya kare.
Ranar asabar kuma za mu kawo lefe.
Fulani ta ce, Turkashi, wani aiki sai Amale, bikin Kanuri sai Askira! Allah ya sa muna da rabon gani.
Aka yi adduoi aka shafa, bayan mazan ma sun yi nasu tsare tsaren, sannan duk suka fara watsewa. Amma sai da daya daga cikin kannen Yarima da ake kira Houdda yar dakin Yakirjinoma ta je har kofar dakin Saade ta yi magana ta hudar kofar dakin tamkar mai yin waka cikin harshen Kanuri.
Ki gama boyon amarya, kin riga kin zo hannu, da sannu za mu yi miki kaulu, kelatul, biji ginata da tulur, sannan mu damka wa Yarima ke.
Murjanatu ta zuba mata duka a baya [dundu], ta ce, Houdda kar da ki tsoratata ta kara kunshewa a daki duk zafin nan da ake yi, in kika firgita masa amarya ke da shi ne, kin fi kowa sanin halin sa.
Saade da ke cikin daki duk tana jinsu ba ta san sanda ta fashe da kuka ba..
Da gaske dai ya tabbata an yi mata auren kenan, this is the reality da take ta kokawa da zuciyar ta wajen yarda da shi. Take yaudarar kanta da kanta da cewa mafarki ne. Iyalin Askirama bazasu bata lokacin su su zo har da na wata kasa ba idan ba gaskiya bane. [They are very serious people] a sanin data yi musu. Auren kuma ba da kowa ba sai UNCLE YAREEMA! Yariman da ta yi wa farin sani, uban dakinta mijin Aisha-Sultana. Yanzu ya tashi daga mijin Sultana ita kadai, ya koma mijinsu su biyu. Da wane karfin zuciya za ta iya karbar wannan sauyin rayuwar na bagatatan da ya zo mata rana daya?
Ta tura kanta karkashin filo tana ta kuka, wani irin kuka wanda tun lokacin da Fulani ta sanar da ita zancen auren ba ta yi shi ba sai yanzu. Yanzu data ji ana shirye-shiryen biki kain da nain daga kowanne bangare.
Daga bakin kofa ta ji ana sallama da wata irin murya cike da doki da zakuwa ga son ta bude. Muryar da ba za ta taba mantawa ba. Ko mutuwa ta yi ta dawo bazata kasa shaida muryar Hanne ba, Hannenta, Hannen Tsanyawa! Diyar Innar Hanne da Baba Saleh.
Ai ba ta san lokacin da ta isa ga kofa ta bude ta da sauri ba.
Hanne da Saade aka tsaya ana kallon-kallo, kafin su runtuma da gudu su rungume juna tsam tsam.
Cikin yan kallon sakanni da suka yi wa juna, kowacce ta karanto irin sauyin rayuwar da ke tare da yar uwarta. Bi maana, Hanne ta gano tarin sauyi na ci gaba da nasarar rayuwa a tare da Saadenta, domin inda a hanya ta ganta ba za ta gane ta ba, to dadin abun mahaifiyarta Fulani ce da kanta ta tabbatar mata Saade na cikin dakin nan a kwance, in ta yi magana ta ji ita ce za ta bude mata.
A yayin da Saade ta hango tarin nakasu da koma baya a rayuwar Hannenta, ta zama kamar mai shekaru arbain bayan ko ashirin ba su rufa ba. Ta yi baki; ta rame; ga goyon wani katon yaro a bayanta wanda da gani ka san ya wuce goyo domin har rinjayarta yake. Saade ta soma kokarin kwanto dan daga bayanta don Hanne ta ji dadin zama, suka karasa bakin gado suka zauna suna hawaye.
Ina Baba Saleh?