Sashe 10
Masarautar Mu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Raheemah Kyari, ta yi wani irin lallausar murmushi. Ta kama hannayen Saade ta rike cikin nata.
“inda kowacce mace take kai mijin ta Saadatu! Ina ma ni ce ke Saade! Ki yarda ba tun yau ba cewa you are among the luckiest. Auren matured men shi ne aure, wadanda suka san ciwon kansu, ki rabu da samarin nan yan rawar kai ki kama mijinki da iyayen ki suka zaba miki kin ji? What is your own business da rayuwar matar sa?
Kuma tunda Fulani ta ce ya raba muku gida, kuma ya amince, ina ruwanki da matarsa? Wannan rayuwar su ce shi da ita bai shafe ki ba.”
Saade ta zumburo baki, Raheemah ba za ki gane ba. I have no feelings a kan Yareema Sageer, na dauka zaman auren sai da feelings din soyayya yake yiwuwa???
Raheema ta girgiza kai, ta ce, inji wa? Saadatu, ki gode wa Allah kawai, ki kuma hada da addua, ki roki Allah ya sanya miki soyayyar mijinki, kuma zabin iyayenki. Soyayya da kike ambato shirme ce, cike take da unbearable challenges, aure daban soyayya daban, sai kin yi auren soyayyar in gishiri ya sauka daga kan kaza za ki gane shayi ruwa ne.
Above all kin ce kina ganin girman Yareema, to magana ta kare. Along the way soyayyar za ta zo, irinki in ku ka tashi soyayyar ma mahaukaciya ku ke yi, kuma makauniya, tunda kin ce ba ki ga alamun shi yana kin auren ba.
Muryar Saade abin tausayi ta ce, Sai ma kin ji bakar maganar da ya gaya min da na ce ba zan koma Abuja ba zan gudu kauyenmu he was like (in yi ta gudu, in fi ruwa gudu, giya in shirya sha tare da matarsa) meaning bai dauki maganganun nawa da wani muhimmanci ba.
Raheema ta yi dariya sosai, ta ce.
I would like to see Yarima Sageer. Sister you are blessed for having him as a husband, ina son brave men, wadanda suka yarda da kansu, cika baki ko rikicin mace ba ya razana su su ja da baya a kan soyayyar su. Ni ma sai in ce,
Sai kin dawo, a gaida mutanen Tsanyawa.
Saade ta kai mata bugu ta goce tana mata dariya. Muryar ta abin tausayi tace.
Wato dai Raheema kema kina bayan in auri mai mata ko? Ta je bar ta dawo ta yi min dan karen duka?
Dariya sosai Raheema ta sake yi, ta ce, Tunda ki ka ce ga inda ya auro ta kuma ga asalinta me ye abun mamaki don ta sha giya? Su fa yadda muke shan soft drinks, haka suke shanta don baki taba fita ketare bane, canjin addininta ba zai sa ta iya dainawa farat daya ba, tunda dai ba shi yake sha ba shi kenan falillahil hamdu, ki yi mata addua Allah ya sa tana da rabon dainawa.
Sai kiran sallar asuba suka ji a kunnuwan su, dole suka mike don bada farali. Daga nan kuma suka kwanta, Hanne sai barcinta ta ke hankali kwance bisa katuwar katifa ita da danta Naziru.
*****
Washegari aka tashi da event na farko, wato sakun lalle. Masarautar ta cika ta batse da yan uwa da abokan arziki da baki da aka gayyato daga masarautu daban-daban, ga kuma alummar garin Askira wadanda ma ba a gayyata ba. Da ma in dai biki na gidan sarki ne ba sai an gayyace su ba, kwansu da kwarkwatarsu suke tahowa daga gidajensu zuwa gidan Sarki.
To balle auren Yareema Sageer kuma wanda Maimartaba da kanshi ya shelanta gayyatar ga kowa da ke Askira, bayan saukowa sallar jumaa a babban masallacin jumaa. Don haka ba a taba ganin taron bikin da ya hada jamaa irin na yau ba a masarautar gabadaya. Tun daga kan auren su Yaa Maira har zuwa kan na yar sarki ta karshe da aka aurar Najaatu.
An saka amarya a lalle lafiya, Raheema da Hanne da kanwar Raheema Sarina sune kawayen amarya. Washegari alhamis aka yi NIYA wato ranar yin royal snacks su nakiya, alkali, dubulan, bakilawa da sauransu daro-daro don raba wa mutane.
Ranar jumaa aka yi WUSHE-WUSHE. A babban filin dake cikin fada aka kira decorators suka tsara shi yayi kyau sosai. Wushe-wushe shine wuri daya da Yareema da Sa'ade Zasu hadu a duk tsawon bikin su, makada ne aka gaiyyato daban daban daga garuruwa daban-daban ciki har da HajjaGumsu da yaran ta da suka zo daga Maiduguri. Sai da aka taru ana kade-kade ango ya zo cikin manyan kaya da abokan shi karkashin rakiyar Awaisu Ibrahim Waziri da kuma sisters din shi mata su Mairam Murjanatu, Yaa Maira and co.zagaye da shi cikin laffaya mai hasken sararin samaniya suna rike da kaskon turaren wuta suna turara shi, makadan fada na biye da su,suna kide-kide da bushe-bushe suna wake Yarima da amarya Saadatu har su ka kai shi mazaunin da aka tanadar musu shi da Saadatun.
Abokanen shi kuma aka yi musu shimfidun kilishi na alfarma daga gefen sa, sannan su yan uwan shi mata su kuma suna zaune inda aka tanadar musu.
Sai aka cigaba da wasa da kide-kiden cikin zakuwar fitowar amarya, wanda yawanci sai an dan ja lokaci sosai kawai dan a ja wa ango rai, haka aladar bikin masarautar Askira ke gudana a kowanne bikin dan sarki.
Saade an shirya ta cikin laffaya an rufe ta ruf har kai. Sannan kawayen ta su Rahimah da Hanne sun saka ankon dongasho da su murjani sun rike kaskon turarukan wuta suka sako ta a tsakiya kamar yadda aka koyar dasu.Maman Rahimah da Innar Hanne na rike da ita cikin rakiyar kide-kide har aka kai ta aka zaunar a gefen Yarima Sageer, wanda a lokacin da Saade ta zauna a gefen sa sai da ya dauke numfashin sa na wucin-gadi. Kawayen ta kuma by her side akan shimfidundake kallon na abokan ango.
Daga nan sai aka cigaba da kide-kide da wasanni.Saade bata yarda sun hada ido da Yarima ba duk kokarin sa ga son faruwar hakan, bata ma bude fuskarta daga cikin laffaya ba, duk kokarin Yarima Sageer na son gano halin da kwayar idon ta ke ciki a wannan lokacin hakan bai yiwu ba.
Tana jin sanda Uncle Sageer da yan uwan sa mata da maza da abokai suka yi ta yi mataruwan liki. Har tsakar dare ana wannan shagalin kafin taron wushe-wushe ya tashi. Kuma Yarima bai samu damar ganin Saadeprivately ba har su Maman Rahimah suka kama ta suka koma cikin gida.
Ranar asabar kuma aka yi KELATUL wato aka wanke wa amarya gashi aka yarfa mata kitson bare-bari kanana-kanana sun kai guda dari uku. Da yammacin ranar kuma aka yi biji-ginata inda aka shimfida manyan tabarmi aka ajiye amarya a tsakiya ana kida ana wakoki irin na barebarin Askira. Bayan an yi mata kwalliyar masarauta.
Ranar lahadi aka yi kaulu na amarya da na ango da safe. Kaulu shi ne za a ajiye miyar yauki a gaban amarya bayan an mata kitso da kwalliya. Baaba suka goya amarya suka kai ta filin da ake yin kaulu. Yan uwan Yareema na ciki daya da na sauran dakunan suka dinga dibar wannan miyar yaukin suna shafa mata, sannan daya bayan daya suka zo suna ajiye mata kyaututtuka na bajinta haka sauran matan Maimartaba.
Da yammacin ranar aka yi dubdo, wato wunin biki a harshen Hausa. Biki ya yi biki ba ka jin komai a masarautar Askira sai kade-kade da bushe-bushen algaita. Duk wadannan events din da ake yi ango bai ga fuskar amarya ba, kuma Fulani Bilkisu ita ke da alhakin yin miskero, wato abincin da ake kai wa gidan amarya. Kuma ita ke ciyar da ango da amarya dadadan girke-girke masu kara lafiya da kuzari.
In ta girka sai kuyanginta su kai sassan Yareema su ci shi da Awaisu. Korafi kam Awaisu ya sha shi gurin Yareema, kan cewa shi fa bikin nan ya ishe shi hayaniya ta yi masa yawa. A ba shi amaryarshi kawai su kama hanya. Shi ba auren fari ba to wadannan aladun duk na menene?
Awaisu sai dai ya yi murmushi don ya gama gane Yareema Sageer ya karbi auren nan da hannu bibbiyu. Har fiye da auren sa da baturiyar sa mai kananan ido. Auren da yake kira na soyayya kuma babu ya shi. Abin da bai sani ba, kuma yake matukar son sani shi ne, da ma can Yareema yana son Saade ne ko sai da aka ce an aura masa ita ya fara son ta??
Sai da Baaba (kannen Maimartaba mata) da kannen Ya Gumsu suka shigo tafiya da amarya ne idonta ya karasa raina fata. Domin a baya kallon komai take matsayin almara ko mafarki. Saadatu ta kankame Fulani tana ihu sosai ita ba inda za ta je ta bar Fulani.
Sai yanzu ne ta tabbatar da gaske an yi mata aure, kuma ba da kowa ba da Yariman Askira, Uncle Yareeman da ta ke girmamawa fiye da kowa in ka dauke iyayenta, Dr. Sageer a NTNU, kuma mijin Aisha-Sultana.
A karshe Baaba sai goya amarya suka yi tana kuka tana komai, kannen Yareema mata su Houdda sai tsiya suke mata, ko irin nasihar nan ta uwa Fulani ba ta samu damar yi mata ba sabida kukan da ta ke tun safe ya daga mata hankali. Su Mama (Babar Raheema) da su Raheeman suna gidan amarya tun safe inda ake aikin jere da kafi.
Duk wasu furnitures da aka zuba a sassan Saade dake gidan Yarima Alhaji Kyari ne ya taho da su tafiyayyu daga kasar Italiya, wadanda Maimartaba ya yi mata an wuce mata da su Abuja.
******
“inda kowacce mace take kai mijin ta Saadatu! Ina ma ni ce ke Saade! Ki yarda ba tun yau ba cewa you are among the luckiest. Auren matured men shi ne aure, wadanda suka san ciwon kansu, ki rabu da samarin nan yan rawar kai ki kama mijinki da iyayen ki suka zaba miki kin ji? What is your own business da rayuwar matar sa?
Kuma tunda Fulani ta ce ya raba muku gida, kuma ya amince, ina ruwanki da matarsa? Wannan rayuwar su ce shi da ita bai shafe ki ba.”
Saade ta zumburo baki, Raheemah ba za ki gane ba. I have no feelings a kan Yareema Sageer, na dauka zaman auren sai da feelings din soyayya yake yiwuwa???
Raheema ta girgiza kai, ta ce, inji wa? Saadatu, ki gode wa Allah kawai, ki kuma hada da addua, ki roki Allah ya sanya miki soyayyar mijinki, kuma zabin iyayenki. Soyayya da kike ambato shirme ce, cike take da unbearable challenges, aure daban soyayya daban, sai kin yi auren soyayyar in gishiri ya sauka daga kan kaza za ki gane shayi ruwa ne.
Above all kin ce kina ganin girman Yareema, to magana ta kare. Along the way soyayyar za ta zo, irinki in ku ka tashi soyayyar ma mahaukaciya ku ke yi, kuma makauniya, tunda kin ce ba ki ga alamun shi yana kin auren ba.
Muryar Saade abin tausayi ta ce, Sai ma kin ji bakar maganar da ya gaya min da na ce ba zan koma Abuja ba zan gudu kauyenmu he was like (in yi ta gudu, in fi ruwa gudu, giya in shirya sha tare da matarsa) meaning bai dauki maganganun nawa da wani muhimmanci ba.
Raheema ta yi dariya sosai, ta ce.
I would like to see Yarima Sageer. Sister you are blessed for having him as a husband, ina son brave men, wadanda suka yarda da kansu, cika baki ko rikicin mace ba ya razana su su ja da baya a kan soyayyar su. Ni ma sai in ce,
Sai kin dawo, a gaida mutanen Tsanyawa.
Saade ta kai mata bugu ta goce tana mata dariya. Muryar ta abin tausayi tace.
Wato dai Raheema kema kina bayan in auri mai mata ko? Ta je bar ta dawo ta yi min dan karen duka?
Dariya sosai Raheema ta sake yi, ta ce, Tunda ki ka ce ga inda ya auro ta kuma ga asalinta me ye abun mamaki don ta sha giya? Su fa yadda muke shan soft drinks, haka suke shanta don baki taba fita ketare bane, canjin addininta ba zai sa ta iya dainawa farat daya ba, tunda dai ba shi yake sha ba shi kenan falillahil hamdu, ki yi mata addua Allah ya sa tana da rabon dainawa.
Sai kiran sallar asuba suka ji a kunnuwan su, dole suka mike don bada farali. Daga nan kuma suka kwanta, Hanne sai barcinta ta ke hankali kwance bisa katuwar katifa ita da danta Naziru.
*****
Washegari aka tashi da event na farko, wato sakun lalle. Masarautar ta cika ta batse da yan uwa da abokan arziki da baki da aka gayyato daga masarautu daban-daban, ga kuma alummar garin Askira wadanda ma ba a gayyata ba. Da ma in dai biki na gidan sarki ne ba sai an gayyace su ba, kwansu da kwarkwatarsu suke tahowa daga gidajensu zuwa gidan Sarki.
To balle auren Yareema Sageer kuma wanda Maimartaba da kanshi ya shelanta gayyatar ga kowa da ke Askira, bayan saukowa sallar jumaa a babban masallacin jumaa. Don haka ba a taba ganin taron bikin da ya hada jamaa irin na yau ba a masarautar gabadaya. Tun daga kan auren su Yaa Maira har zuwa kan na yar sarki ta karshe da aka aurar Najaatu.
An saka amarya a lalle lafiya, Raheema da Hanne da kanwar Raheema Sarina sune kawayen amarya. Washegari alhamis aka yi NIYA wato ranar yin royal snacks su nakiya, alkali, dubulan, bakilawa da sauransu daro-daro don raba wa mutane.
Ranar jumaa aka yi WUSHE-WUSHE. A babban filin dake cikin fada aka kira decorators suka tsara shi yayi kyau sosai. Wushe-wushe shine wuri daya da Yareema da Sa'ade Zasu hadu a duk tsawon bikin su, makada ne aka gaiyyato daban daban daga garuruwa daban-daban ciki har da HajjaGumsu da yaran ta da suka zo daga Maiduguri. Sai da aka taru ana kade-kade ango ya zo cikin manyan kaya da abokan shi karkashin rakiyar Awaisu Ibrahim Waziri da kuma sisters din shi mata su Mairam Murjanatu, Yaa Maira and co.zagaye da shi cikin laffaya mai hasken sararin samaniya suna rike da kaskon turaren wuta suna turara shi, makadan fada na biye da su,suna kide-kide da bushe-bushe suna wake Yarima da amarya Saadatu har su ka kai shi mazaunin da aka tanadar musu shi da Saadatun.
Abokanen shi kuma aka yi musu shimfidun kilishi na alfarma daga gefen sa, sannan su yan uwan shi mata su kuma suna zaune inda aka tanadar musu.
Sai aka cigaba da wasa da kide-kiden cikin zakuwar fitowar amarya, wanda yawanci sai an dan ja lokaci sosai kawai dan a ja wa ango rai, haka aladar bikin masarautar Askira ke gudana a kowanne bikin dan sarki.
Saade an shirya ta cikin laffaya an rufe ta ruf har kai. Sannan kawayen ta su Rahimah da Hanne sun saka ankon dongasho da su murjani sun rike kaskon turarukan wuta suka sako ta a tsakiya kamar yadda aka koyar dasu.Maman Rahimah da Innar Hanne na rike da ita cikin rakiyar kide-kide har aka kai ta aka zaunar a gefen Yarima Sageer, wanda a lokacin da Saade ta zauna a gefen sa sai da ya dauke numfashin sa na wucin-gadi. Kawayen ta kuma by her side akan shimfidundake kallon na abokan ango.
Daga nan sai aka cigaba da kide-kide da wasanni.Saade bata yarda sun hada ido da Yarima ba duk kokarin sa ga son faruwar hakan, bata ma bude fuskarta daga cikin laffaya ba, duk kokarin Yarima Sageer na son gano halin da kwayar idon ta ke ciki a wannan lokacin hakan bai yiwu ba.
Tana jin sanda Uncle Sageer da yan uwan sa mata da maza da abokai suka yi ta yi mataruwan liki. Har tsakar dare ana wannan shagalin kafin taron wushe-wushe ya tashi. Kuma Yarima bai samu damar ganin Saadeprivately ba har su Maman Rahimah suka kama ta suka koma cikin gida.
Ranar asabar kuma aka yi KELATUL wato aka wanke wa amarya gashi aka yarfa mata kitson bare-bari kanana-kanana sun kai guda dari uku. Da yammacin ranar kuma aka yi biji-ginata inda aka shimfida manyan tabarmi aka ajiye amarya a tsakiya ana kida ana wakoki irin na barebarin Askira. Bayan an yi mata kwalliyar masarauta.
Ranar lahadi aka yi kaulu na amarya da na ango da safe. Kaulu shi ne za a ajiye miyar yauki a gaban amarya bayan an mata kitso da kwalliya. Baaba suka goya amarya suka kai ta filin da ake yin kaulu. Yan uwan Yareema na ciki daya da na sauran dakunan suka dinga dibar wannan miyar yaukin suna shafa mata, sannan daya bayan daya suka zo suna ajiye mata kyaututtuka na bajinta haka sauran matan Maimartaba.
Da yammacin ranar aka yi dubdo, wato wunin biki a harshen Hausa. Biki ya yi biki ba ka jin komai a masarautar Askira sai kade-kade da bushe-bushen algaita. Duk wadannan events din da ake yi ango bai ga fuskar amarya ba, kuma Fulani Bilkisu ita ke da alhakin yin miskero, wato abincin da ake kai wa gidan amarya. Kuma ita ke ciyar da ango da amarya dadadan girke-girke masu kara lafiya da kuzari.
In ta girka sai kuyanginta su kai sassan Yareema su ci shi da Awaisu. Korafi kam Awaisu ya sha shi gurin Yareema, kan cewa shi fa bikin nan ya ishe shi hayaniya ta yi masa yawa. A ba shi amaryarshi kawai su kama hanya. Shi ba auren fari ba to wadannan aladun duk na menene?
Awaisu sai dai ya yi murmushi don ya gama gane Yareema Sageer ya karbi auren nan da hannu bibbiyu. Har fiye da auren sa da baturiyar sa mai kananan ido. Auren da yake kira na soyayya kuma babu ya shi. Abin da bai sani ba, kuma yake matukar son sani shi ne, da ma can Yareema yana son Saade ne ko sai da aka ce an aura masa ita ya fara son ta??
Sai da Baaba (kannen Maimartaba mata) da kannen Ya Gumsu suka shigo tafiya da amarya ne idonta ya karasa raina fata. Domin a baya kallon komai take matsayin almara ko mafarki. Saadatu ta kankame Fulani tana ihu sosai ita ba inda za ta je ta bar Fulani.
Sai yanzu ne ta tabbatar da gaske an yi mata aure, kuma ba da kowa ba da Yariman Askira, Uncle Yareeman da ta ke girmamawa fiye da kowa in ka dauke iyayenta, Dr. Sageer a NTNU, kuma mijin Aisha-Sultana.
A karshe Baaba sai goya amarya suka yi tana kuka tana komai, kannen Yareema mata su Houdda sai tsiya suke mata, ko irin nasihar nan ta uwa Fulani ba ta samu damar yi mata ba sabida kukan da ta ke tun safe ya daga mata hankali. Su Mama (Babar Raheema) da su Raheeman suna gidan amarya tun safe inda ake aikin jere da kafi.
Duk wasu furnitures da aka zuba a sassan Saade dake gidan Yarima Alhaji Kyari ne ya taho da su tafiyayyu daga kasar Italiya, wadanda Maimartaba ya yi mata an wuce mata da su Abuja.
******