Sashe 3
Masarautar Mu Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ban da munafurci me ye na boye mana cewa yarta ce? Ina ruwanmu don ta taba aure? Gori yana tsiro a goshi ne? Duk wata harka ta kishiya sai kin samu dunkulallen munafurci a ciki. Ashe ma a bazawara ta zo shi ne ta bi ta juye kan tsoho, kinibabbiya, haba! Ni fa in ce wannan so da Askirama ke wa yarinyar nan da walakin, ashe agola diyar mowa ce, to muna jira mu ga wan baban yarinyar da idanunmu don mu tabbatar ba shegiyar bace.
Kuma shi Yareema shi ke nan ba zai auri yar sarauta ba, auren misali sai dai ya gani a wurin tsararrakin sa? Alhalin ba gata aka fi shi ba? Daga jinsin yahudawa da masu kanan ido sai jinin talakka agola a matsayinsa na Yarima mai jiran gadon Askira?
Ya Maira ta yi kasa da murya ta ce.
Yaa Gumsu, gara talaka, agola tushen musulunci tashin musulunci a kan tubabben da aka ce daga kwalba ta ke yi a bar, sallar ma ta daina. Ki gode wa rahmar Allah Ya Gumsu alheri Askirama ke nufinmu da shi. Yariman ai ba wankakke ba ne kin fi kowa sani. 'Yar Bilkisu aka cutada auren Yarima ba Yarima ba.
Ni tun ganina da yarinyar na farko na san za ta zame mana wani jigo cikin zuriar mu. Tana da charisma mai yawa. Tana da wisdom bayyananne. Allah ne bai taba kai hankali na kan Yarima ba, musamman da ya zo ya yi auren sa daga baya. Amma na yi zaton Ashgar zaa bai wa, sai dai lalurar sa ba za ta bari ya yi aure ba,
Jiki na ya dade da bani hakan cewa bazata wuce mazan gidan nan ba koda ba daga dakin nan ba.
Yaa Gumsu Ta kyabe baki tace Mairam ki fita ido na in rufe, na bi wisdom da gudu na tattake babu takalmi a kafata me yasa baa baiwa dakin Yaa Kirjiloma ba? Uban wa yace miki Ashgar bazai iya aure ba? Sai Yarima na dana dora dukkan buri akan sa da yayan da zai haifa? Kawai sai kuka ya kwace mata.
Yaa Maira ta rasa yadda zata yi da Yaa Gumsu, duk dabarar ta ta kare. Haka ta yi ta tausar Ya Gumsu tana nuna mata muhimmancin wannan aure ga mutuncin Yarima da rayuwarsa, da alkhairin da ta ke hangowa a cikinsa na kimtsuwar Yarima.
Yaa Gumsu baki da masaniyar cewa har yanzu Yarima Sageer bai bar bin mata a garin Abuja ba? In baki sani ba ki sani, in kuma kin sani ki tuna.
Ko jikin ta ya yi sanyi dai ba ta nuna ba, Ya Gumsu akwai Ki-Fadi, ko ma me ye ba za ta so hada jini da Bilkisu ba gara dan kowa a kan nata. Da ta rasa hujjar kamawa sai ta ce da Yaa Maira.
Shi ke nan kuma shi ba zai yi aure irin na gidansu ba? Ba zai yi auren martaba (auren sarauta) ba sabida ubansa na auren uwarta?
Yaa Maira ta sake kwantar da murya, Allah ya taimaki Gumsun Askira, ai akwai sauran damarmaki. Yarima na da gurbin wasu matan biyu bayan Saadatu, ki ka sani ko duka ya auri yayan masarautu a sauran guraben yadda kike masa shaawa?
A nan ne Ya Gumsu ta yi ajiyar zuciya, don shaf bacin rai ya sa ta manta da hakan, yayi zabin sa ya yi zabin mahaifin sa dole nan gaba kadan ya yi nata zabin. Ta ce,
Yanzu ki ka yi magana Mairam, daga yau zan fara binciken yayan babban gida wa Yarima. Ba zai yiwu a ce duka aurarrakinsa babu zabina a ciki ba.
Yaa Maira ta ce, Oh ni ya su. Amma Ya Gumsu ki bari ki ga kamun ludayin zaman nasu tukunna, kafin ki nema masa sabon aure. Yarima kodayake basarake to bature ne na gani kashe ni. Ba zai so da kuruciyarsa a cika masa gida da mata ba. Ki yi hakuri ki daga masa kafa zuwa wani lokacin.
Haka ta yi ta lallashin Ya Gumsu cikin kwantar da kai da lalama, kodayake da ma cikin yayanta kakaf Yaa Maira ce kadai ta iya tafiyar da ita cikin hikima duk taurin kanta. Ko dai ba ta sauko duka ba, to Yaa Maira ta yi nasarar dakushe kiyayyarta da auren kashi talatin cikin dari. Tunda ta ji Saade ba shegiya ba ce sannan yar Fulani ce ta cikinta ba yar riko ba kamar yadda suke tsammani. Kuma ta ji cewa dangin ubanta za su bayyana kansu.
Wannan ne kadai ya sassauta zuciyar Ya Gumsu har ta yarda ta amince musu su je su shirya biki nasu na aladar masarautar Askira. Amma ita tana nan sassan ta ko waje bazata leka ba.
Don farin ciki Ya Maira a take ta hau buga wa kannenta mata da maza waya ta ce duk su hadu yau a Unguwar Fulani Bilkisu kan shirin bikin Yareema bayan sallar isha’.
Kafin lokacin Mairam-Murjanatu ta iso. Ko hutawa ba ta yi ba suka dinga firfitowa daga sassan iyayensu mata zuwa na Fulani Bilkisu.
Da ma kuma tun da yamma Yaa Maira ta aika wa da Fanna sakon zuwan nasu. Fanna kuma ta gaya wa uwargijiyarta. Don haka ba su zauna ba tun lokacin suke dafe-dafen abinci na alfarma domin saukar su Yaa Maira da sauran yayan Askirama maza.
Humaira ce kadai ta ki zuwa don ta shiga matukar damuwa da wannan auren da aka daura. Fulani Hibbani kuma ta ce ta raba kanta da wahala, fadan da ya fi karfin ka ka maida shi wasa, ta fita batun Fulani Bilkisu da yarta, don sun gama da ubanta saidai wani sarkin ba shi ba, in kuma ta ki ji ita ce a wahale.
Saade da ma ba ta yarda ta bar dakinta a bude tun daga lokacin da suka yi magana da Fulani a kan aurenta da Yareema, ita kanta Fulanin haushi take bata yanzu don ta lura ta gama mika wuya ga auren sabida son da take wa mijin ta Askirama, kuma bata dauki shirin sa da wasa ba, ko don bata san waye Dr. Sageer ba? Ko kuma bata dauki hakan da muhimmanci ba? Aisha Sultana bazata yi masa karya ba da ta ce hes committing adultery kuma SAI YA BARI ITAMA ZATA BAR GIYA, wannan ne gidan da Fulani ta amince a kai ta kuma cikin mutanen da take mata fatan rayuwa ta har abada?
Ita kuma Fulanin kamar ta san tunanin da take yi sai ta fita sabgarta, shirye-shiryenta ta ke kain da nain, ta ce cikin ran ta,
Allah shine mai shirya bawa bani da tsumi banida dabara sai abinda Allah ya shiryawa rayuwar ki Sa'ade. In kun tafi Abujar ku karata can, ni biki ne a gaba na. dama ai tare kuka zo, don kun koma tare matsayin miji da mata yanzu babu laifi.
To yau ma tana jin su suna maganar kabakin abincin da za a shirya wa su Yaa Maira ita da kuyangin ta wadanda a nan za su ci abincin dare, bata dai ji hakikanin me zai kawo su ba amma taji ana maganar abinci na gani na fada zaayi yayan Askirama gabadayan su, da gudu ta kara murza key din kofar ta duk da dama a kulle ta ke. Kada ma wani ya shigo in da take. A bar ta ta ji da damuwar ta ita kadai tunda babu mai taya ta bakin cikin kaddarar da ta same ta. Karewa ma kowa harkar gaban sa yake yi, dan tausayin ta da Fulani ke ji a farko ta zubar. Abinci wannan Saade ta daina cinsa sai fruits kawai ta ke sha a firjinta, sai ko fresh milk din oldenburger gora-gora idan yunwa ta matsa mata.
Yau kwanaki biyu kenan rabon da ta sa Fulani a idonta. Wayarta ta kashe ta don ta san dole Saidu zai kira ta, ba ta san da wanne baki za ta fara masa bayanin ita matar aure ba ce yanzu, ta san babu kyau mace ta dinga muamala da wani kuma. Ta ce ita matar Uncle Yarima ce ma ai yanzu ai abun kunya ne bayan ta gama yi masa homar Yayan ta ne. Saidu-Saidun ta hakika zata yi kewar sa. Babban tsoron nata shi ne kada Yarima ya kira ta a waya.
Tuna sunansa kadai fadar mata da gaba yake yi. Duk wata kyakkyawar alaka da ke tsakaninsu a baya daga yanzu ta yanke ta. Karatun ma in dai ba hostel zaa maida ita ba ta hakura ta yafe shi har abada. Tana nan kusa da uwarta da kanwarta, a rayuwa wannan shi ne babban kwanciyar hankalinta wato ta gan ta tsakanin Fulani da Zarah.
Bayan ita ma Zaran ko za ta wuni tana buga mata kofa ba za ta bude ba sai Fulani ta zo ta kore ta a wurin.
Kuma shi Yareema shi ke nan ba zai auri yar sarauta ba, auren misali sai dai ya gani a wurin tsararrakin sa? Alhalin ba gata aka fi shi ba? Daga jinsin yahudawa da masu kanan ido sai jinin talakka agola a matsayinsa na Yarima mai jiran gadon Askira?
Ya Maira ta yi kasa da murya ta ce.
Yaa Gumsu, gara talaka, agola tushen musulunci tashin musulunci a kan tubabben da aka ce daga kwalba ta ke yi a bar, sallar ma ta daina. Ki gode wa rahmar Allah Ya Gumsu alheri Askirama ke nufinmu da shi. Yariman ai ba wankakke ba ne kin fi kowa sani. 'Yar Bilkisu aka cutada auren Yarima ba Yarima ba.
Ni tun ganina da yarinyar na farko na san za ta zame mana wani jigo cikin zuriar mu. Tana da charisma mai yawa. Tana da wisdom bayyananne. Allah ne bai taba kai hankali na kan Yarima ba, musamman da ya zo ya yi auren sa daga baya. Amma na yi zaton Ashgar zaa bai wa, sai dai lalurar sa ba za ta bari ya yi aure ba,
Jiki na ya dade da bani hakan cewa bazata wuce mazan gidan nan ba koda ba daga dakin nan ba.
Yaa Gumsu Ta kyabe baki tace Mairam ki fita ido na in rufe, na bi wisdom da gudu na tattake babu takalmi a kafata me yasa baa baiwa dakin Yaa Kirjiloma ba? Uban wa yace miki Ashgar bazai iya aure ba? Sai Yarima na dana dora dukkan buri akan sa da yayan da zai haifa? Kawai sai kuka ya kwace mata.
Yaa Maira ta rasa yadda zata yi da Yaa Gumsu, duk dabarar ta ta kare. Haka ta yi ta tausar Ya Gumsu tana nuna mata muhimmancin wannan aure ga mutuncin Yarima da rayuwarsa, da alkhairin da ta ke hangowa a cikinsa na kimtsuwar Yarima.
Yaa Gumsu baki da masaniyar cewa har yanzu Yarima Sageer bai bar bin mata a garin Abuja ba? In baki sani ba ki sani, in kuma kin sani ki tuna.
Ko jikin ta ya yi sanyi dai ba ta nuna ba, Ya Gumsu akwai Ki-Fadi, ko ma me ye ba za ta so hada jini da Bilkisu ba gara dan kowa a kan nata. Da ta rasa hujjar kamawa sai ta ce da Yaa Maira.
Shi ke nan kuma shi ba zai yi aure irin na gidansu ba? Ba zai yi auren martaba (auren sarauta) ba sabida ubansa na auren uwarta?
Yaa Maira ta sake kwantar da murya, Allah ya taimaki Gumsun Askira, ai akwai sauran damarmaki. Yarima na da gurbin wasu matan biyu bayan Saadatu, ki ka sani ko duka ya auri yayan masarautu a sauran guraben yadda kike masa shaawa?
A nan ne Ya Gumsu ta yi ajiyar zuciya, don shaf bacin rai ya sa ta manta da hakan, yayi zabin sa ya yi zabin mahaifin sa dole nan gaba kadan ya yi nata zabin. Ta ce,
Yanzu ki ka yi magana Mairam, daga yau zan fara binciken yayan babban gida wa Yarima. Ba zai yiwu a ce duka aurarrakinsa babu zabina a ciki ba.
Yaa Maira ta ce, Oh ni ya su. Amma Ya Gumsu ki bari ki ga kamun ludayin zaman nasu tukunna, kafin ki nema masa sabon aure. Yarima kodayake basarake to bature ne na gani kashe ni. Ba zai so da kuruciyarsa a cika masa gida da mata ba. Ki yi hakuri ki daga masa kafa zuwa wani lokacin.
Haka ta yi ta lallashin Ya Gumsu cikin kwantar da kai da lalama, kodayake da ma cikin yayanta kakaf Yaa Maira ce kadai ta iya tafiyar da ita cikin hikima duk taurin kanta. Ko dai ba ta sauko duka ba, to Yaa Maira ta yi nasarar dakushe kiyayyarta da auren kashi talatin cikin dari. Tunda ta ji Saade ba shegiya ba ce sannan yar Fulani ce ta cikinta ba yar riko ba kamar yadda suke tsammani. Kuma ta ji cewa dangin ubanta za su bayyana kansu.
Wannan ne kadai ya sassauta zuciyar Ya Gumsu har ta yarda ta amince musu su je su shirya biki nasu na aladar masarautar Askira. Amma ita tana nan sassan ta ko waje bazata leka ba.
Don farin ciki Ya Maira a take ta hau buga wa kannenta mata da maza waya ta ce duk su hadu yau a Unguwar Fulani Bilkisu kan shirin bikin Yareema bayan sallar isha’.
Kafin lokacin Mairam-Murjanatu ta iso. Ko hutawa ba ta yi ba suka dinga firfitowa daga sassan iyayensu mata zuwa na Fulani Bilkisu.
Da ma kuma tun da yamma Yaa Maira ta aika wa da Fanna sakon zuwan nasu. Fanna kuma ta gaya wa uwargijiyarta. Don haka ba su zauna ba tun lokacin suke dafe-dafen abinci na alfarma domin saukar su Yaa Maira da sauran yayan Askirama maza.
Humaira ce kadai ta ki zuwa don ta shiga matukar damuwa da wannan auren da aka daura. Fulani Hibbani kuma ta ce ta raba kanta da wahala, fadan da ya fi karfin ka ka maida shi wasa, ta fita batun Fulani Bilkisu da yarta, don sun gama da ubanta saidai wani sarkin ba shi ba, in kuma ta ki ji ita ce a wahale.
Saade da ma ba ta yarda ta bar dakinta a bude tun daga lokacin da suka yi magana da Fulani a kan aurenta da Yareema, ita kanta Fulanin haushi take bata yanzu don ta lura ta gama mika wuya ga auren sabida son da take wa mijin ta Askirama, kuma bata dauki shirin sa da wasa ba, ko don bata san waye Dr. Sageer ba? Ko kuma bata dauki hakan da muhimmanci ba? Aisha Sultana bazata yi masa karya ba da ta ce hes committing adultery kuma SAI YA BARI ITAMA ZATA BAR GIYA, wannan ne gidan da Fulani ta amince a kai ta kuma cikin mutanen da take mata fatan rayuwa ta har abada?
Ita kuma Fulanin kamar ta san tunanin da take yi sai ta fita sabgarta, shirye-shiryenta ta ke kain da nain, ta ce cikin ran ta,
Allah shine mai shirya bawa bani da tsumi banida dabara sai abinda Allah ya shiryawa rayuwar ki Sa'ade. In kun tafi Abujar ku karata can, ni biki ne a gaba na. dama ai tare kuka zo, don kun koma tare matsayin miji da mata yanzu babu laifi.
To yau ma tana jin su suna maganar kabakin abincin da za a shirya wa su Yaa Maira ita da kuyangin ta wadanda a nan za su ci abincin dare, bata dai ji hakikanin me zai kawo su ba amma taji ana maganar abinci na gani na fada zaayi yayan Askirama gabadayan su, da gudu ta kara murza key din kofar ta duk da dama a kulle ta ke. Kada ma wani ya shigo in da take. A bar ta ta ji da damuwar ta ita kadai tunda babu mai taya ta bakin cikin kaddarar da ta same ta. Karewa ma kowa harkar gaban sa yake yi, dan tausayin ta da Fulani ke ji a farko ta zubar. Abinci wannan Saade ta daina cinsa sai fruits kawai ta ke sha a firjinta, sai ko fresh milk din oldenburger gora-gora idan yunwa ta matsa mata.
Yau kwanaki biyu kenan rabon da ta sa Fulani a idonta. Wayarta ta kashe ta don ta san dole Saidu zai kira ta, ba ta san da wanne baki za ta fara masa bayanin ita matar aure ba ce yanzu, ta san babu kyau mace ta dinga muamala da wani kuma. Ta ce ita matar Uncle Yarima ce ma ai yanzu ai abun kunya ne bayan ta gama yi masa homar Yayan ta ne. Saidu-Saidun ta hakika zata yi kewar sa. Babban tsoron nata shi ne kada Yarima ya kira ta a waya.
Tuna sunansa kadai fadar mata da gaba yake yi. Duk wata kyakkyawar alaka da ke tsakaninsu a baya daga yanzu ta yanke ta. Karatun ma in dai ba hostel zaa maida ita ba ta hakura ta yafe shi har abada. Tana nan kusa da uwarta da kanwarta, a rayuwa wannan shi ne babban kwanciyar hankalinta wato ta gan ta tsakanin Fulani da Zarah.
Bayan ita ma Zaran ko za ta wuni tana buga mata kofa ba za ta bude ba sai Fulani ta zo ta kore ta a wurin.