← Book details Masarautar Mu Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 19

Sashe 19

Masarautar Mu Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

*****
Har karfe sha biyun dare yana tare da Aisha-Sultana a sabon flat din da ya kama mata a Maitama, jira yake giya ta sake ta, ta wartsake sannan su yi magana. Tunda suka zo ta ke barci, maigadin da ya daukar mata shi ya fiddo duk kayan sanyawarta jaka-jaka daga bayan motar Yareema ya shiga da su ciki, wadanda ya sa Uche ya kwaso mata.
Da ya kashe motarshi ya dauke ta a kafadunsa zuwa cikin apartment din, ya kwantar da ita bisa gado kasancewar ya yi order already an zuba komai na bukata a gidan. Haka ya zauna zaman jiranta ta wartsake, ya tashi ya yi alwala ya yi sallar isha, sannan ya zauna kiraye-kirayen waya, ya gabatar da dukkan uzurorinsa ta waya. Amma duk abin nan da yake Saadatu na makale cikin ransa. Allah-Allah yake Sultana ta farka su yi maganar da yake so su yi, ya tafi wajen Saadatu.
Sulatana ba ita ta farka ba sai karfe sha biyu na dare. Ta yi mika sannan ta hau bude idonta a hankali, sai ta ganta a bakon wuri. Ganin Sageer a gefe yana sallah, sai tsoronta ya ragu. Ta sani ko ma ina ne shi ya kawo ta kenan a lokacin da ta ke cikin maye.
Darling ina ne nan?
Ta tambaya tana hamma.
When did you get back? I missed you!.
Hararar ta ya yi, sannan ya dauke kansa. Can kuma ya dago ya dube ta cikin ido.

“My father saw you drunk!.

Sultana ta zaro ido, Oh dear! Me ya sa ba ka gaya min kun taho ba?
Ya galla mata harara, ya ce, sau nawa zan ce miki in kina son zamanmu ya dore sai kin bar shan giya?
Ta zumburo baki, sannan ta mike ta yi kan Sageer ya soma ja da baya ya kuma kira sunanta da karfi,
Sultana!
Ba ta fasa abin da ta ke ba, ta ce, Ai ni ma na gama magana, ranar da ka daina branching da yammatan bisa titi ni ma zan daina shan giya tell your Dad Im sorry.
Ya ce, Sultana na dade da bari, har na kara aure. Don Allah ki daina in ba haka ba rabuwarmu ita ce mafi alkhairi.
Sauran maganar makalewa ta yi a makoshinsa sakamakon cewa, Aisha Sultana ba ta ba shi damar karasawa ba. And then she seduce him. Da ma ya dade cikin kishirwa, sai ya kasa tankwabe tayinta da kaunar da ta ke kokarin nuna masa. Ga dukkan alamu ba ta ji cewa da ya yi ya kara aure ba, idan kuma ta jin, to ba ta fahimta ba.
Yareema Sageer bai tashi dawowa Sageer dinsa ba sai karfe hudu na sulusin dare.
Lokacin da kuma ba zai iya tafiya gida ba. Ya tuno Saadensa, da kadaicin da ya barta ciki ranarta ta farko a gidan mijinta. Amma a addinance bai aikata haramun ba sabida girkin Sultana ne, ya yi mata kwana bakwai dinta da addini ya bata babu kwange.
Ya duba agogo ya kuma dubi Sultana da ke ta sharar barci. Ta inganta masa daren jiya kamar ba gobe, iyaka iyawarta. Don dai ta mantar da shi laifinta amma duk da haka ya kasa mantawa, abu in ya hada da Maimartaba ba ya daukansa da sauki. Ya yi wanka ya tsarkake kansa ya dauro alwalla. Bai jima yana nafilfili ba ladani ya kira sallar asubah a masallacin da ke kusa da su sai ya ga bara kawai ya shiga masallacin tunda ba su da nisa daga can ya wuce gidan Saadatu, sai ya hukunta Sultana.
Ya hau dukan bayan Sultana ya ce ta tashi ta yi sallah shi zai wuce masallaci daga can ya wuce gida. Ta ce,
Wane gidan kuma? Na dauka mun yi parking zuwa nan ne?
Ya ce, Kin yi parking dai, amma mu muna can, ke da gani na sai ranar da ki ka bar GIYA Sultana.
Da haka ya fice tana ba shi hakuri, amma ko juyowa bai yi ba.
Ita ma ta yi shirin ofis ranta a bace. Ba abin da ta ke so a duniya irin Yareema Sageer. Shi kadai ne daidai da rayuwarta haka babu mai wahalar da ita a duniya irinsa. Amma me ya sa ya kasa gane cewa alcoholism is an addiction?
Tana tuki cikin hawaye har ta isa wajen aikinta da ke kan titin Aguiyi Ironsi.

Ya karya kan motar ya shiga gidan sa. Yayi horn maigadi ya taso da azama ya bude masa kofa, misalin karfe shidda na safe, yana shigar da hancin motar maadanin ta yana harhada kalaman da zai yi amfani da su wajen lallashin Saade bisa wannan babban laifi da yayi mata da bai san yadda zai yi ya wanke kansa ba.
******

MU KARASA A LITTAFI NA 4. KADA KU DAMU TARE SUKE. TAKU HAR ABADA; SUMAYYAH ABDULQADIR (TAKORI).
26|11|2021

NA HUCE..
LITTAFIN
SUMAYYAH ABDULKADIR
Hawayen da yake ta rikewa ne suka kwace masa, ya juya kadan ya dubi Rahinah wadda ke kallon bayansa a lokacin, suka kuma hada ido, ji ta yi zuciyar ta na son karyewa (rauni irin na diya mace na son mamayar ta) amma ta amince wannan shine decision mai kyau ga rayuwar ta.
Sai ta maida idanunta ta lumshe su a hankali. Tana sauke ajiyar zuciya.
Shi kuma ya sa kai ya fita daga dakin, babu ko waiwaye. Kamar yadda yake ji a ransa ba zai kara waiwayar RAHINAH OMAR a rayuwarsa ba. Ko da bayan cikar burin ta, na zama cikakkar otorhinolaryngologist.
****
Ta dauki hoton karamin kyakkyawan yaron mai kama da ubansa a komai tana kallo with so much adoration, hawaye na sauka a kan fararen kundukukin ta. Ta san yanzu ya girma, watakila aji hudu na firamare? Cikin kowanne hali dai ta san zai kula da shi. Damuwar ta ba a kan kulawar da yaron zai samu ba ne domin hakika tana da tabbacin HABIBUNAHUCHEzai kula da dansa har fiye da yadda yake kula da Hotels din sa. Damuwar ta akan yadda har gobe ta kasa kallon kowanne namiji da idanun sigaraure, kowa ya zo sai ta ga bai kai shi ba, ko farcen kafarsa bai kama ba, ko da kuwaya fi shi komai na rayuwa.
Duk da cewa ta san shi ne kawai a matsayin dalibin jami'ar Cologne ba'a matsayinsa na yanzun ba (mamallakin NAHUCHE HOTELS) amma tana bibiye da duk wani fadi-tashinsa na rayuwa tun daga ranar da ya raba ta da Dan su.
Dalilin bibiyar ne ba ta sani ba har yau, tunda ita ta ce bata son sa. Farin jini kam har bata san irin nata ba, manema ba irin wadanda Allah bai ba ta ba, kuma burin Dada shine ta yi aure tun kafin Allah ya dau ranta, amma har gobe ta kasa kallon kan sauran maza daga shi sai dan mutanen NAHUCHE. The one that took away her pride na diya mace. Wanda ta tabbatar zuwa yanzu ya manta da ita, a irin shuhurar da Allah ya yi masa cikin shekaru goma kacal da rabuwarsu.
Bata san hawaye take ba. Sai da ta ji dandanon gishiri a bakin ta. Hawayen da ta tabbatar ba za ta daina zubar da su ba har zuwa karshen rayuwarta. Idan har rayuwa ba ta koma yadda take a baya ba; with him aside.
"Auren Wucin Gadi".
"Auren kwanaki bakwai kacal". Wadanda abubuwan da suka wakana cikinsu sun fi tsayin na shekaru bakwai. Wanda ya samar da kaddarar Dan da ke a tsakani, Dan da silar zuwansa duniya ne ya yi connecting komai, ya hada zukata ya kuma raba su cikin kwanaki bakwai. Jami'ar Cologne din Jamus ita ce tushe, mafari, ginshiki na dukkan walagigin rayuwar da ta samu kanta.
-Takori
Chapter 19 · 0% Book details