← Book details Maaikaciyar Gomnati Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 53 OF 57

Sashe 53

Maaikaciyar Gomnati Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Baffa sunje asibiti kowa da kowa na family Suna Gaban Haj Rahina wacce take rai a hannun Allah.kuka sukeyi ita da Binta, Binta tana ki yafemin kawata naci amanarki,Ita kuma Haj Rahina tana ke ki rabu dani Binta tsinaniya,so take ta ce Allah na tuba ka yafemin maimakon haka sai zafin ciwon yasa ta koma fadin Alhaji Mohd Inshaa'Allahu......insha'Allahu,sai ta koma cewa nashiga uku mun godewa Allah mun yabi Annabi. Sai rerawa takeyi da wanka.

Bangaren Sahar kuwa ta dan samu sauki amma ta haukace domin duk namijin da ta gani ko yaro ko Babba,ko karami ko babantane da taga da Namiji sai ta bude masa zaninta gabanta ya fito fatsar tace Malam Zaka siya?

Babanta yasa an kulleta a daki na musamman, ammma ko Daddy ta gani sai ta bude masa tace Daddy Na siyarwa ne fa,kan haka wata rana Daddy yayi mata dukan tsiya ya farfasa mata jiki.yana ta kuka shi da Mummy tare da Nadama.
Omar ba abinda ke damunsa irin sha'awar Iklas, wankan da takeyi shike kara rura masa wutar sonta da sha'awarta, ya gama gama sawa Iklas ido, tare da Dana mata tarkonsa ba tare da ta ganeba.burinsa ya samu Iklas ta fara Sallah,bazai iya zama cikin wahalaba ace har sai tayi arba'in. Ga shigar da takeyi me Jan Hankali. Iklas kuma yanda taji wahalar haihuwa tace baza ta kara yarda da Omar ba sai tayi 3mnths ta murmure, kuma hakan ma sai an mata family planning.

AsmaBaffanku ce readers. Tnx all for d comments.ayi min Afwa da typing error ba time ne.ⓂⓂⓂ
MA'AIKACIYAR
GOMNATI
ⓂⓂⓂ

195-200

By
AsmaBaffa

Haj Rahina tana sambatun wahala tace Alhaji Mohd ka yafemin,ina Omar a nemo min shi na masa laifi na jefa masa cuta,Mama ki yafe min,tana nishi taci gaba ni...ni....nice....na..je....wajen...boka...ya sawa Omar cutar da ya bar gida kwata kwata,kuma....kuma...na jefa masa lalaura da dama Wanda bai sameshi ba,Nan dai ta tonawa kanta asiri kaf,
Ita kuma Haj Binta tace ni...kuma...kece zaki yafemin Rahina....naci...amarnarki...kin bani kudi...naje wajen....boka...amma na naki zuwa....na dinga shuka miki karya....na cinye miki kudi...na gina kaina.....sabo....sabo da Bana so kici gaba.
Haj.Rahina ce ta fashe da kuka tace wa Binta ke annamimiya ba take nakeyi ba....ki kyaleni inji da kaina...kowa yana gabansu both family Binta da Rahina sai kuka sukeyi.Omar da Iklas sun shigo suma,nan take Omar yace kanku kuka yiwa na yafe.....da sauri Iklas ta rufe masa baki,cike da shagwaba ta rada masa a kunne Allah ni baza ka yafe musu ba,da ace da hali ma gwara a karasa datse musu kafafunsu

No wifey cewar Omar,to shike nan a datse musu hannu ko daya ne,kuma baza a yafe musu ba masu shirka,suka cucemu mijina yayi ta shan Wahalar kuka nima aka sani kuka
Na dinga tausauyin Omar Ina kuka to kukan da suka sani bazan yafe ba.
Omar ne dauke da prince a kafada ya karasa jikin Bed din yace sannu Allah Baku lfy,da sauri Haj Rahina tace ka yafemin da yarana mun zalinceka,na yafe muku komai wlh,Mama ma ta yafe,Baffa kuwa tunda yaji lafazin Rahina ya fuce cike da takaici
Su Sadiya sun cika wajen da kuka ba ji ba gani suma suna rokon a yafe musu.

Iklas tace honey na gaji kasan fa yau 2 days da yin suna ni na gaji kazo mu tafi gida,Ummi ce ta harari Iklas,Mama tace kuje Omar tunda ka yafe ba matsala ,ni zan zauna dasu tare da Ummi.

Baffa anyi anyi yaki ya yafe musu da kyar Mama ta lallabashi sannan yace ya yafe musu,Omar mota ya budewa Iklas ta shiga shima ya shiga yau shine driver prince yana Bayan mota a kwance,Iklas ce ta kalli Omar da harara tare da dauke kai,hannunta ya riko yana mirzawa lfy ke kuma?me nayi ake hararata.Kaine ai Honey ragon maza kawai,daga anyi Abu sai zuciyarka tayi Rauni ka yafe musu,yanzu mene abin yafe musu anan,ko kukan da sukani na tausayin cutar da ke damunka sanda kana gidanmu baka duba ba ka wani je gabansu Na yafe muku Allah yafe mana gaba daya,ta kwaikwayi maganar omar,shi kuwa murmushi kawai yakeyi,ta kara cewa wannan idan suka warke na hango rabaka dani Za suyi kaje kai ta yafe musu ,mashirka dasu Indai mutum a rayuwarsa yace malamai zai rike,komai mutum bazai tsarkake zuciyarsa ba ya yarda da Allah yana addua to wlh yana tare da wahala duniya da lahira,shirka honey bafa karamin Abu bane,kuma malaman suyi ta cinye musu kudi suna musu wayo,Allah shi keyin komai,babu Wanda ya isa yayi ma abinda Allah bai bai yi ma ba.

Amma a yanzu da yawa mutum bazai Dage da addua wajen Allah ba,ya mike ya roka da kansa,sai dai ya dinga kai kukansa wajen malaman bokaye,maybe ma mutum yafi malamin da yaje gunsa daraja wajen Allah.amma yaki rokarsa. Ana fa kuskure,yan kasuwa,matan aure,yan mata,zawarawa,ma'aikata,etc kowa yanzu da yawa za kaga malamai sukeyi kala kala,malamina.to wlh mutuwa bata sallama,ba sai lallai da ciwo ba za a wuce,idan ma baka mutu ba ka tuba baka da tabbacin an karbi tuban naka ko ba'a karba ba?yanzu honey ni kaina sanda nake nakudar nan ai na zata wucewa zanyi.

Dariya Omar yayi my heart ta Girma jibi wa'azin da kikeyi haka inda kike birgeni watarana zancen manya kikeyi idan Abu yazo serious kike daukansa,amma idan rigima da darunki suka tashi ba sauki da kyar ake shawo kanki.
Murmushi tayi cike da shagwaba ta fada jikin Omar dake tuki, ni....ka daina cemin rigimammiya wannan ai sai prince.wani shock ke fisgar Omar na tsananin sha'awar Iklas.murya a dishe yace Wifey yaushe mace take fara Sallah in ta Haihu?cike da dabara Iklas tace idan Wanda sukayi haihuwa uku zuwa hudu ne to 40days sukeyi suke fara Sallah, wasu 1wk ma,wasu 2-3wks kai wasu ma sai su wuce 40days din etc ya danganta da yanda mace take.

Da Sauri Omar yace to irinku fa masu haihuwa daya,tamke fuska tayi ba wasa, tace masu haihuwar fari musamman irinmu da muke yan yara to sai munyi minimum 3to 4mnths,kai irinmu da muke 16yrs to 17yrs har 5mnths munayi kafin jini ya dauke mu fara Sallah.
Bare ni da nake ta dabance kasan dai ko period tsuuuuuuuuuuuuu yake zubo min kamar an bude tap,dariya Omar yayi sosai yanda da girmansa da Ilminsa Iklas sai raina masa hankali takeyi zata wai yi masa wayo.

A fili kuwa nunawa yayi ya yarda da zancenta Omar ya kara mata haske da tab ai dama na sanki wajen period bare wannan ai nasan flowing zaiyi like a river. Da sauri tace kamar ka sani kuwa,a river dinma bafa karama ba babban kogi,ko Dam.
Harda kara kankame Omar saboda murna wai tayi masa wayo.

Omar kuwa rungumeshin da tayi shi ya jawo Omar yaci birki kiiiiiit tare da gangarewa kasa.cikin zafin zafin nama ya hade bakinsu wuri daya, a haukace yake rikitata da salonsa,Iklas ta fara hargitsewa Itama musamman daya fara wasa da dukiyar fulaninta,itama biye masa tayi suka haukacewa juna da gani sunyi missing din juna,kawai I miss u suke furtawa juna.

Iklas gani tayi abin na Omar yayi yawa, idan ta bari itace zata kwana ciki,dan sai ta kuma samun ciki ta Shiga uku. Da kyar ta kwaci kanta,da taga yaki kyaleta kuka ta saka masa, sannan ya kyaleta cike damuwa.yaci gaba da driving.

Iklas taji wahalar Haihuwa Mama ta samu a room dinta ta je ta gaisheta kamar zata mata sujjada tsabar biyayya wai ita a dole tasan zafin haihuwa yanzu,lfy Iklas naga kamar kina da magana cewar Mama, Iklas zama ta gyara cike da ladabi tace Mama dan Allah kar ki bari Yaya Omar ya mai dani gidansa idan nayi Arba'in,Mama ta gano Iklas,amma sai tace sabo dame wani abin yake miki?yi gaggawar sanarmin nayi maganinsa,a'a Mama baya min komai wlh,kawai firgitani akeyi a gidansa sai na dinga ganin dodo a jikin bangon room dinmu,dariya Mama tayi karki damu za a kai malamai suyi karatun Qurani,ai Mama musulmai ne dodon basa ji,sun iya karatun suma,idanfa ina karantawa sai dai kiji sunayi suma,kuma Omar bai fada min cewar mama,ai mama ni kadaice na san dasu,a'a wannan za ayi maganinsu cewar Mama, Iklas tace asarar kudi zakuyi gwara Ku barni a nan gidan, Mama tace jeki za ayi bincike,amma bamu da iko sai abinda mijinki yace
Da Sauri ta juyo tace Mama dan girman Allah Ku taimakamin,wlh idan kuka fada masa bazai yarda ba,ni dai kar kuyi masa zancen to.
Murmushi Mama tayi jeki kinji za asan abinyi,kuma baza a fada masa ba,to Mama na gode ta kara jaddawa Mama dan darajar Allah kuyi min Rai,Ku duba lamarin nan,Mama tace Insha'allah.
ta fita tana murna,

Palo ta koma ta Iske Khairat ta cakare kusa da Omar.a fusace Iklas ta dauki katuwar kwalabar wani lemo me tsada ta daki jikin bango nan take kwalabar ta tarwatse Rabin kwalabar da tsini a hannun Iklas, gashi har wata ta yanketa a tafin hannu,amma a haka tayi kan Khairat gadan gadan zata buga mata kwalaba, Omar ya riketa kam sai zullo takeyi sai ya saketa,sosai Iklas take son kwacewa tare da nishi ka kyaleni pls honey, Omar kuma ya rungumeta ya hanata Motsi,sai huci takeyi tana wlh idan na kamata sai ta gane kurenta,
Yer uwarki ce fa cewar Omar?ina ruwana da ita,na tsaneta bana sonta,da gudu Khairat ta tafi part dinsu tana rokon sauran suzo su bar Nigeria, da kyar a ka lallasheta cewar gobe za a tafi, sai kuka takeyi wiwi
Omar kuwa da kyar ya kwace Kwalabar daga haannun Iklas sai lallashinta yakeyi tare da kwantar mata da hankali,yana shafa gadon bayanta tare da dan bubbugawa,yana rada mata a kunne relax wifey bana son saurin fushin nan naki, ki dinga hakuri, yanzu laifina ka gani?cewar Ikla taci gaba tunda taxo takeyin Abuwa bad a kanka ina kallon nake sharewa, kai kuma sai biye mata kakeyi, wlh hakurina ya kare da ace ta tsaya sai na mata bille a kirjinta da fuska,Kasan kuma zan iya danma na canja halina da ace ni din ta dace da tuni kaima Kasan nayi maganinta,gwara in tazo ka dinga matsawa dan next time ka kara barinta har da kai zan hada.
Chapter 53 · 0% Book details