Sashe 52
Maaikaciyar Gomnati Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Aikuwa Iklas ta busar da gashinta da hand drier ta tajeshi tsab ta shafeshi da man gashi me kamshi,da turaren gashi ma aka shafa,tea ta sha me kaurin gaske,sannan taci kaji da sakwara miyar egusi,Omar kuwa tuni Subby ta fada masa ta Haihu lfy amma ance ya jira za a kirashi,ai kudi ya zaro wanda bai san yawansu ba ya bawa Subby yar Albishir,sauran nurses ma kawai kudi yake ta fella musu,
har yau shuru,har yayi Sallar isha yana jira,Iklas zama tayi ta shafa body lotion dinta me arnen kamshi,
Ta sa Wani Sabon dinkin doguwar rigar material black and milk yayi mugun mata kyau,sama ya dame kasa ya bude,Gomnati fa ta gaji amma haka ta dage tana kwance ta shafa powder ta,ta sa red jambaki,kamar ba ita ta haihu ba,
Dagwas da ita tana kwance Ummi ta mika mata turaruka ta shafa wasu ta fesa wasu,kamshi takeyi na fitar hankali,jariri kuwa tuni Mama ta goge masa jiki da zaitun bayan ya dan dade akayi masa wanka tas dashi aka shafa masa lotion irin na jarirai masu matukar tsada da kamshi Omar ne ya siyosu tun cikin Iklas na 7mnths,kaya masu kauri da pampers aka sa masa suma kayan sai da Mama ta shafa musu turare kafin a sa masa
Yaro gwanin sha'awa,sai da komai ya zama normal sannan a hankali Iklas tace Ummi a kira min ya Omar, Mama sabo da Murna duk ta kira mutane ta sanar musu,Iklas ma haka,Omar kuwa bai kira kowa ba yafi so yaga Halin da matarsa ke ciki.
Yana zaune Ummi baki har kunne tace shigo Umaru,ai Omar ya Riga Ummi shiga dakin,mamakine ya cikashi,bai zaci haka zaiga Iklas ba.shi gani yayi ma ta kara kyau,sai yar ramar wahala da tayi kadan,ga kamshi da take zubawa,tuni Mama da Ummi sunyi waje sun basu waje,Omar ya rungume Iklas murna ta hanashi sukuni,sannu my sweet heart,kinsha wahala,har mamakin Murnar Omar tayi.
Kisses ya dinga manna mata tako ina,kamar zai cinyeta sai sinsinar kamshinta yake tayi kamar zai zauce,yaron dake gefe ya dauka yayi masa Addua sosai sai kallon sa yakeyi ba kifta ido,zama yayi gefen Iklas yaron na jikinsa Kara kallon yaron yayi ya kalli Iklas tare da cewa amma wannan yaron na Kwandala ne ko?dariya sukayi gaba dayansu,tana dukan Omar a baya cike da shagwaba,
Sai kunyar abubuwan dayi takeji a gaban mutane,yaro ya dara alamar Neman Nono,wifey nono za a bawa intestine tunda kince a bashi hanji,murmushi tayi tana shagwaba tace ni... Sai..na huta bacci nakeji,ki bashi mana yasha sai kiyi baccin, a'a ruwan nono bai zo ba fa,a bashi zam zam yasha kawai,dole Omar ya bashi Zam zam.ita kuma tana ta baccinta.
Sai da ta kwashe 8hrs tana bacci,Omar har yaje gida yayi sabon wanka ya dawo,Mama tace Tunda kinci abinci yanzu ki bashi yasha mana kinga har ya fara kuka,a bari na kara yin wanka Mama, wanka tayi ta canja wata shigar ta lace Riga da skert cib ita,kamar dazu haka ta kara hadewa,
Yaro sai kukan yunwa yakeyi,Omar ya shigo room din me ya sameshi haka?Ummi ta bata fuska gata nan taki bashi nono, daga tace wancen sai tace wannan,Mama ce tayi waje tana amsa wayar Baffa,cike da Fushi Iklas ta kalli Ummi ni... Nifa.. Nonona zubewa zaiyi ya lalace,kuma mijina fa?salati Ummi tayi,Omar kuwa dadi yaji ana ji dashi,ya zauna gefenta da sigar lallashi yana Haba wifey ai duk daya ne ni da shi,kinga shima yasha Nima a boye min nawa,bazai yi komai ba in dai ana kula dashi,
Tana kunkuni ta dauki Baby ta saka Hijab ta boye sannan ta fara bashi,yana zuka tace wayyo Allah,Omar yace mene rada masa tayi a kunne tana cije lips wannan da zafi wahala yake bani ba irin naka yakeyi ba,dole ayi masa fada,murmushi Omar yayi yace yes ai ni na musamman ne kalar nawa daban,,Iklas tace cikin rada shi yasa nace kar a bashi gudan jini ko heart a kaishi wajen madaciya,ko hanji.
Haka ne my love,Ummi ce tace munafukan banza aikinku kenan,ke harda boye nono kar a gani ko,Iklas tace ae Ummi abina me daraja ne,nufinki in dinga kwayeshi gaban kowa nasan muhimmancinsa.
Ke ni kar ki isheni da Surutun tsiya dazu kika gama kururwa da kuka,sambatu ba Wanda baki ba kin samu kanki yanzu kin ishe mu,Omar waya yake ta kira cike da zumudi an haifar masa a bouncing Baby Boy,
Mama tace kar a sallamesu sai gobe Iklas tayi bacci ta huta.
Ibzzy Boy yan sanda sun masa jina jina yayi nadamar halinsa,yayin da ya shiga taitayinsa,da kyar aka karbeshi.ya tafi cike da nadamar rayuwarsa ta baya,sai Istigifari yakeyi.
Sadiya ta samu kiran gaggawa daga Office dinsu tana zuwa aka mika mata takardar sallama daga wajen aikinsu,saboda taci bashinsu masu matukar yawa na company taki biya,Sadiya tayi nadamar irin karyar da suka shirya a bikinsu domin da kudin ta ranta ta kara,
Tayi kuka ta gode Allah,tana Oh nasan wannan hukuncina nake karba sanadiyyar abubuwan da nayiwa su Ya Omar,ya zama dole na fada musu abinda muka shuka.
Aisha kuwa yarta da ta Haifa yanzu an gano tana da sickle cell,wato cutar sikila,kullum a hospital suke suna kashe kudi,basu da kwanciyar hankali.
Dama shi laifi in kayi watarana ma sai ka shiryu ka daina sannan a fara jefo ma kaddarori,to su Sadiya karba tasu sukeyi tako Ina,addua kawai sukeyi,sun tabbas hakkin Mama,dasu Omar ne yake binsu,
Dan yanzu haka Sadiya hawan jini ya shigeta,an dorata akan magani.Hajia Rahina da kawarta Hajia Binta sun shirya zasu je ayi musu wata addua wurin malam ,saboda abinda ke fadowa Kansu na masifa.
Suna hanyar Nijar wasu yan fashi suka taresu a mota suka karbe kudaden tare da yi misu fyade sannan suka harbesu a kafafu da Hannu,driver kuwa basu kulashi ba ganin shi talaka ne,shine ya buga waya ya fadawa Baffa yayin da saura 4days sunan Baby na Omar.haka aka kwasosu ranga ranga rai a hannun Allah.
Asibiti aka wuce dasu ,a wulakance,rai a hannun Allah,dama ita duniya dai dai take da kowa,mutum yayi ta shuka tsiyarsa,rana daya Allah ya maidashi ba kowa bane,kyashi,hassada,bakin ciki,gulma,cin amana ta ko ina sunyi yawa a alummarmu ga jarabar son abin duniya,kowa burinshi yaga yafi kowa.Allah kyauta.
Sahar kuwa an gaji an dawo da ita gida,ta fige,ta yage,tayi baki,kai ba Wanda ke gane Sahar yanzu ta dawo kamar kwarangwal,tsoron zuwa dubiyaa akeyi ma,malamai sai aiki sukeyi a kanta ba dare ba rana.dama duk wani iskanci da mutum keyi lafiya ce tayi masa waya,yau gashi halin da suka fada.
Muji tsoron Allah don yanzu tun a duniya ake karbar saka mako.
Bayan an sallami su Iklas,suna gida an cika ana zuwa barka kungiya kungiya,Omar yana dakin da aka bawa Iklas kullum yana tsakiyar Bed shi yake mika jariri,Mama ce take korarsa amma ya nace a room din.
Masu ganin jariri sunyi saukin zuwa,Baffa yazo Room din Iklas ya daukeshi cike da farin ciki,sai addua yake zuba ma jaririn.Iklas yanda take daukan wanka kamar zata party kullum,kai kace bata haihu ba,kullum sabon kayan da Omar ya dinka mata wajen set 20 dasu take cakarewa.kamshi na gaske ke fita a ko ina na jikinta,haka Baby ma kana gani kaga yan gayu ne iyayensa.
Kullum Ummi ke yiwa Iklas wanka ta gasata sosai,ita kuma Iklas anayin wankan tana kuka,tun kafin ma aje wankan take fara kuka.
Me gyaran jiki ta biya kudi ake mata kullum,sai kace zatayi bikin aure,
Khairat suna nan suma sunga jariri,ganin Iklas na busy ta kara likewa Omar,Iklas kuwa hankalinta na kan mijinta tana kallon abinda Khairat keyi.
Angel kawar Iklas ce tazo ganin jariri tace Gomnati ya haihuwar?kallonta Iklas tayi tace keeeeeee Marododo kenan,kinji azaba wlh kubi uwarku na fada miki ki dage da yiwa mamanki biyayya,sai yanzu naga muhimmanci uwa,ke ni yanzu da Mahaifiyata tana da rai ai da taga biyayyar da bata taba gani ba.
Duk inda ake tunanin ciwon ya wuce tunanin me tunani,duk inda zan miki bayani baza ki ganeba Angel,ki bari sai kinyi kya ji.
Wani duhu duhu na dinga gani,ke nifa ban San sanda na koma ganin Hoton kwandala a idona ba,Angel tace kwandala?abinda ba wani amfani ake dasu ba yanzu amma kika ga pic din kwandala,Iklas ta gyara zama tace to wlh kwandala na dinga gani a cikin idona kawai,sai kuma naga danwake da danmalele,ke harda dankwali Ashe na Ummi ne.
Kinga da dan nan ya fito wani duhu na gani duf sai naga wani kwan fitila yayi flashing wall wal,kinsan irin fitilar da can da tsofaffi suke durawa kerosine?Angel tace yeah tace to irinta fa na gani Dana fara farfadowa,Ashe kwan nepa ne.Angel sai dariya take mata.
Omar ne ya shigo da jariri ya mikawa Iklas lokacin Angel tana sallah,zama yayi zai fito da nono ya bawa jariri Da sauri Iklas ta dafe Rigarta miko min Hijab,ke wifey kawarki ce kawai a room dinfa kuma sallah takeyi,ae ni dai ka dauko min,dakko mata yayi tasa ta fara bawa jaririn nono, Omar dage hijab din yayi ya shige shima ya kwanta a cinyarta,Jariri na shan nono Omar na kan cinyar Iklas tana shafa masa gashinsa.
Da dare Iklas ta fesa wanka ita da jariri ta sashi gaba cikin haske ta kura masa ido kurrrrrrrrr ko kiftawa batayi,har Ummi ta shigo bata San ta shigo ba,tana ta kallon Baby tana murmushi ita kadai,afili ta fara maganganunta Kai yanzu Allah ni na haifeka?kato dakai amma ka fito ta wannan yar kafar kofa?kalleka me kyau,gaskia Ina sonka,ina sonka,nafi kowa kaunarka a duniya,Allah raya min kai,ka zama dan albarka,dagashi tayi sama tana ta kissing dinsa ta ko ina ba ji ba gani,Ummi ce ta katseta ina jin dai Aljanu sun shigeki ko?Murmushi Iklas tayi tare da kwantar da yaron,Ummi Allah dan Boy din nan yayi kyau da yawa,kalli hancinsa irin na honey. Ummi wai kamar ni amma ina da haka,gaskia na samu abokina,rufemin baki sakarar banza cewar Ummi.
Shi Omar yanda Iklas ke chake gayu ne yake birgeshi,ta haihu kullum busy amma tana kula da kanta,shi gani yakeyi har tafi da kafin ta haihu daukan wanka da komai da komai.
Kasancewar Hajiya Rahina na asibiti Iklas batayi taron suna ba,yaro yaci Sunan Baban Iklas wato Abubakar suna kiransa Prince,raguna 2 da katon Sa Omar ya yankawa Iklas.
Gomnati so takeyi kawai ayi Suna tayi maganin Khairat.
har yau shuru,har yayi Sallar isha yana jira,Iklas zama tayi ta shafa body lotion dinta me arnen kamshi,
Ta sa Wani Sabon dinkin doguwar rigar material black and milk yayi mugun mata kyau,sama ya dame kasa ya bude,Gomnati fa ta gaji amma haka ta dage tana kwance ta shafa powder ta,ta sa red jambaki,kamar ba ita ta haihu ba,
Dagwas da ita tana kwance Ummi ta mika mata turaruka ta shafa wasu ta fesa wasu,kamshi takeyi na fitar hankali,jariri kuwa tuni Mama ta goge masa jiki da zaitun bayan ya dan dade akayi masa wanka tas dashi aka shafa masa lotion irin na jarirai masu matukar tsada da kamshi Omar ne ya siyosu tun cikin Iklas na 7mnths,kaya masu kauri da pampers aka sa masa suma kayan sai da Mama ta shafa musu turare kafin a sa masa
Yaro gwanin sha'awa,sai da komai ya zama normal sannan a hankali Iklas tace Ummi a kira min ya Omar, Mama sabo da Murna duk ta kira mutane ta sanar musu,Iklas ma haka,Omar kuwa bai kira kowa ba yafi so yaga Halin da matarsa ke ciki.
Yana zaune Ummi baki har kunne tace shigo Umaru,ai Omar ya Riga Ummi shiga dakin,mamakine ya cikashi,bai zaci haka zaiga Iklas ba.shi gani yayi ma ta kara kyau,sai yar ramar wahala da tayi kadan,ga kamshi da take zubawa,tuni Mama da Ummi sunyi waje sun basu waje,Omar ya rungume Iklas murna ta hanashi sukuni,sannu my sweet heart,kinsha wahala,har mamakin Murnar Omar tayi.
Kisses ya dinga manna mata tako ina,kamar zai cinyeta sai sinsinar kamshinta yake tayi kamar zai zauce,yaron dake gefe ya dauka yayi masa Addua sosai sai kallon sa yakeyi ba kifta ido,zama yayi gefen Iklas yaron na jikinsa Kara kallon yaron yayi ya kalli Iklas tare da cewa amma wannan yaron na Kwandala ne ko?dariya sukayi gaba dayansu,tana dukan Omar a baya cike da shagwaba,
Sai kunyar abubuwan dayi takeji a gaban mutane,yaro ya dara alamar Neman Nono,wifey nono za a bawa intestine tunda kince a bashi hanji,murmushi tayi tana shagwaba tace ni... Sai..na huta bacci nakeji,ki bashi mana yasha sai kiyi baccin, a'a ruwan nono bai zo ba fa,a bashi zam zam yasha kawai,dole Omar ya bashi Zam zam.ita kuma tana ta baccinta.
Sai da ta kwashe 8hrs tana bacci,Omar har yaje gida yayi sabon wanka ya dawo,Mama tace Tunda kinci abinci yanzu ki bashi yasha mana kinga har ya fara kuka,a bari na kara yin wanka Mama, wanka tayi ta canja wata shigar ta lace Riga da skert cib ita,kamar dazu haka ta kara hadewa,
Yaro sai kukan yunwa yakeyi,Omar ya shigo room din me ya sameshi haka?Ummi ta bata fuska gata nan taki bashi nono, daga tace wancen sai tace wannan,Mama ce tayi waje tana amsa wayar Baffa,cike da Fushi Iklas ta kalli Ummi ni... Nifa.. Nonona zubewa zaiyi ya lalace,kuma mijina fa?salati Ummi tayi,Omar kuwa dadi yaji ana ji dashi,ya zauna gefenta da sigar lallashi yana Haba wifey ai duk daya ne ni da shi,kinga shima yasha Nima a boye min nawa,bazai yi komai ba in dai ana kula dashi,
Tana kunkuni ta dauki Baby ta saka Hijab ta boye sannan ta fara bashi,yana zuka tace wayyo Allah,Omar yace mene rada masa tayi a kunne tana cije lips wannan da zafi wahala yake bani ba irin naka yakeyi ba,dole ayi masa fada,murmushi Omar yayi yace yes ai ni na musamman ne kalar nawa daban,,Iklas tace cikin rada shi yasa nace kar a bashi gudan jini ko heart a kaishi wajen madaciya,ko hanji.
Haka ne my love,Ummi ce tace munafukan banza aikinku kenan,ke harda boye nono kar a gani ko,Iklas tace ae Ummi abina me daraja ne,nufinki in dinga kwayeshi gaban kowa nasan muhimmancinsa.
Ke ni kar ki isheni da Surutun tsiya dazu kika gama kururwa da kuka,sambatu ba Wanda baki ba kin samu kanki yanzu kin ishe mu,Omar waya yake ta kira cike da zumudi an haifar masa a bouncing Baby Boy,
Mama tace kar a sallamesu sai gobe Iklas tayi bacci ta huta.
Ibzzy Boy yan sanda sun masa jina jina yayi nadamar halinsa,yayin da ya shiga taitayinsa,da kyar aka karbeshi.ya tafi cike da nadamar rayuwarsa ta baya,sai Istigifari yakeyi.
Sadiya ta samu kiran gaggawa daga Office dinsu tana zuwa aka mika mata takardar sallama daga wajen aikinsu,saboda taci bashinsu masu matukar yawa na company taki biya,Sadiya tayi nadamar irin karyar da suka shirya a bikinsu domin da kudin ta ranta ta kara,
Tayi kuka ta gode Allah,tana Oh nasan wannan hukuncina nake karba sanadiyyar abubuwan da nayiwa su Ya Omar,ya zama dole na fada musu abinda muka shuka.
Aisha kuwa yarta da ta Haifa yanzu an gano tana da sickle cell,wato cutar sikila,kullum a hospital suke suna kashe kudi,basu da kwanciyar hankali.
Dama shi laifi in kayi watarana ma sai ka shiryu ka daina sannan a fara jefo ma kaddarori,to su Sadiya karba tasu sukeyi tako Ina,addua kawai sukeyi,sun tabbas hakkin Mama,dasu Omar ne yake binsu,
Dan yanzu haka Sadiya hawan jini ya shigeta,an dorata akan magani.Hajia Rahina da kawarta Hajia Binta sun shirya zasu je ayi musu wata addua wurin malam ,saboda abinda ke fadowa Kansu na masifa.
Suna hanyar Nijar wasu yan fashi suka taresu a mota suka karbe kudaden tare da yi misu fyade sannan suka harbesu a kafafu da Hannu,driver kuwa basu kulashi ba ganin shi talaka ne,shine ya buga waya ya fadawa Baffa yayin da saura 4days sunan Baby na Omar.haka aka kwasosu ranga ranga rai a hannun Allah.
Asibiti aka wuce dasu ,a wulakance,rai a hannun Allah,dama ita duniya dai dai take da kowa,mutum yayi ta shuka tsiyarsa,rana daya Allah ya maidashi ba kowa bane,kyashi,hassada,bakin ciki,gulma,cin amana ta ko ina sunyi yawa a alummarmu ga jarabar son abin duniya,kowa burinshi yaga yafi kowa.Allah kyauta.
Sahar kuwa an gaji an dawo da ita gida,ta fige,ta yage,tayi baki,kai ba Wanda ke gane Sahar yanzu ta dawo kamar kwarangwal,tsoron zuwa dubiyaa akeyi ma,malamai sai aiki sukeyi a kanta ba dare ba rana.dama duk wani iskanci da mutum keyi lafiya ce tayi masa waya,yau gashi halin da suka fada.
Muji tsoron Allah don yanzu tun a duniya ake karbar saka mako.
Bayan an sallami su Iklas,suna gida an cika ana zuwa barka kungiya kungiya,Omar yana dakin da aka bawa Iklas kullum yana tsakiyar Bed shi yake mika jariri,Mama ce take korarsa amma ya nace a room din.
Masu ganin jariri sunyi saukin zuwa,Baffa yazo Room din Iklas ya daukeshi cike da farin ciki,sai addua yake zuba ma jaririn.Iklas yanda take daukan wanka kamar zata party kullum,kai kace bata haihu ba,kullum sabon kayan da Omar ya dinka mata wajen set 20 dasu take cakarewa.kamshi na gaske ke fita a ko ina na jikinta,haka Baby ma kana gani kaga yan gayu ne iyayensa.
Kullum Ummi ke yiwa Iklas wanka ta gasata sosai,ita kuma Iklas anayin wankan tana kuka,tun kafin ma aje wankan take fara kuka.
Me gyaran jiki ta biya kudi ake mata kullum,sai kace zatayi bikin aure,
Khairat suna nan suma sunga jariri,ganin Iklas na busy ta kara likewa Omar,Iklas kuwa hankalinta na kan mijinta tana kallon abinda Khairat keyi.
Angel kawar Iklas ce tazo ganin jariri tace Gomnati ya haihuwar?kallonta Iklas tayi tace keeeeeee Marododo kenan,kinji azaba wlh kubi uwarku na fada miki ki dage da yiwa mamanki biyayya,sai yanzu naga muhimmanci uwa,ke ni yanzu da Mahaifiyata tana da rai ai da taga biyayyar da bata taba gani ba.
Duk inda ake tunanin ciwon ya wuce tunanin me tunani,duk inda zan miki bayani baza ki ganeba Angel,ki bari sai kinyi kya ji.
Wani duhu duhu na dinga gani,ke nifa ban San sanda na koma ganin Hoton kwandala a idona ba,Angel tace kwandala?abinda ba wani amfani ake dasu ba yanzu amma kika ga pic din kwandala,Iklas ta gyara zama tace to wlh kwandala na dinga gani a cikin idona kawai,sai kuma naga danwake da danmalele,ke harda dankwali Ashe na Ummi ne.
Kinga da dan nan ya fito wani duhu na gani duf sai naga wani kwan fitila yayi flashing wall wal,kinsan irin fitilar da can da tsofaffi suke durawa kerosine?Angel tace yeah tace to irinta fa na gani Dana fara farfadowa,Ashe kwan nepa ne.Angel sai dariya take mata.
Omar ne ya shigo da jariri ya mikawa Iklas lokacin Angel tana sallah,zama yayi zai fito da nono ya bawa jariri Da sauri Iklas ta dafe Rigarta miko min Hijab,ke wifey kawarki ce kawai a room dinfa kuma sallah takeyi,ae ni dai ka dauko min,dakko mata yayi tasa ta fara bawa jaririn nono, Omar dage hijab din yayi ya shige shima ya kwanta a cinyarta,Jariri na shan nono Omar na kan cinyar Iklas tana shafa masa gashinsa.
Da dare Iklas ta fesa wanka ita da jariri ta sashi gaba cikin haske ta kura masa ido kurrrrrrrrr ko kiftawa batayi,har Ummi ta shigo bata San ta shigo ba,tana ta kallon Baby tana murmushi ita kadai,afili ta fara maganganunta Kai yanzu Allah ni na haifeka?kato dakai amma ka fito ta wannan yar kafar kofa?kalleka me kyau,gaskia Ina sonka,ina sonka,nafi kowa kaunarka a duniya,Allah raya min kai,ka zama dan albarka,dagashi tayi sama tana ta kissing dinsa ta ko ina ba ji ba gani,Ummi ce ta katseta ina jin dai Aljanu sun shigeki ko?Murmushi Iklas tayi tare da kwantar da yaron,Ummi Allah dan Boy din nan yayi kyau da yawa,kalli hancinsa irin na honey. Ummi wai kamar ni amma ina da haka,gaskia na samu abokina,rufemin baki sakarar banza cewar Ummi.
Shi Omar yanda Iklas ke chake gayu ne yake birgeshi,ta haihu kullum busy amma tana kula da kanta,shi gani yakeyi har tafi da kafin ta haihu daukan wanka da komai da komai.
Kasancewar Hajiya Rahina na asibiti Iklas batayi taron suna ba,yaro yaci Sunan Baban Iklas wato Abubakar suna kiransa Prince,raguna 2 da katon Sa Omar ya yankawa Iklas.
Gomnati so takeyi kawai ayi Suna tayi maganin Khairat.