Sashe 9
Kishiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A chan d'akin inna Asabe kuwa bayan Fatima ta fita , bilya ne ya dubi inna Asabe yace " gwaggo wacece wannan dana gani a gidan nan, saboda ban tab'a ganinta a gidan nan ba ", kyab'e baki tayi sannan tace" Fatima mana y'ar kishiya ta da ta rasu " zabura yayi cike da jin dad'i " yauwa anzo wajen ya fad'a yana sosa kai ," baban shi ne ya dube shi , yace ya akayi ne d'an baba , ya fad'a ya sauraronshi," baba dama gaskiya ina sonta kuma so nakeyi na aureta ", tashin hankali Wanda ba'a sanya masa rana , ai inna Asabe ji tayi kamar zata mutu , kallon d'an uwan nata tayi taji me zai cewa d'an nasa " ah Masha Allahu ai hakan ma yayi lallai yayi kyau , ah abu a cikin gida " ita dai Asabe ta kasa cewa komai, shi kuwa bilya murna jin mahaifinsa ya amince , sosai suka yi hira har bayan la'asar kafin su fara shirin tafiya , ita dai Asabe abin duniya ya dame ta saboda tana tsammanin ta yi abin da ba mahalukin da zai so fatima amma ga wata sabuwa, ta aurar da d'iyarta ga d'an birni tana ganin ba wanda zai k'ara cewa yana sonta amma gashi mai kud'i daga birni ya zo yana sonta, sallama yayi mata tare da sanar da ita cewa lallai ta sanar da Fatima halin da ake ciki kuma ba dad'ewa za'ayi ba za'ayi bikin saboda tsananin son abin duniyarta ta kwantar da kai , ya sallameta da kud'i masu tsoka haka shima bilya ya bata najin dad'in cewar ta amince za'a bashi fatima, haka suka yi sallama suka kama hanyar fita daga k'auyen.
A cikin gida kuwa bayan inna Asabe ta shiga kasa zaune tayi ta kasa tsaye , ta saka wannan ta kwance wanchan , duk dai akan Fatima ne da batasan ta auri bilya saboda tasan suna da kud'i kuma batason ta shiga daula tana son tayi ta ganinta cikin tsanani, amma da ta tuna da waye bilya da irin halayensa ai sai ta godewa Allah dan ko ba komai Fatima zata k'unshi bak"'in ciki saboda auren mashayin giya da Neman mata bazai haifar mata da komai ba sai tashin hankali domin kuwa babu kwanciyar hankali , k'arshe ma dai ciwon zuciya ya kamata ta mutu , wannan tunanin da tayi ne ya bata k'warin guiwar tunkarar Fatima da zancen.
🌸🌸🌸🌹🌹🌹🌸🌹
Da daddare bayan Fatima ta dawo daga tallan ta da ta saba , zuwa tayi ta iske Asabe a kishingid'e tana cin nama balagu da ta bayar da kud'i a siya mata wajen idi mai nama , duk kuwa a cikin kud'in da yayan nata ya bata ne , " inna sannu da gida , Fatima ta fad'a had'e da rusunawa tana mik'a mata kudin cinikin da tayi " karb'a tayi ta k'irga su tsab daga bisani ta tura su k'ark'ashin tabarmar da take kishingid'e, har zata tashi ta zaunar da ita sannan ta fara yi mata zancen bilya da duk abinda ya ke faruwa sannan ta k'ara da cewa " kuma wallahi auren nan kamar anyi shi angama, dan na yanke ranar auren nan da wata d'aya mai zuwa za'ayi shi", gaban Fatima ne ya fad'i sakamakon wannan magana da innar ta ta tayi , da to ta amsa sannan ta juya ta shiga d'akinta cike da tashin hankali.
🌸🌸🌹🌹🌸🌸🌹🌹🌸🌸
A cikin d'aki kuwa safa da marwa ta Shiga yi , tana tunanin yadda zata b'ullowa da lamarin, a gaskiya kota halin ya ya ne bazata tab'a yadda da auren wannan mutumin ba , zatayi duk mai yiwuwa wajen gujewa aurensa to ta ina zata fara , tayi zurfi a cikin tunani ta tuna da aminiyarta ta yarinta hannatu , aikuwa ta yardarwa kanta cewar lallai zata samu mafita bisa ga hukuncin da ta yankewa kanta , tana ta tunani har chan dare sai daga baya bacci b'arawo yayi awon gaba da ita.
🌸🌹🌸🌹🌸🌹🌸🌹
Da asuba ta farka da Sauri ta gama aikin gida tsaf , ta gama abin da zata fita dashi tallah , sallama ta yiwa inna Asabe bayan tayi aikinta tsab sannan ta fita talla, Alhamdulillah ta siyar da wuri dan haka ta wuce gidan hannatu domin samun mafita , da take itama hannatun tayi aure shekaru biyun baya da suka wuce , a tsakar gida ta tarar da ita suka rungume juna cike da murna , sosai sukayi murna na ganin juna, bayan sun gama murnarsu sanan Fatima ta fad'awa aminiyar ta ta abin da ya kawo ta , sosai hannatu ta girgiza da jin wannan maganar , ta dubi Fatima cike da kulawa tace " Fatima nasan kinyi hak'uri , a yanzu bazan baki shawarar ki zauna a aura mini mashayin giya da Neman mata ba , dan haka yanzu meye mafita, nan Fatima ta shaida mata Cesar tanason ta tafi neman dangin mahaifiyarta , hannatu ce ta k'arfafa mata guiwa na cewar hakan yayi indai tasan inda suke ta sanar da ita cewar mahaifinta kafin ya rasu ya sanar da ita garin mahaifiyarta ta , amma ita yanzu matsalarta guda rashin kud'i a hannunta , hannatu ta sanar da ita baza'a samu matsalar kud'i ba insha Allahu , haka su ka k'ark'are matsalar ta su haka ta tafi gida cikin farin ciki .
🌸🌹🌹🌸🌹🌹🌸🌹
Haka dai rayuwa tayi ta tafiya , cikin k'warin guiwa ga Fatima , na yarda ta samu damar zuwa Neman dangin mahaifiyarta , ko ba komai zata ga ko da hoton mahaifiyar ta ta , kuma ta sadu da sauran y'an uwa mahaifiyar ta ta, tana ta shirin barin garin , a yayin da inna Asabe a b'angarenta it a ma tana ta shirin biki ta sanarwa da kowa domin murnar da takeyi na cewar fatima zata shiga kabarinta ne , sosai fa takeyi shiri kamar ba bu abinda Yake ranta , bayan ta gama shawo kan y'an uwa malam iliya , da nuna musu alfanun yadda auren zai kasance , suka kuwa yarda da hakan har suke tunanin ma Asabe ai tayi hankali.
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
A haka har satin biki ya shigo , yayin da fatima ta shirya tsaf da komai nata bayan ta karb'i kud'i wajen hannatu domin shiga mota yayin tafiyar ta wajen kakanninta.
Dangin ango sun kawo kud'in sadaki da kayan lefe , kaya sosai aka kawo duk da bak'in cikin da Asabe ke ji amma idan ta tuna yadda Fatima zata dawo sai taga ba komai bane ba , an fara biki yayin da Fatima take nuna musu ba abinda yake damunta .
A Daren ranar d'aurin aure mutane mata mata masu girki NATA aikinsu , Fatima CE ta lek'o ganin hankalin kowa yana ga aikinsa ya Sanya cikin sand'a ta juya ta d'auko duk wani kaya da zata buk'ata da kud'in da k'awarta ta bata , lallab'a ta fice daga gidan ba tare da kowa ya ganta ba ta nufi k'ofar gida, tana tafiya kuwa ta had'u da mai mashin godiya tayi ga Allah duk da a lokacin bata kawo cewar zata samu abin hawa ba saboda dare yayi sosai , ta tsareshi had'i da fad'a masa tashar motocin garin zai kai ta , ya amince ta hau bayan sunyi cinki ta yarda , basu zame ko ina ba sai tasha , tana zuwa kuwa tayi sa'ar samun direban na k'ok'arin tashi Dama sauran mutum d'aya Duke jira aikuwa tanajin motar zariya ce da Sauri ta fad'a bayan ta sallami mai mashin d'in da ta hau , da take tafiyar ta dare ce babu wuya suka bita daga cikin k'auyen suka cilla babban titi , sai a sannan Fatima ta saki dogon numfashi samun nasara .......
Please
Share
&comments
To be continue........
🌸🌸🌸🌸🌹🌹🌹🌹
🌿🌿🌿Nussad🌿🌿🌿
🌸🌹KISHIYAR UWA🌹🌸
(True life story)
🍁 Daga Alk'alamin Nussad🌸
GODIYA GA ALLAH SUBHANAHU WATA'ALA , DAYA BANI DAMAR CIGABA DA RUBUTUN LITTAFIN NAN , TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA GA SHUGABANMU ANNABI MUHAMMAD, DA ALIHI DA SAHABBANSA MASU GIRMA.
BAYAN HAKA NA SADAUKAR DA LITTAFINA GA D'AUKACIN Y'AN UWANA NA SABON RUWA'S FAMILY, LUV U ALL🥰🥰
AJUJI'S FAMILY KUMA HAR DA KU BAZAN MANTA DAKU BA , JINJINAR BAN GIRMA GAREKU ALLAH YA K'ARA ZUMUNCI , AMIN🥰🥰
MAHAIFIYATA ALLAH YA JA DA RANKI , HAJIYA FATIMA TURAKI ADAM , LUV U MY MOM❣️❣️
KISHIYAR UWA FAN'S NA GAISHEKU SOSAI DA SOSAI.
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌹🌹🌹🌹🌹
🌸🌸🌸🌸
🌹🌹🌹
🌸🌸
🌹
SHAFI NA 15-16
A cikin gida kuwa bayan inna Asabe ta shiga kasa zaune tayi ta kasa tsaye , ta saka wannan ta kwance wanchan , duk dai akan Fatima ne da batasan ta auri bilya saboda tasan suna da kud'i kuma batason ta shiga daula tana son tayi ta ganinta cikin tsanani, amma da ta tuna da waye bilya da irin halayensa ai sai ta godewa Allah dan ko ba komai Fatima zata k'unshi bak"'in ciki saboda auren mashayin giya da Neman mata bazai haifar mata da komai ba sai tashin hankali domin kuwa babu kwanciyar hankali , k'arshe ma dai ciwon zuciya ya kamata ta mutu , wannan tunanin da tayi ne ya bata k'warin guiwar tunkarar Fatima da zancen.
🌸🌸🌸🌹🌹🌹🌸🌹
Da daddare bayan Fatima ta dawo daga tallan ta da ta saba , zuwa tayi ta iske Asabe a kishingid'e tana cin nama balagu da ta bayar da kud'i a siya mata wajen idi mai nama , duk kuwa a cikin kud'in da yayan nata ya bata ne , " inna sannu da gida , Fatima ta fad'a had'e da rusunawa tana mik'a mata kudin cinikin da tayi " karb'a tayi ta k'irga su tsab daga bisani ta tura su k'ark'ashin tabarmar da take kishingid'e, har zata tashi ta zaunar da ita sannan ta fara yi mata zancen bilya da duk abinda ya ke faruwa sannan ta k'ara da cewa " kuma wallahi auren nan kamar anyi shi angama, dan na yanke ranar auren nan da wata d'aya mai zuwa za'ayi shi", gaban Fatima ne ya fad'i sakamakon wannan magana da innar ta ta tayi , da to ta amsa sannan ta juya ta shiga d'akinta cike da tashin hankali.
🌸🌸🌹🌹🌸🌸🌹🌹🌸🌸
A cikin d'aki kuwa safa da marwa ta Shiga yi , tana tunanin yadda zata b'ullowa da lamarin, a gaskiya kota halin ya ya ne bazata tab'a yadda da auren wannan mutumin ba , zatayi duk mai yiwuwa wajen gujewa aurensa to ta ina zata fara , tayi zurfi a cikin tunani ta tuna da aminiyarta ta yarinta hannatu , aikuwa ta yardarwa kanta cewar lallai zata samu mafita bisa ga hukuncin da ta yankewa kanta , tana ta tunani har chan dare sai daga baya bacci b'arawo yayi awon gaba da ita.
🌸🌹🌸🌹🌸🌹🌸🌹
Da asuba ta farka da Sauri ta gama aikin gida tsaf , ta gama abin da zata fita dashi tallah , sallama ta yiwa inna Asabe bayan tayi aikinta tsab sannan ta fita talla, Alhamdulillah ta siyar da wuri dan haka ta wuce gidan hannatu domin samun mafita , da take itama hannatun tayi aure shekaru biyun baya da suka wuce , a tsakar gida ta tarar da ita suka rungume juna cike da murna , sosai sukayi murna na ganin juna, bayan sun gama murnarsu sanan Fatima ta fad'awa aminiyar ta ta abin da ya kawo ta , sosai hannatu ta girgiza da jin wannan maganar , ta dubi Fatima cike da kulawa tace " Fatima nasan kinyi hak'uri , a yanzu bazan baki shawarar ki zauna a aura mini mashayin giya da Neman mata ba , dan haka yanzu meye mafita, nan Fatima ta shaida mata Cesar tanason ta tafi neman dangin mahaifiyarta , hannatu ce ta k'arfafa mata guiwa na cewar hakan yayi indai tasan inda suke ta sanar da ita cewar mahaifinta kafin ya rasu ya sanar da ita garin mahaifiyarta ta , amma ita yanzu matsalarta guda rashin kud'i a hannunta , hannatu ta sanar da ita baza'a samu matsalar kud'i ba insha Allahu , haka su ka k'ark'are matsalar ta su haka ta tafi gida cikin farin ciki .
🌸🌹🌹🌸🌹🌹🌸🌹
Haka dai rayuwa tayi ta tafiya , cikin k'warin guiwa ga Fatima , na yarda ta samu damar zuwa Neman dangin mahaifiyarta , ko ba komai zata ga ko da hoton mahaifiyar ta ta , kuma ta sadu da sauran y'an uwa mahaifiyar ta ta, tana ta shirin barin garin , a yayin da inna Asabe a b'angarenta it a ma tana ta shirin biki ta sanarwa da kowa domin murnar da takeyi na cewar fatima zata shiga kabarinta ne , sosai fa takeyi shiri kamar ba bu abinda Yake ranta , bayan ta gama shawo kan y'an uwa malam iliya , da nuna musu alfanun yadda auren zai kasance , suka kuwa yarda da hakan har suke tunanin ma Asabe ai tayi hankali.
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
A haka har satin biki ya shigo , yayin da fatima ta shirya tsaf da komai nata bayan ta karb'i kud'i wajen hannatu domin shiga mota yayin tafiyar ta wajen kakanninta.
Dangin ango sun kawo kud'in sadaki da kayan lefe , kaya sosai aka kawo duk da bak'in cikin da Asabe ke ji amma idan ta tuna yadda Fatima zata dawo sai taga ba komai bane ba , an fara biki yayin da Fatima take nuna musu ba abinda yake damunta .
A Daren ranar d'aurin aure mutane mata mata masu girki NATA aikinsu , Fatima CE ta lek'o ganin hankalin kowa yana ga aikinsa ya Sanya cikin sand'a ta juya ta d'auko duk wani kaya da zata buk'ata da kud'in da k'awarta ta bata , lallab'a ta fice daga gidan ba tare da kowa ya ganta ba ta nufi k'ofar gida, tana tafiya kuwa ta had'u da mai mashin godiya tayi ga Allah duk da a lokacin bata kawo cewar zata samu abin hawa ba saboda dare yayi sosai , ta tsareshi had'i da fad'a masa tashar motocin garin zai kai ta , ya amince ta hau bayan sunyi cinki ta yarda , basu zame ko ina ba sai tasha , tana zuwa kuwa tayi sa'ar samun direban na k'ok'arin tashi Dama sauran mutum d'aya Duke jira aikuwa tanajin motar zariya ce da Sauri ta fad'a bayan ta sallami mai mashin d'in da ta hau , da take tafiyar ta dare ce babu wuya suka bita daga cikin k'auyen suka cilla babban titi , sai a sannan Fatima ta saki dogon numfashi samun nasara .......
Please
Share
&comments
To be continue........
🌸🌸🌸🌸🌹🌹🌹🌹
🌿🌿🌿Nussad🌿🌿🌿
🌸🌹KISHIYAR UWA🌹🌸
(True life story)
🍁 Daga Alk'alamin Nussad🌸
GODIYA GA ALLAH SUBHANAHU WATA'ALA , DAYA BANI DAMAR CIGABA DA RUBUTUN LITTAFIN NAN , TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA GA SHUGABANMU ANNABI MUHAMMAD, DA ALIHI DA SAHABBANSA MASU GIRMA.
BAYAN HAKA NA SADAUKAR DA LITTAFINA GA D'AUKACIN Y'AN UWANA NA SABON RUWA'S FAMILY, LUV U ALL🥰🥰
AJUJI'S FAMILY KUMA HAR DA KU BAZAN MANTA DAKU BA , JINJINAR BAN GIRMA GAREKU ALLAH YA K'ARA ZUMUNCI , AMIN🥰🥰
MAHAIFIYATA ALLAH YA JA DA RANKI , HAJIYA FATIMA TURAKI ADAM , LUV U MY MOM❣️❣️
KISHIYAR UWA FAN'S NA GAISHEKU SOSAI DA SOSAI.
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌹🌹🌹🌹🌹
🌸🌸🌸🌸
🌹🌹🌹
🌸🌸
🌹
SHAFI NA 15-16