Sashe 22
Kishiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A ranar da ta cika wata d'aya tun asubah ya kama hanyar Zaria , karfe shida a k'ofar gidan ta masa, sosai ya ga ta sauya masa, tayi kyau saboda gyaran da aka mata, bayan sun gaggaisa , ya sanarwa da gwaggon na sa abinda ya kawo shi , duk da ya shaida mata tun jiya, tana son zama da d'iyarta amma kuma aure ya raba su, ita kanta Fatima bata ji dad'i da zasu rabu ba , a haka aka zuba mata kayanta a mota, suka yi sallama da kakannin na ta da mahaifiyarta, tana kuka ta shiga motar shima ya shiga ya ta da ta , bayan ya musu sallama, su ka d'auki hanya sai Kaduna............
Please
Share
&
Comments
To be continue.................
🌿🌿🌿NUSSAD🌿🌿🌿
🌸🌹KISHIYAR UWA🌹🌸
(True life story)
🍁Daga Alk'alamin Nussad🌸
SHAFI NA 39_40
KADUNA
Ko da suka k'arasa Kaduna, gidan Mummy kai tsaye su ka wuce, Fatima jin ta take yi a wata duniya ta dabam , ko a mafarki bata tab'a kawo Mummy a matsayin wadda suka had'a dangantaka da ita ba, har su ka Shiga gidan , bata sani ba sai da Ahmad ya d'an bubbuga jikin kujerar sannan tayi firgigit ta dawo daga tunani" sai ki fito in kingama tunanin ", yayi murmushi ita ma murmushin tayi sannan ta fita.
A falo su ka tarar da Mummy , mamaki ne ya kamata , lallai Ahmad yanzu sai da ya je ya d'auko ta, ai ita tama manta yau ne ranar dawowar fatiman kai yaran yanzu ma sai dai a barsu kawai, gaisheta su ka yi ta amsa , sannan ta tambayeta mutanen Zaria , nan su ka shiga hira,Mummy ce ta kalli Fatima , "am daughter ki gama shirinki goben Allah ya kaimu , zaki tare a gidanki dan haka ki gama shirya komai", da " toh , kawai ta amsa , a sanyaye sannan ta tashi "Mummy bacci zanyi ", " OK , je ki kwanta nima bari na shiga d'aki ", da toh ta amsa sannan ta nufi d'akinta , ita ma Mummy haka.
Ahmad su ka bari a falo , yana ganin Mummy ta shiga d'aki yayi zuruf , kamar wani b'arawo ya nufi d'akin Fatima, a hankali ya tura k'ofar d'akin , tana kwance tana niyyar yin bacci, da yake ta juya bata ji shigowarsa ba , jin an zauna a gefen gado , tayi tsammanin ma Mummy ce, sai da k'amshin turarensa ya buge ta, sannan tayi saurin juya wa," am yallab'ai , me kake buk'ata, ta fad'a tana k'ok'arin tashi , tunawa da tayi irin kayan da ke jikinta ya sanya ta koma ta kwanta", sai da ya gama k'are mata kallo sannan ya rab'a gefenta ya kwanta, cikin zaro idanu tace " amma fa yau Mummy tana nan ", " ai na sani ba wani abu nace zanyi ba, bacci zanyi " ya fad'a yana k'ok'arin janyo ta jikin shi ," dan Allah yallab'ai Mummy fa tana nan ", " kar ki dame ni " , abinda yace kenan ya rungume ta, ita dai sai rarraba idanu take yi har bacci ya d'auke su , ko da Mummy ta fito ganin baya nan tayi tsammanin ya tafi sashensa , sai ta koma d'aki ita ma domin ta d'an matse bacci.
A chan b'angare d'aya , LAILA na hanga a zaune tare da wani saurayi , hannunsu a sak'ale da juna, banji mai suke tattaunawa ba, naga dai sai dariya suke shekawa, wa'iyazubillah , kamar ba matar aure ba, " wallahi Aareef kana ji da ni, irin wannan kyauta haka " , cikin dariya shi ma yace " ai in dai zaki dinga sanya ni farin ciki ba abinda bazanyi miki ba, fatana mu kasance har abada", da k'yar su ka rabu da juna , na nufi gida, sai a yanzu take danasanin yin aure , ashe abinda su Aliya suke fad'a mata gaskiya ne , ba komai a cikin aure sai nadama , da ace a lokacin Aareef ta had'u da shi da aurenta tafi jin dad'i , a haka ta shiga gida har a lokacin bai dawo gida ba abinci taci sannan ta haura sama domin hutawa, wayar hannunta ce tayi k'ara , ganin mai kiran ya sanya tayi dariya had'i da d'agawa, " lallai matar nan kin samu duniya kin manta damu ko, aka fad'a daga chan b'angaren ," ah haba Aliya wallahi guy d'in da na had'u da shi ne ya k'ure k'arshe , amma ban manta da ke ba , so ya gida ", daga chan b'angaren Aliya ta amsa, nan su ka ci gaba da hira cikin nishad'i , ita kuma LAILA tana bawa Aliya labarin Aareef, bayan sunyi sallama , ta kishingid'a bacci kuwa yayi awon gaba da ita.
A b'angaren su Fatima kuwa sosai baccin ya musu dad'i musamman ma Ahmad yaji dad'in baccin sosai, sai k'arfe kusan biyu sannan suka tashi, Ahmad ne ya riga tashi dan haka da azama ya nufi k'ofar falo Allah ya taimake shi Mummy bata falo hakan ya sanya ya tafi part d'insa , domin yin sallah.
Ko da Fatima ta tashi , ganin baya nan ta ji dad'i , hakan ya sanya ta shiga toilet domin yin alwala.
Ko da tayi sallah , kasa fita falo tayi gani take yi kamar mummy tasan Ahmad a tare su ka yi bacci da ita , a chan falo ganin Mummy tayi har lokacin Fatima bata fito taci abinci ba , "am baba na duba min kaga daughter ta lafiya , naga har yanzu shiru, ko gajiyar ce har yanzu", tashi yayi ya nufi k'ofar d'akin Fatima, da sallama ya shiga cikin d'akin tana zaune a bakin gadon tana ganin shi tayi zumbur ta mik'e , " ki je inji Mummynki , domin naga yanzu kin k'wace min fada ta", murmushi tayi kawai tayi hanyar waje shima ya bita, ko da su ka gama con abincin , sai ya zauna su ka dasa hira shi da Mummy, ita dai Fatima bata samu su baki kasancewar akan tariyar tata ake yin maganar , ganin abun na su yayi yawa ya sanya ta shiga d'aki ta barsu, sai wajen bayan magriba sannan ya tafi gida .
Ko da ya isa gida , bai bi takan LAILA ba ya nufi d'akinsa , kasancewar yayi sallah a masallacin gidan Mummy , ana shirin yin isha'i , ya nufi masallaci, ana idarwa ya dawo ,a d'aki ya zauna , aiki yayi sosai sannan ya kwanta , da farin cikin gobe ya war haka yana tare da Fatima a gida d'aya , ji yayi kamar ya janyo goben, a haka dai ya lallab'a yayi bacci cikin nishad'i.
A b'angaren LAILA ko da ta ga bai shigo ba, kuma taga dawowarsa hakan ba k'aramin dad'i ya mata ba kasancewar tana charting da wani sabon saurayi da suka had'u a Instagram, sosai guy d'in ya tafi da imaninta, soyayya suke zubawa , kamar ba matar aure ba, a yanzu ma da shi suke chart, ko da yake sauran ma bata rabu da su ba , sai misalin karfe d'aya sannan ta kwanta bayan sunyi sallama..............
Please
Share
&
Comments
To be continue..........
🌿🌿🌿NUSSAD🌿🌿🌿
🌸🌹KISHIYAR UWA🌹🌸
(True life story)
🍁 Daga Alk'alamin Nussad🌸
SHAFI NA 41__42
Washe gari , tun asubah ya tashi , kasancewar akwai aikin da ba'a k'arasa ba a gidan Fatima, kuma ya bar masu aiki , zasu yi aikin kwana, da hanzari ya shirya, k'arfe bakwai daidai ya fita daga gidan bayan ya sanarwa da LAILA cewar zaiyi tafiya, kafin ya dawo ta shirya masa kayansa a jaka,da murnarta ta amsa har sai da yayi mamaki, kasancewar in dai zaiyi tafiya ta dinga k'orafi kenan , yana fita daga gidan ta shiga falo , had'i da lalubar number Aareef , kasancewar ya shaida mata lallai su had'u a yau , dan haka ko da ya d'aga da murnarta ta sanar masa shima yayi farin ciki, sannan ya fad'a mata inda zasu had'u.
A chan b'angare guda bayan ya k'arasa gidan ya tarar da komai ya kammala , saboda ya makara a office ya sanya bai biya gidan mummy ba sai dai ya sanar da ita amgama aikin, saboda ta shaida masa cewar za'a so jere, bayan ya gama sanar mata ne ya wuce office.
A chan gidan mummy kuwa, daga ita sai mahaifiyar Fatima sai kuma aminiyarta , wato hajiya sadiya, kasancewar ta sanar da su dalilin auren d'an nata ya sanya su ma suka yadda da hakan , sannan suka sanya albarka, su da kansu suka yiwa yarinyar ta su jere na gani na fad'a, komai masha Allahu, sai san barka, wannan kenan.
Fatima a zaune a d'aki, yayin da Halima k'awarta tana ta aikin lallashi, " kinga Fatima ki nutsu ki k'watarwa kanki y'anci, kinga dai yadda yanzu rayuwa take , wallahi da ni na samu ya Ahmad da wallahi yaga yadda ake tarairaya, , dan wallahi ko ita LAILAN zata yi mamaki , ki rik'e mijinki hannu biyu biyu , kinji na fad'a miki " , cikin sheshshek'ar kuka Fatima tace " Halima bazaki gane ba ina tsoron LAILA wallahi , saboda irin matan nan ne masu mugun kishi akan mijinta ba abinda bazata yi ba walllahi", " shi yasa na fad'a miki ki jajirce tunda yanzu matsayinku d'aya da ita , a da dai ke ba kowa bace ba amma a yanzu gaji y'ar uwa a gare shi kuma mata , ki sanyawa kanki salama", sosai ta mata nasiha yadda jikin Fatima yayi sanyi sosai ta yaddarwa kanta cewar zata iya , sai da ta ga ta saki jikinta sannan ta kira mai k'unshin da zata mata , dama an gyara mata kai dan haka aka fara yi mata k'unshin.
Sai k'arfe biyar sannan ya samu damar barin office, gida kai tsaye ya nufa, ko da ya k'arasa tarba ta musamman ya samu daga LAILA , yayi mamaki sosai amma haka ya biye mata , ya kammala komai , yadda a b'angaren LAILA ta matsu da tafiyar Ahmad haka shi ma ya matsu da ya tafi , har bakin mota ta raka shi , sai da ta tabbatar ya bar gidan sannan ta juya ciki domin fara shiri, cike da murnarta, hmmmmn LAILA kenan.
Please
Share
&
Comments
To be continue.................
🌿🌿🌿NUSSAD🌿🌿🌿
🌸🌹KISHIYAR UWA🌹🌸
(True life story)
🍁Daga Alk'alamin Nussad🌸
SHAFI NA 39_40
KADUNA
Ko da suka k'arasa Kaduna, gidan Mummy kai tsaye su ka wuce, Fatima jin ta take yi a wata duniya ta dabam , ko a mafarki bata tab'a kawo Mummy a matsayin wadda suka had'a dangantaka da ita ba, har su ka Shiga gidan , bata sani ba sai da Ahmad ya d'an bubbuga jikin kujerar sannan tayi firgigit ta dawo daga tunani" sai ki fito in kingama tunanin ", yayi murmushi ita ma murmushin tayi sannan ta fita.
A falo su ka tarar da Mummy , mamaki ne ya kamata , lallai Ahmad yanzu sai da ya je ya d'auko ta, ai ita tama manta yau ne ranar dawowar fatiman kai yaran yanzu ma sai dai a barsu kawai, gaisheta su ka yi ta amsa , sannan ta tambayeta mutanen Zaria , nan su ka shiga hira,Mummy ce ta kalli Fatima , "am daughter ki gama shirinki goben Allah ya kaimu , zaki tare a gidanki dan haka ki gama shirya komai", da " toh , kawai ta amsa , a sanyaye sannan ta tashi "Mummy bacci zanyi ", " OK , je ki kwanta nima bari na shiga d'aki ", da toh ta amsa sannan ta nufi d'akinta , ita ma Mummy haka.
Ahmad su ka bari a falo , yana ganin Mummy ta shiga d'aki yayi zuruf , kamar wani b'arawo ya nufi d'akin Fatima, a hankali ya tura k'ofar d'akin , tana kwance tana niyyar yin bacci, da yake ta juya bata ji shigowarsa ba , jin an zauna a gefen gado , tayi tsammanin ma Mummy ce, sai da k'amshin turarensa ya buge ta, sannan tayi saurin juya wa," am yallab'ai , me kake buk'ata, ta fad'a tana k'ok'arin tashi , tunawa da tayi irin kayan da ke jikinta ya sanya ta koma ta kwanta", sai da ya gama k'are mata kallo sannan ya rab'a gefenta ya kwanta, cikin zaro idanu tace " amma fa yau Mummy tana nan ", " ai na sani ba wani abu nace zanyi ba, bacci zanyi " ya fad'a yana k'ok'arin janyo ta jikin shi ," dan Allah yallab'ai Mummy fa tana nan ", " kar ki dame ni " , abinda yace kenan ya rungume ta, ita dai sai rarraba idanu take yi har bacci ya d'auke su , ko da Mummy ta fito ganin baya nan tayi tsammanin ya tafi sashensa , sai ta koma d'aki ita ma domin ta d'an matse bacci.
A chan b'angare d'aya , LAILA na hanga a zaune tare da wani saurayi , hannunsu a sak'ale da juna, banji mai suke tattaunawa ba, naga dai sai dariya suke shekawa, wa'iyazubillah , kamar ba matar aure ba, " wallahi Aareef kana ji da ni, irin wannan kyauta haka " , cikin dariya shi ma yace " ai in dai zaki dinga sanya ni farin ciki ba abinda bazanyi miki ba, fatana mu kasance har abada", da k'yar su ka rabu da juna , na nufi gida, sai a yanzu take danasanin yin aure , ashe abinda su Aliya suke fad'a mata gaskiya ne , ba komai a cikin aure sai nadama , da ace a lokacin Aareef ta had'u da shi da aurenta tafi jin dad'i , a haka ta shiga gida har a lokacin bai dawo gida ba abinci taci sannan ta haura sama domin hutawa, wayar hannunta ce tayi k'ara , ganin mai kiran ya sanya tayi dariya had'i da d'agawa, " lallai matar nan kin samu duniya kin manta damu ko, aka fad'a daga chan b'angaren ," ah haba Aliya wallahi guy d'in da na had'u da shi ne ya k'ure k'arshe , amma ban manta da ke ba , so ya gida ", daga chan b'angaren Aliya ta amsa, nan su ka ci gaba da hira cikin nishad'i , ita kuma LAILA tana bawa Aliya labarin Aareef, bayan sunyi sallama , ta kishingid'a bacci kuwa yayi awon gaba da ita.
A b'angaren su Fatima kuwa sosai baccin ya musu dad'i musamman ma Ahmad yaji dad'in baccin sosai, sai k'arfe kusan biyu sannan suka tashi, Ahmad ne ya riga tashi dan haka da azama ya nufi k'ofar falo Allah ya taimake shi Mummy bata falo hakan ya sanya ya tafi part d'insa , domin yin sallah.
Ko da Fatima ta tashi , ganin baya nan ta ji dad'i , hakan ya sanya ta shiga toilet domin yin alwala.
Ko da tayi sallah , kasa fita falo tayi gani take yi kamar mummy tasan Ahmad a tare su ka yi bacci da ita , a chan falo ganin Mummy tayi har lokacin Fatima bata fito taci abinci ba , "am baba na duba min kaga daughter ta lafiya , naga har yanzu shiru, ko gajiyar ce har yanzu", tashi yayi ya nufi k'ofar d'akin Fatima, da sallama ya shiga cikin d'akin tana zaune a bakin gadon tana ganin shi tayi zumbur ta mik'e , " ki je inji Mummynki , domin naga yanzu kin k'wace min fada ta", murmushi tayi kawai tayi hanyar waje shima ya bita, ko da su ka gama con abincin , sai ya zauna su ka dasa hira shi da Mummy, ita dai Fatima bata samu su baki kasancewar akan tariyar tata ake yin maganar , ganin abun na su yayi yawa ya sanya ta shiga d'aki ta barsu, sai wajen bayan magriba sannan ya tafi gida .
Ko da ya isa gida , bai bi takan LAILA ba ya nufi d'akinsa , kasancewar yayi sallah a masallacin gidan Mummy , ana shirin yin isha'i , ya nufi masallaci, ana idarwa ya dawo ,a d'aki ya zauna , aiki yayi sosai sannan ya kwanta , da farin cikin gobe ya war haka yana tare da Fatima a gida d'aya , ji yayi kamar ya janyo goben, a haka dai ya lallab'a yayi bacci cikin nishad'i.
A b'angaren LAILA ko da ta ga bai shigo ba, kuma taga dawowarsa hakan ba k'aramin dad'i ya mata ba kasancewar tana charting da wani sabon saurayi da suka had'u a Instagram, sosai guy d'in ya tafi da imaninta, soyayya suke zubawa , kamar ba matar aure ba, a yanzu ma da shi suke chart, ko da yake sauran ma bata rabu da su ba , sai misalin karfe d'aya sannan ta kwanta bayan sunyi sallama..............
Please
Share
&
Comments
To be continue..........
🌿🌿🌿NUSSAD🌿🌿🌿
🌸🌹KISHIYAR UWA🌹🌸
(True life story)
🍁 Daga Alk'alamin Nussad🌸
SHAFI NA 41__42
Washe gari , tun asubah ya tashi , kasancewar akwai aikin da ba'a k'arasa ba a gidan Fatima, kuma ya bar masu aiki , zasu yi aikin kwana, da hanzari ya shirya, k'arfe bakwai daidai ya fita daga gidan bayan ya sanarwa da LAILA cewar zaiyi tafiya, kafin ya dawo ta shirya masa kayansa a jaka,da murnarta ta amsa har sai da yayi mamaki, kasancewar in dai zaiyi tafiya ta dinga k'orafi kenan , yana fita daga gidan ta shiga falo , had'i da lalubar number Aareef , kasancewar ya shaida mata lallai su had'u a yau , dan haka ko da ya d'aga da murnarta ta sanar masa shima yayi farin ciki, sannan ya fad'a mata inda zasu had'u.
A chan b'angare guda bayan ya k'arasa gidan ya tarar da komai ya kammala , saboda ya makara a office ya sanya bai biya gidan mummy ba sai dai ya sanar da ita amgama aikin, saboda ta shaida masa cewar za'a so jere, bayan ya gama sanar mata ne ya wuce office.
A chan gidan mummy kuwa, daga ita sai mahaifiyar Fatima sai kuma aminiyarta , wato hajiya sadiya, kasancewar ta sanar da su dalilin auren d'an nata ya sanya su ma suka yadda da hakan , sannan suka sanya albarka, su da kansu suka yiwa yarinyar ta su jere na gani na fad'a, komai masha Allahu, sai san barka, wannan kenan.
Fatima a zaune a d'aki, yayin da Halima k'awarta tana ta aikin lallashi, " kinga Fatima ki nutsu ki k'watarwa kanki y'anci, kinga dai yadda yanzu rayuwa take , wallahi da ni na samu ya Ahmad da wallahi yaga yadda ake tarairaya, , dan wallahi ko ita LAILAN zata yi mamaki , ki rik'e mijinki hannu biyu biyu , kinji na fad'a miki " , cikin sheshshek'ar kuka Fatima tace " Halima bazaki gane ba ina tsoron LAILA wallahi , saboda irin matan nan ne masu mugun kishi akan mijinta ba abinda bazata yi ba walllahi", " shi yasa na fad'a miki ki jajirce tunda yanzu matsayinku d'aya da ita , a da dai ke ba kowa bace ba amma a yanzu gaji y'ar uwa a gare shi kuma mata , ki sanyawa kanki salama", sosai ta mata nasiha yadda jikin Fatima yayi sanyi sosai ta yaddarwa kanta cewar zata iya , sai da ta ga ta saki jikinta sannan ta kira mai k'unshin da zata mata , dama an gyara mata kai dan haka aka fara yi mata k'unshin.
Sai k'arfe biyar sannan ya samu damar barin office, gida kai tsaye ya nufa, ko da ya k'arasa tarba ta musamman ya samu daga LAILA , yayi mamaki sosai amma haka ya biye mata , ya kammala komai , yadda a b'angaren LAILA ta matsu da tafiyar Ahmad haka shi ma ya matsu da ya tafi , har bakin mota ta raka shi , sai da ta tabbatar ya bar gidan sannan ta juya ciki domin fara shiri, cike da murnarta, hmmmmn LAILA kenan.