Sashe 3
Kishiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana cikin bacci nan taji an kwara mata , a razane ta farka, "au ke yanzu dan ubanki maimakon ki zo kiyi abin da za ki yi, kin san ki na da aiki shine kika zauna , shegiya mai mugun hali , tashi shegiya kawai" Asabe tayi furucin da bokitin ruwa a hannunta, "to inna zan fito ", “au jiran ki zan yi ki fito dan ubanki" ta tambayeta tana kokarin fincikota hade da kai mata duka, “inna dan Allah kiyi haƙuri wallahi na gaji" , “au ni ki ke cewa kin gaji, lallai wuyanki yayi kauri yau zaki gane kurenki a gidannan fito" , ta fada tana ƙoƙarin shiga daki , dukanta ta shiga yi ba ji ba gani, sai da ta tabbatar bazata iya moruwa ba, duk jikinta ta fasa mata shi "kuma ki tashi kije ki yayo itacen da zakiyi girkin dare tunda yau mallam IIlyan bai dawo ba" tana nufin mahaifinsu su Fatima , da Ƙyar ta tashi da rarrafe ta dauki yagaggen mayafimta ta fita domin yo itace a daji bata dawo daga itacen ba sai chan yamma a lokacin ta gaji sosai, amma haka ta daure ta daura girkin bayan ga Abu a zaune tana faman barar gyad'a tana zubawa a baki .
A haka rayuwar Fatima ta cigaba da tafiya, cike da tsanani, da tsauri, da azabtuwa, har suka kai shekaru goma sha biyar ita da Abu a lokacin ne maƙerin budurci ya fara ƙera su , Fatima ta fito a matsayin kyakykyawar budurwa son kowa, to a sannan ne fa samarin kauye suka ƙara yimata chaaaa a kanta ciki kuwa har da Ado wanda har yanzu yake kan bakansa na soyayya da ita , domin har ya sanar da mahaifiyarsa domin ta sanar da inna Asabe. Duk da wannan kyawun nata daya bayyana, amma hakan bai hana tsantsar wahalar da take ciki , ta bayyana akan kyakykyawar fatarta ba.
A wannan shekarun abubuwa sun faru na daɗi, da akasin haka, ciki kuwa har gama makarantar Fatima, ta firamare wadda da ƙyar hakan ta samu, bayan gwagwarmayar da aka sha da inna Asabe akan harkar makarantar , a yanxu cikin ikon Allah komai ya zama tarihi game da makarantarta ta primary, secondary ce dai bata amince ba, duk kuwa da cewar malaminsu na makaranta, malam Ahmad yayi gwagwarmayar ta cigaba, ganin irin hazakar da take da shi amma fafur ta k'iya , ganin haka ya hakura har ya koma garinsu Kaduna, dama bautar kasa yazo kuma ya gama ya koma ba tare da samun ya samu ya cika burinsa na ganin Fatima ta cigaba da makaranta ba .
A yanzu gashi mahaifinsu girma ya kamashi dan haka baya iya tab'uka komai , duk da, ada ma ba iya yin komai ballantana yanzu da ƙarfinsa ya ƙare duk da yana gudu da ƙyamar abun a zuciyar shi, ganin yadda ake yiwa d'iyarsa , a lokaci da dama ya kan so ya baiwa yarinyarsa labarin mahaifiyarta amma idan ya tashi faɗa mata sai ya kasa , a haka yake barin abin a ransa badan yana so ba, wani lokacin ya kan ji kamar ya yi kuka, idan ya tuna da mahaifiyar Fatima da irin zaman da sukayi lallai ba shakka Fatima ta dauki halin hakuri irin na mahaifiyarta.
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
(Asalin labari)
Shin wai wanene mallam iliyasu mahaifinsu Fatima ?
Malam iliyasu hafaffen garin kano ne, a ƙaramar hukumar wudil yankin darki , yana zaune tare da iyayensa da yayyensa da ƙannensa, mahaifinsa malam Bello matan sa uku , laraba da hansai da kuma Rabi kowacce su tana da yara laraba itace ta fari, tana da yara biyar kuma itace mahaifiyar su mallam Iliya , bayan haka yana da ƙanne, biyu mata biyu, maza biyu, Khadija , Lami, da kuma Habibu da sulaiman , a dakin hansai wadda itace ta biyu yaranta huɗu , Adam, Muhammad, da kuma Salamatu, Rabi yaranta biyu , Hannatu da kuma Hadiza waɗannan sune zuri'ar malam bello .
Mallam bello da iyalansa suna rayuwa cikin nutsuwa da kwanciyar hankali da tarbiyarsu, abin birgewa da sha'awa , yana kulawa da iyalansa yadda kowa kanyi sha'awar waɗannan iyalan . Hakama matan gidan suna da haɗin kai sosai kowacce duk da zaman kauye ne takan taimakawa ƴar uwarta, kuma suna taimakawa mijinsu .
Malam iliya shine babba cikin yaran malam bello, gaba ɗaya ragowar yaran gidan kannensa ne , yakan sanya kannensa su tafi makarantar allo, kasancewar a lokacin babu makarantar boko, ya taimakawa ƙannenansa sosai wajen iliminsu na muhammadiyya.
Sana'ar malam Bello noma idan ya girbe abinda ya shuka ya kai birni ya sayar , aikinsa noma da fatauci ta haka yake rike da iyalansa , lokacin da malam iliya ya kai mizanin samartaka sai ya sanya iliya akan harkar suna tafiya duk Inda yake harkar fataucinsa , in sun tafi sauran yaran maza sukan kula da harkar noma ta yadda zasu taimakawa mahaifinsu, lokacin da suka dawo gida fatauci Allah ya hadashi da Asabe wadda ta kasance yarinyace ƴar mace mahaifinta ya rasu tun tasa ƙarama dan haka ta tashi hannun mahaifiyarta babu kwaɓa , anyi gwagwarmaya kafin auren dan mahaifinsa bai so auren ba, amma ganin d'an nasa ya na ce yana sonta yasa ya barshi a haka akayi auren ba tare duk da ba kowa yaso auren ba amma a haka akayi auren ...........
Please🙏🏻
Share
&comments
To be continue.........
🌿🌿🌿Nussad🌿🌿🌿
🌸🌹Kishiyar uwa🌹🌸
(True life story)
🍁Daga alk'alamin Nussad🌸
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*```We are the moonlight writers we shine all over the world.``🌍`* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
Fatan alkhairi ga duk makaranta littafina , godiya ta musamman ga masu gyara min kura kurai na .
Jinjina gareki aunty nersmah da aunty dije, kuna namijin kokari wajen kuga littafina yayi daidai ba tareda samun matsala ba ina godiya sosai Allah ya bar kauna a tsakanin yan moonlight writer's association amin.
Luv u all my dear fan's🥰 wannan page din sadaukarwa ne gareku.
Shafi na 4️⃣
A haka akayi auren har amarya ta tare , kadahan kadaran ake zaune tsakanin Asabe da dangin malam iliya, babu wani jituwa a tsakaninsu , da yake ita kuma ba wani iya mu'amala tayi ba bata damu da su ba su ma basa zuwa inda take itama haka , a haka har akaci wata hud'u da aurensu a sannan ne ya ci gaba ta tafiye tafiyensa zuwa garuruwa , sai ya hutashshe da mahaifinsa akan ya zauna tunda shi ya kawo karfi sai ya dauki kaninsa su ka ci gaba da tafiya.
Abinda yake damun 'yan uwan malam iliya akan irin rashin mutuncin da matarsa Asabe keyi na bata ganin kowa da mutunci k'annensa basa zuwa gidan yayansu , duk kuwa da irin soyayyar da ta ke tsakaninsu dan shi Allah yayi shi mai so kyautatawa 'yan uwansa , amma kash sai Allah ya hada shi da mata marar sanin darajar mutane.
Har iya wannan tsawon lokacin Asabe ko batan wata bata tab'ayi ba hakan ne ya sanya ta kara bakin jini cikin dangin malam iliya , abinka ga k'auye sai surutai kala kala akan taki haihuwa , dan haka mahaifansa mata su ka fara mishi zancen ya kara aure , a sa'ilin da malam iliya yajewa da Asabe zancen nan kamar wadda zatayi hauka dan kishi , ta ci alwashin matukar dana raye babu shi babu kara aure , cin zarafi kuwa babu Wanda bai sha ba a wajen Asabe , ranar tayi yaji ta sanar da mahaifiyarta , abin ka ga gidan da babu tarbiyya haka mahaifiyar ta ta ta goya mata baya , kwananta d'aya a gidansu washe gari malam iliya yaje gidansu Asabe biko amma anan uwar ta ta ta sauke masa kwandon rashin mutunci da cin al washin ba za'a ayiwa yarinyarta kishiya ba indai tana raye kuwa , hakuri yayi ta bayarwa akan insha Allahu hakan bazata faru ba sannan ta yadda 'yar tata ta koma gidan amma sai da tayi ak'alla sati guda sannan ta koma.
Malam iliya zaune gaban mahaifinsa wanda ya sanya aka masa kiranshi , ya sunkuyar da kai kasa yana sauraron mahaifinsa cike da girmamawa , " kaji abinda na ce maka ba rigada na yanke hukunci na zab'a maka maryama 'yar gidan aminina malam kalla kuma umarni na baka ba shawara ba na yanke aurenka nan da saba'ar wata in Allah ya kaimu da rai da lafiya sai ka sanar da mai dakinka" , "to" ya amsa cike da girmamawa saboda baya tab'a jayayya da mahaifinsa akan komai ma , amma shi kadai ya san halin da ya ke ciki game da zancen da mahaifinsa ya fada masa , yayi masa sallama tareda shiga cikin gidan domin gaisar da iyayenshi mata , sosai inna hansai ta mishi fada tareda kwadaitar dashi romon da ake samu yayin da aka samu zuri'ah , ta gama yi masa nasiha sannan yayi musu sallama tare da innar sa ya tafi gida cike da fargabar ta ya ya zai fadawa matar sa Asabe a haka ya yini ya kwana babu sukuni da walwala , har sai da Asabe ta gane tambayarsa tayi yace mata ba komai wucewa tayi ba tare da kulawa ba .
Washe gari da safe ya tashi da nufin sanar da mai dakin nashi, amma ya kasa , haka yayi ta ajiye da maganar har biki ya kusa saura sati biyu bai sanar da iya ba.
A haka rayuwar Fatima ta cigaba da tafiya, cike da tsanani, da tsauri, da azabtuwa, har suka kai shekaru goma sha biyar ita da Abu a lokacin ne maƙerin budurci ya fara ƙera su , Fatima ta fito a matsayin kyakykyawar budurwa son kowa, to a sannan ne fa samarin kauye suka ƙara yimata chaaaa a kanta ciki kuwa har da Ado wanda har yanzu yake kan bakansa na soyayya da ita , domin har ya sanar da mahaifiyarsa domin ta sanar da inna Asabe. Duk da wannan kyawun nata daya bayyana, amma hakan bai hana tsantsar wahalar da take ciki , ta bayyana akan kyakykyawar fatarta ba.
A wannan shekarun abubuwa sun faru na daɗi, da akasin haka, ciki kuwa har gama makarantar Fatima, ta firamare wadda da ƙyar hakan ta samu, bayan gwagwarmayar da aka sha da inna Asabe akan harkar makarantar , a yanxu cikin ikon Allah komai ya zama tarihi game da makarantarta ta primary, secondary ce dai bata amince ba, duk kuwa da cewar malaminsu na makaranta, malam Ahmad yayi gwagwarmayar ta cigaba, ganin irin hazakar da take da shi amma fafur ta k'iya , ganin haka ya hakura har ya koma garinsu Kaduna, dama bautar kasa yazo kuma ya gama ya koma ba tare da samun ya samu ya cika burinsa na ganin Fatima ta cigaba da makaranta ba .
A yanzu gashi mahaifinsu girma ya kamashi dan haka baya iya tab'uka komai , duk da, ada ma ba iya yin komai ballantana yanzu da ƙarfinsa ya ƙare duk da yana gudu da ƙyamar abun a zuciyar shi, ganin yadda ake yiwa d'iyarsa , a lokaci da dama ya kan so ya baiwa yarinyarsa labarin mahaifiyarta amma idan ya tashi faɗa mata sai ya kasa , a haka yake barin abin a ransa badan yana so ba, wani lokacin ya kan ji kamar ya yi kuka, idan ya tuna da mahaifiyar Fatima da irin zaman da sukayi lallai ba shakka Fatima ta dauki halin hakuri irin na mahaifiyarta.
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
(Asalin labari)
Shin wai wanene mallam iliyasu mahaifinsu Fatima ?
Malam iliyasu hafaffen garin kano ne, a ƙaramar hukumar wudil yankin darki , yana zaune tare da iyayensa da yayyensa da ƙannensa, mahaifinsa malam Bello matan sa uku , laraba da hansai da kuma Rabi kowacce su tana da yara laraba itace ta fari, tana da yara biyar kuma itace mahaifiyar su mallam Iliya , bayan haka yana da ƙanne, biyu mata biyu, maza biyu, Khadija , Lami, da kuma Habibu da sulaiman , a dakin hansai wadda itace ta biyu yaranta huɗu , Adam, Muhammad, da kuma Salamatu, Rabi yaranta biyu , Hannatu da kuma Hadiza waɗannan sune zuri'ar malam bello .
Mallam bello da iyalansa suna rayuwa cikin nutsuwa da kwanciyar hankali da tarbiyarsu, abin birgewa da sha'awa , yana kulawa da iyalansa yadda kowa kanyi sha'awar waɗannan iyalan . Hakama matan gidan suna da haɗin kai sosai kowacce duk da zaman kauye ne takan taimakawa ƴar uwarta, kuma suna taimakawa mijinsu .
Malam iliya shine babba cikin yaran malam bello, gaba ɗaya ragowar yaran gidan kannensa ne , yakan sanya kannensa su tafi makarantar allo, kasancewar a lokacin babu makarantar boko, ya taimakawa ƙannenansa sosai wajen iliminsu na muhammadiyya.
Sana'ar malam Bello noma idan ya girbe abinda ya shuka ya kai birni ya sayar , aikinsa noma da fatauci ta haka yake rike da iyalansa , lokacin da malam iliya ya kai mizanin samartaka sai ya sanya iliya akan harkar suna tafiya duk Inda yake harkar fataucinsa , in sun tafi sauran yaran maza sukan kula da harkar noma ta yadda zasu taimakawa mahaifinsu, lokacin da suka dawo gida fatauci Allah ya hadashi da Asabe wadda ta kasance yarinyace ƴar mace mahaifinta ya rasu tun tasa ƙarama dan haka ta tashi hannun mahaifiyarta babu kwaɓa , anyi gwagwarmaya kafin auren dan mahaifinsa bai so auren ba, amma ganin d'an nasa ya na ce yana sonta yasa ya barshi a haka akayi auren ba tare duk da ba kowa yaso auren ba amma a haka akayi auren ...........
Please🙏🏻
Share
&comments
To be continue.........
🌿🌿🌿Nussad🌿🌿🌿
🌸🌹Kishiyar uwa🌹🌸
(True life story)
🍁Daga alk'alamin Nussad🌸
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*```We are the moonlight writers we shine all over the world.``🌍`* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
Fatan alkhairi ga duk makaranta littafina , godiya ta musamman ga masu gyara min kura kurai na .
Jinjina gareki aunty nersmah da aunty dije, kuna namijin kokari wajen kuga littafina yayi daidai ba tareda samun matsala ba ina godiya sosai Allah ya bar kauna a tsakanin yan moonlight writer's association amin.
Luv u all my dear fan's🥰 wannan page din sadaukarwa ne gareku.
Shafi na 4️⃣
A haka akayi auren har amarya ta tare , kadahan kadaran ake zaune tsakanin Asabe da dangin malam iliya, babu wani jituwa a tsakaninsu , da yake ita kuma ba wani iya mu'amala tayi ba bata damu da su ba su ma basa zuwa inda take itama haka , a haka har akaci wata hud'u da aurensu a sannan ne ya ci gaba ta tafiye tafiyensa zuwa garuruwa , sai ya hutashshe da mahaifinsa akan ya zauna tunda shi ya kawo karfi sai ya dauki kaninsa su ka ci gaba da tafiya.
Abinda yake damun 'yan uwan malam iliya akan irin rashin mutuncin da matarsa Asabe keyi na bata ganin kowa da mutunci k'annensa basa zuwa gidan yayansu , duk kuwa da irin soyayyar da ta ke tsakaninsu dan shi Allah yayi shi mai so kyautatawa 'yan uwansa , amma kash sai Allah ya hada shi da mata marar sanin darajar mutane.
Har iya wannan tsawon lokacin Asabe ko batan wata bata tab'ayi ba hakan ne ya sanya ta kara bakin jini cikin dangin malam iliya , abinka ga k'auye sai surutai kala kala akan taki haihuwa , dan haka mahaifansa mata su ka fara mishi zancen ya kara aure , a sa'ilin da malam iliya yajewa da Asabe zancen nan kamar wadda zatayi hauka dan kishi , ta ci alwashin matukar dana raye babu shi babu kara aure , cin zarafi kuwa babu Wanda bai sha ba a wajen Asabe , ranar tayi yaji ta sanar da mahaifiyarta , abin ka ga gidan da babu tarbiyya haka mahaifiyar ta ta ta goya mata baya , kwananta d'aya a gidansu washe gari malam iliya yaje gidansu Asabe biko amma anan uwar ta ta ta sauke masa kwandon rashin mutunci da cin al washin ba za'a ayiwa yarinyarta kishiya ba indai tana raye kuwa , hakuri yayi ta bayarwa akan insha Allahu hakan bazata faru ba sannan ta yadda 'yar tata ta koma gidan amma sai da tayi ak'alla sati guda sannan ta koma.
Malam iliya zaune gaban mahaifinsa wanda ya sanya aka masa kiranshi , ya sunkuyar da kai kasa yana sauraron mahaifinsa cike da girmamawa , " kaji abinda na ce maka ba rigada na yanke hukunci na zab'a maka maryama 'yar gidan aminina malam kalla kuma umarni na baka ba shawara ba na yanke aurenka nan da saba'ar wata in Allah ya kaimu da rai da lafiya sai ka sanar da mai dakinka" , "to" ya amsa cike da girmamawa saboda baya tab'a jayayya da mahaifinsa akan komai ma , amma shi kadai ya san halin da ya ke ciki game da zancen da mahaifinsa ya fada masa , yayi masa sallama tareda shiga cikin gidan domin gaisar da iyayenshi mata , sosai inna hansai ta mishi fada tareda kwadaitar dashi romon da ake samu yayin da aka samu zuri'ah , ta gama yi masa nasiha sannan yayi musu sallama tare da innar sa ya tafi gida cike da fargabar ta ya ya zai fadawa matar sa Asabe a haka ya yini ya kwana babu sukuni da walwala , har sai da Asabe ta gane tambayarsa tayi yace mata ba komai wucewa tayi ba tare da kulawa ba .
Washe gari da safe ya tashi da nufin sanar da mai dakin nashi, amma ya kasa , haka yayi ta ajiye da maganar har biki ya kusa saura sati biyu bai sanar da iya ba.