← Book details Kishiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 26

Sashe 23

Kishiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yana k'arasawa bakin gidan, yayi horn mai gadi ya bud'e masa, ya shiga , a lokacin su Mummy sun gama jere sun tafi gida, tsayawa yayi ya jera kayansa a wardrobe sosai tsarin gidan ya burge shi , yana gamawa ya nufi gidan Mummy sakamakon kiranshi da tayi akan cewar yaje ya d'auki matarsa ,aikuwa cikin hanzari ya nufi gidan Mummy, uhmmmm sarakan azarb'ab'i kenan.

Ko da ya k'arasa a lokacin angama shirya ta , ba wani dad'ewa yayi ba , mummy tace su tashi su tafi dare ya fara yi , anan fa aka ga abu domin fafur Fatima ta tubure ba inda zata je, koni sai da na mata k'walla , haka ma mummy da k'yar aka lallab'ata ta shiga motar su ka fice daga gidan.

Ko a hanya ma , kukan ta cigaba da yi , yana sauraronta, duk da yana jin kukan har cikin ransa amma haka ya k'yale ta , a hanya ya tsaya ya siya gasashshiya kaza , da fresh milk sannan su ka nufi gidan .

A chan b'angare guda kuwa, LAILA , kwance akan gadon hotel d'in da Aareef ya kama musu, " wallahi baby kanaji da ni irin sannan garab'asa haka, ta fad'a tana duban Aareef da ke fito wa daga cikin toilet da alama daga wanka ya fito" ai baby kad'an ma kikq gani indai ni ne", murmushi tayi, sannan ta tashi ta fad'a jikinshi daga suka cigaba da aikata abinda su ka zo , wa'iyazubillah.

Ko da su ka k'arasa gidan , da kanshi ya mata jagora har cikin gidan, tana lullub'e da mayafi sai k'amshi take yi , a d'aya daga cikin kujerun ya mata masauki, sannan ya nufi cikin kicin da plate ya fito a hannunsa, ya shiga zuzzuba musu, sai da ya gama sannan ya mata umarni da ta sauka su ci tsabar yunwa ce ta sanyata dole ta sauka su ka fara ci duk da a takure take jin ta, bayan sun gama ya nuna mata d'akinta yace ta shiga tayi alwala , bayan ta gama su ka yi sallah , sannan akayi shirin bacci, toh nima daga nan na janyo k'afafuna na fice daga d'akin baki d'aya, saboda kar ace min nayi gulma, wata k'ara da Fatima ta saki ne ya haddasa ni ba shiri na fice daga gidan a miliyan, don tsabar abin tausayi.
Asubah ta gari amarya da Ango.

Ko da na koma lokacin komai ya wakana, Ahmad zaune a gefen gado yana aikin lallashi , ni kuwa nace tunda ka aikata kuwa sai kayi aikin lallashi , komai shi ya mata , sannan ya barta , tayi wankan tsarki, ya shimfid'a mata darduma , ya jasu sallah, albarka kuwa Fatima ta sha ta gurin Ahmad, gani yake duk duniya yafi ko wanne namiji dace , ya kurbu zumar Fatima daidai gwargwado.

Ko da gari ya waye a lokacin Fatima , zazzabi ya rife ta , Ahmad na zaune yana jinya , yaji ana k'wank'wasa k'ofa a hankali ya mik'e saboda kar Fatima ta farka daga baccin wahalar da take yi , yana zuwa ya ga mai gadin Mummy ne ya bashi basket d'in abincin sannan ya juya ya tafi , shi kuma ya koma cikin falo.

Sai k'arfe goma sannan ta tashi a lokacin ya sata tayi brush ya zuba musu abinci , kunun tsamiya ne sai k'osai sai farfesun layan cikin , da lallashi ya dinga bata , yayin da kunya duk ta addabeta , a haka su kayi kalaci , sannan ya bata magani su ka koma bacci.

A chan b'angare d'aya LAILA sai Washe gari ta koma gida , tare da kyautar da Aareef ya mata , aikuwa suna cikin sallama, da Aareef Allah ya jefo da Dr sadeeq , kasancewar ya kira number Ahmad , baya shiga saboda ko shi kansa bai San yayi auren ba , LAILA da ke tsaye bata lura da shi ba dan haka su ka gama duk abinda zasu yi sannan ta shiga gida , da matukar mamaki a fuskarshi ya juya da mota ya bar k'ofar gidan...........

Please

Share
&
Comments

To be continue............

🌿🌿🌿NUSSAD🌿🌿🌿
🌸🌹 KISHIYAR UWA🌹🌸

( True life story)

🍁 Daga Alk'alamin Nussad🌸
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/

*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~

SHAFI NA 43__44

Toh haka dai Ahmad ya kwashe kwana bakwai a gidan Fatima, suna kwasar amarci da soyayya, tun Fatima najin kunya har ta saba , ta sake tare da taimakon k'awarta Halima, sosai take wayar mata da kai, aikuwa tayi amfani da shawararta ta, sai da ya kammala kwanakinsa, sannan ya koma gidan LAILA badan ya so ba.

A haka dai zaman na su ya kasance cikin walwala, da soyayya, yayin da a b'angare d'aya kuma zaman LAILA da Ahmad, ba'a cewa komai, ita dai ta maida hankalinta ga samarinta yayin da a b'angare d'aya, shi kuma Ahmad yake samun wannan damar in kwanan Fatima ya zagayo, a haka su ka koma makaranta, taci gaba da karatunta, bayan ya shaidawa principal d'in makarantar akan cewar zata yi jarabawar gama secondary a aji biyun senior

Hankalin Fatima ya kwanta , sai Sam barka , suna wata na hud'u da aure Allah ya a zurta , zo kuga murna lokacin da Dr ya sanar musu da wannan sakamakon , wanda a wannan lokacin suna daf da fara jarabawa,sosai ya shiga kula da Fatima cikin so da k'aunar juna , tarairaya ba wadda bata gani, ita kanta idan ta zauna godewa Allah kawai take yi , dan ganin Allah ya sauya mata rayuwarta ta da , da jin dad'i , rayuwarta dai abar sam barka da kwatance.

A b'angare d'aya kuma, Mummy tawa Ahmad magana akan cewar tunda yanzu rayuwar Fatima ta sauya, kamata yayi ya kai ta k'auye domin ziyartar y'an uwanta , a kuma shaida musu duk al amarin da suka faru, sosai ya gamsu da haka, ko da ya koma ya sanarwa da Fatima abinda Mummy tace,tayi murna sosai, ya sanar mata da cewar ana gama jarabawarsu, za su tafi , harda mahaifiyarta.

Fatima a zaune a falo, yayin da cikinta a lokacin ya kai wata bakwai,sallama taji anyi hakan ya sanya ta mik'e da k'yar ta nufi bakin k'ofa kasancewar tayi nauyi, da fara'arta ta bud'e k'ofa," ah aunty Aisha barka da zuwa, wallahi tun d'azu nike jiranki ,ta fad'a tana kallon mak'ofciyar ta ta , wadda suka shigo ita da wata bak'uwa, " ke dai bari Fatima wallahi Aliya ce ta tsayar da ni, kinganta nan k'awata ce sai dai ita bata ji ko kad'an," harara r wasa Aliya ta jefawa Aisha, da sannan Fatima ta matsa musu suka wuce, zuwa cikin falon, da hanzari Fatima ta wuce, domin kawo musu ruwa, Aliya ce ta dubi Aisha cikin mamaki bayan ta yi nuni da hannunta zuwa cikin wani photo,wanda Ahmad ya rungume Fatima aka musu photo, sunyi bala'in kyau sosai kamar ka sace su ," Aisha wannan fa waye, ta tambaya cike da mamaki, " lah ai mijinta ne " , cike da mamaki Aliya ta kalle ta, miji kuma ," girgiza kai tayi sannan tayi shiru, ita kad'ai ta san me take k'issimawa a ranta, Ahmad mijin LAILA shine ya zama mijin wannan yarinyar gashi ma ta lura akwai rabo a jikinta, a hanzarce ta sha ruwan da ta k'agauta ta fita ta sanarwa da LAILA halin da ake ciki, ko da suka gama bata koma gidan Aisha ba ta wuce gidan LAILA.

Tun daga bakin falo take k'wallawa LAILA kira, a hanzarce LAILA ta sauko daga upstair, " haba Aliya ta yaya zaki shigo kina min ihu bayan kinsan ina chan ina hutawa ta"," dallah chan wanne irin hutu , kina hutu amma mijinki yana chan shima yana hutawa " ," bangane ba, ta fad'a tana zare idanu"," toh ki sani cewar mijinki ya k'ara aure ba tare da kinsani ba ", wata uwar ashariya ta doka " ni za'ayi was hauka lallai ma amma ta yaya aka yi kika san cewar Ahmad yayi aure kin tunanin zaiyi aure ba tare da cewar ya fad'a min ba ta fad'a cikin k'araji "," yau da idanuna ma na kalla matar Ahmad harda tsohon ciki "," tsohon ciki fa kika ce tabbas kuwa," , " Aliya rakani in ganewa idanuna domin dai na tabbatar da cewar kina min wasa ne ko kuma gaskiya kike fad'a min , cikin hanzari da tashin hankali ta nufi sama domin daukar mayafinta, sai da ta sauko sannan Aliya ta ja ta , suka nufi mota , Allah Allah LAILA take yi su isa aikuwa ko da suka k'arasa sunyi sa'a mai gadi ya jagaya masallaci , aikuwa cikin hanzari suka shiga , sallama Fatima taji ya sanya ta fito bak'uwar d'azu ta gani , gabanta ne ya fad'i ganin wadda suke tare, " aunty LAILA , ta furta da k'arfi ", LAILA ce ta zare idanu wa take shirin gani kamar wannan mayyar yarinyar nan , aikuwa d'aga idanun da zata yi taci karo da hoton Fatima tare da Ahmad, wani uban hanzari ta daka gami da finciko Fatima , wallahi sai na kashe yarinyar nan , hankali na zai huta, jibgarta ta shiga yi tun Fatima na kuka harsai da ta suma sannan suka k'yaleta , aikuwa jini ya b'alle mata ganin haka ya sanya suka yi shirin ficewa daga gidan.
Chapter 23 · 0% Book details