Sashe 30
Hamshaƙiya Uwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Haka na isa gida cikin kwanciyar hankali sai gajiya. suna gidan kitso na shantake muna ta hira da Umma nake yi mata zancan gida. Atake ta kira Abba yace ginda yana kasuwa har yanzu sannan kuma na can bayansa shima yana kasuwa mai na gefe ba zai saida ba. Nace to in na koma gida Tac za muyi maganar da shi. Nima nayo kitso da lalle . Umma ta soya wa su Meema gyada mai gishiri sun ce suna so a saya musu su ci, shine ta auno kwano tace sa kwana biyu suna ci.
Tunmuna hanya naji zuciyata natashi nayi mugunci. Muna isa gida kuwa sai amai kamar zan amayar da hanjin cikina.
Kafin washe gari duk na yi zuru zuru. Mukaje Asuibiti da safe bayan gwaje-gwaje aka gano ina da shigar cikin sati daya.
Murna a gurin Shamaki nace kamar ba ga yaran nan muna da su ba. Yace Baby Haihuwa ita ce ribar Soyayya sai dai in ba a samu ba,sai a hakura.
Washe gari ya tashi da azumi a she wai bakance ya yi zai yi azumi bakwai in Allah ya ba ni ciki. Haka muka taru ina jinya yana Azumi, amai kuwa arana sai inyi sau goma. Ban samu dan sauki ba sai da na yi wata biyu.
Ummara da zamutafi har da yara duka Azima ce dai yaki yace ai yaje da ita. Na kada na raya amma yaki. Sannan a wadan da ya biya mawa har da kawaye Hajiya kamar Hajiya Zaliha da kuma wata Hajiya Zainab wadan da ni na bashi shawara. Nace yana da kyau ka girmama 'Yan uwan da kawaye na mahaifiyarka.
Bayan mundawo lafiya na ga kula da riritawa ni da yarana. cikina har ya soma girma lokacin tuni Shamaki ya saye wannan gidan ya hada da na bayan shi aka bige wa su Umma a nan ana ginawa.
Duk da ina da ciki Shamaki bai daina makale min ba, Wai har nafi lokacin da bani da ciki komai a gurin sa. To duk da ina da ciki ban zauna ragwaf ba. Kitso kunshi, gyaran jiki bana wasa tun da na gane shi din dan kwalliya son gayu ne. Abinda na rage sha shine kayan mata, sai irin su zuma kayan marmari da romon farfesu sai madarar shanu.
Cikin haka haihuwa ta riske ni cikin dare, ranar ba a gurina yake ba. Da yake Umma tace min ana yin juyin wata kuma kuma dama Edd dina bai kai ba, dan haka na daure na cije. Aikuwa haka na kwana ina juyi ana kiran sallar farko kan jariri ya danno bashiri na danna lambar Shamaki na dai ji tana ringing ina nishi sai ganin shi na yi da gudu. Ya kamani nace kan jariri ya turo amma ina ganin zan mutune. Yace "A a zaki haihu lafiya bari a kira likitanmu. Ya kira likita ya fada masa cewa kan Baby ya fito. Likita yace a kwantar da ita, rigingine zai turo Nurse . Haka dai likitan ke fadin ga yadda za a yi cikin yardar Allah sai wani nishi ya taho wanda na sa araina cewa mutuwa ce rai na ne zai fita, ina yi ina salati sai wani yunkuri ya zo min na rike Shamaki gam sai fitar da mukaji gaba daya da mahaifa. Lokacin da Nurse ta iso Baby na cikin bargo likita ya gayawa Shamaki yadda zamu yanke cibiyar, du munyi faca faca cikin jini. Nurse tace "Ikon Allah yau naga wata haihuwa a kan gado. To me aka haifa? Muka kalli juna, nace ina ganin mace ce ta zo ta bude ta duba gaban yaron ta ce ai namiji ne. Dasau Shamaki ya ciro shi yana dubawa, yace da gaske ne amma sam bamu lura ba, domin a hoto mace ce. Shamaki ya yi hamdalar godiya ga Allah.
Zuwa Safiya mun yi fes ni da dana. Muna zaune da Azima sai ga Maman Umar da murnar ta, Abban su ya zo. Kafin wani lokacin gida ya cika da dangi har su Ummanaphora. Tawaje na Juma dama ita ce ta wanke min dana nima ta yi min wanka ta gashe ni ras. Harda kuka wai ta so ace Hajiya ta ga wannan rana. Shamaki ya shigo anan dai aka yi wa dan huduba da Aliyu. Ko wa fadi ya ke dan sak Shamaki.
Shima nace baza ayi taron suna ba. Shamaki ya ce sam ai wannan namiji ne ya san cewa Hajiya ma tana can tana tare da farin ciki. Azima tace "Anty na san saboda ni ki ke yi, wallahi ba komai ki bari a yi, tunda haihuwar Safna ai mutuwar Hajiya tana sabuwa.
Haka dai na hakura dan dole na. Aka yi taron suna a Zeena Event Maganar ga yu ko samun wata gudunmawa kauyanci ne. Tunda Shamaki Gayyata ya yi wadda baiyi ba a bikinmu ba. Manyan mutane kuwa ba a magana harda Gwamna mai ci a wannan lokacin. Ranar na kara sanin waye Shamaki a kasar nan. Jariri har da mota ya samu ba a maganar chaki na kudi.
Naci gaba da wankana cikin kwanciyar hankali sai lokacin na soma kiba namurnure na yi kyau. Ina mamaki idan na kalli madubi, na nemi kasusuwana na rasa na zama Hamshakiya matar manya. Shamaki ya taso ni a gaba saina amshi girki ni kuma
Maman Iman ta zigani tace kar in koma sai na gyara jikina. dan haka na dukufa gyara ciki da wajen. Rannan dai ya gaji ya shigo yace "Baby wai saura kwana nawa ki yi arba'in din nan ne? " Nace sati daya jal ya rage. yace "To ranar za a daura min aure nagaji." Na zaro ido tare da fadin wasa ka ke. Yace "Da kamar bazan karba ba, Hajiya Zaliha ta bani yarta Na ima. Nace kana ba'a ne. Yace "Wallahi." Na mike tsaye da sauri. Kuma ka karba ka yarda?" Yace to ke me kika gani? Na taba baki nace ina ruwa na bayan sai da ku ka gama shawara sannan zaka ce me nagani. Na tashi na fice abina.
Ranar na fara yin fushi maitsanai da Shamaki. Dama Azima ce ke da girki dan haka na asali.ban leka dakinsa ba duk da ina zuwa in taya shi wasu Lissafe lissafe. Shima naga ya share ni bai zo ba, nace mu zuba. Ina bacci na yi mafarkin Hajiya ko dan na kwanta da tunanin maganganunta. Wai tazo tana ce min ina rokon ki rike amanar da na baki ki cika all.kawarin da ki ka dauka.
......
Ki yi masa sassauci a hukunci. Da safe abin ya tsaya min a raina. Duk sanshi da Junior daga masallaci sai ya zo ya tashe shi amma yauv bai shigo ba. Bayan yara sun tafi makaranta na je dakin sa. Juma ta kai abin kari Azima tana zuba masa. Muka gaisa da Azima na gashe shi ya amsa amma ko kallo ban ishe shi ba. Na juya ina mamaki wane laifi na yi mai zafi haka.
Washe gari na amshi girki bai dawo gidan ba har tara mutumin da a gida ya ke yin magariba. Dama ranar ban kira shi ba, shima dama ya daina kirana tunda ya fara fushi, muda sai mu yi waya so biyar a rana. Na dauki waya na kira shi ya daga bai yi magana ba. Nace Ina ka tsaya? Yace "Da sakon ki a hannu na ne? Nace E mana kai kanka ai amana ne a gurina maganar aure ce dan Allah ka daina min wadannan dabi'un ka yi aurenka shike nani? Yace "Ba shike nan ba hakkina da aka hani fa? Nace kai da za a daura maka aure me zaka yi da ni? Kawai dai ka dawo gida. Yace ina hanya daga zance nake. Duk daukana wasa ne sai gashi ya tabbatar domin a gaba na ta kira shi tana tambayar ya zo gida lafiya.
Tunmuna hanya naji zuciyata natashi nayi mugunci. Muna isa gida kuwa sai amai kamar zan amayar da hanjin cikina.
Kafin washe gari duk na yi zuru zuru. Mukaje Asuibiti da safe bayan gwaje-gwaje aka gano ina da shigar cikin sati daya.
Murna a gurin Shamaki nace kamar ba ga yaran nan muna da su ba. Yace Baby Haihuwa ita ce ribar Soyayya sai dai in ba a samu ba,sai a hakura.
Washe gari ya tashi da azumi a she wai bakance ya yi zai yi azumi bakwai in Allah ya ba ni ciki. Haka muka taru ina jinya yana Azumi, amai kuwa arana sai inyi sau goma. Ban samu dan sauki ba sai da na yi wata biyu.
Ummara da zamutafi har da yara duka Azima ce dai yaki yace ai yaje da ita. Na kada na raya amma yaki. Sannan a wadan da ya biya mawa har da kawaye Hajiya kamar Hajiya Zaliha da kuma wata Hajiya Zainab wadan da ni na bashi shawara. Nace yana da kyau ka girmama 'Yan uwan da kawaye na mahaifiyarka.
Bayan mundawo lafiya na ga kula da riritawa ni da yarana. cikina har ya soma girma lokacin tuni Shamaki ya saye wannan gidan ya hada da na bayan shi aka bige wa su Umma a nan ana ginawa.
Duk da ina da ciki Shamaki bai daina makale min ba, Wai har nafi lokacin da bani da ciki komai a gurin sa. To duk da ina da ciki ban zauna ragwaf ba. Kitso kunshi, gyaran jiki bana wasa tun da na gane shi din dan kwalliya son gayu ne. Abinda na rage sha shine kayan mata, sai irin su zuma kayan marmari da romon farfesu sai madarar shanu.
Cikin haka haihuwa ta riske ni cikin dare, ranar ba a gurina yake ba. Da yake Umma tace min ana yin juyin wata kuma kuma dama Edd dina bai kai ba, dan haka na daure na cije. Aikuwa haka na kwana ina juyi ana kiran sallar farko kan jariri ya danno bashiri na danna lambar Shamaki na dai ji tana ringing ina nishi sai ganin shi na yi da gudu. Ya kamani nace kan jariri ya turo amma ina ganin zan mutune. Yace "A a zaki haihu lafiya bari a kira likitanmu. Ya kira likita ya fada masa cewa kan Baby ya fito. Likita yace a kwantar da ita, rigingine zai turo Nurse . Haka dai likitan ke fadin ga yadda za a yi cikin yardar Allah sai wani nishi ya taho wanda na sa araina cewa mutuwa ce rai na ne zai fita, ina yi ina salati sai wani yunkuri ya zo min na rike Shamaki gam sai fitar da mukaji gaba daya da mahaifa. Lokacin da Nurse ta iso Baby na cikin bargo likita ya gayawa Shamaki yadda zamu yanke cibiyar, du munyi faca faca cikin jini. Nurse tace "Ikon Allah yau naga wata haihuwa a kan gado. To me aka haifa? Muka kalli juna, nace ina ganin mace ce ta zo ta bude ta duba gaban yaron ta ce ai namiji ne. Dasau Shamaki ya ciro shi yana dubawa, yace da gaske ne amma sam bamu lura ba, domin a hoto mace ce. Shamaki ya yi hamdalar godiya ga Allah.
Zuwa Safiya mun yi fes ni da dana. Muna zaune da Azima sai ga Maman Umar da murnar ta, Abban su ya zo. Kafin wani lokacin gida ya cika da dangi har su Ummanaphora. Tawaje na Juma dama ita ce ta wanke min dana nima ta yi min wanka ta gashe ni ras. Harda kuka wai ta so ace Hajiya ta ga wannan rana. Shamaki ya shigo anan dai aka yi wa dan huduba da Aliyu. Ko wa fadi ya ke dan sak Shamaki.
Shima nace baza ayi taron suna ba. Shamaki ya ce sam ai wannan namiji ne ya san cewa Hajiya ma tana can tana tare da farin ciki. Azima tace "Anty na san saboda ni ki ke yi, wallahi ba komai ki bari a yi, tunda haihuwar Safna ai mutuwar Hajiya tana sabuwa.
Haka dai na hakura dan dole na. Aka yi taron suna a Zeena Event Maganar ga yu ko samun wata gudunmawa kauyanci ne. Tunda Shamaki Gayyata ya yi wadda baiyi ba a bikinmu ba. Manyan mutane kuwa ba a magana harda Gwamna mai ci a wannan lokacin. Ranar na kara sanin waye Shamaki a kasar nan. Jariri har da mota ya samu ba a maganar chaki na kudi.
Naci gaba da wankana cikin kwanciyar hankali sai lokacin na soma kiba namurnure na yi kyau. Ina mamaki idan na kalli madubi, na nemi kasusuwana na rasa na zama Hamshakiya matar manya. Shamaki ya taso ni a gaba saina amshi girki ni kuma
Maman Iman ta zigani tace kar in koma sai na gyara jikina. dan haka na dukufa gyara ciki da wajen. Rannan dai ya gaji ya shigo yace "Baby wai saura kwana nawa ki yi arba'in din nan ne? " Nace sati daya jal ya rage. yace "To ranar za a daura min aure nagaji." Na zaro ido tare da fadin wasa ka ke. Yace "Da kamar bazan karba ba, Hajiya Zaliha ta bani yarta Na ima. Nace kana ba'a ne. Yace "Wallahi." Na mike tsaye da sauri. Kuma ka karba ka yarda?" Yace to ke me kika gani? Na taba baki nace ina ruwa na bayan sai da ku ka gama shawara sannan zaka ce me nagani. Na tashi na fice abina.
Ranar na fara yin fushi maitsanai da Shamaki. Dama Azima ce ke da girki dan haka na asali.ban leka dakinsa ba duk da ina zuwa in taya shi wasu Lissafe lissafe. Shima naga ya share ni bai zo ba, nace mu zuba. Ina bacci na yi mafarkin Hajiya ko dan na kwanta da tunanin maganganunta. Wai tazo tana ce min ina rokon ki rike amanar da na baki ki cika all.kawarin da ki ka dauka.
......
Ki yi masa sassauci a hukunci. Da safe abin ya tsaya min a raina. Duk sanshi da Junior daga masallaci sai ya zo ya tashe shi amma yauv bai shigo ba. Bayan yara sun tafi makaranta na je dakin sa. Juma ta kai abin kari Azima tana zuba masa. Muka gaisa da Azima na gashe shi ya amsa amma ko kallo ban ishe shi ba. Na juya ina mamaki wane laifi na yi mai zafi haka.
Washe gari na amshi girki bai dawo gidan ba har tara mutumin da a gida ya ke yin magariba. Dama ranar ban kira shi ba, shima dama ya daina kirana tunda ya fara fushi, muda sai mu yi waya so biyar a rana. Na dauki waya na kira shi ya daga bai yi magana ba. Nace Ina ka tsaya? Yace "Da sakon ki a hannu na ne? Nace E mana kai kanka ai amana ne a gurina maganar aure ce dan Allah ka daina min wadannan dabi'un ka yi aurenka shike nani? Yace "Ba shike nan ba hakkina da aka hani fa? Nace kai da za a daura maka aure me zaka yi da ni? Kawai dai ka dawo gida. Yace ina hanya daga zance nake. Duk daukana wasa ne sai gashi ya tabbatar domin a gaba na ta kira shi tana tambayar ya zo gida lafiya.