Sashe 1
Hamshaƙiya Uwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hamshakiyar uwa book 3
Ban an kara ba kawai sai ji nayi ya jani jikinsa, na fara mitar dan Allah a yi sauri kar Umma ta tafi yana faɗin "Haba Baby babu inda zataje." Nace bazan so ta gane me nayi ba fa kamar rashin kunya ne, ɗan Allah nikam kayi saur.... Bakinshi ya saka ya datse surutu na, wanda haka ya tilasta min yin tsit.
Bayan ya samu kanshi na uzzira mishi ya yi wanka ya shirya amma dole na zura mishi ido ya yi salla saboda an riga anyi a masallaci. Ni kuwa ko wakan banyi ba burina dai ya fita. Kafin ya kammala na ɗauki jakarsa na rataya a kafaɗa. Yace "Yau a haka zan tafi bazan saka turare ba?" Nace E yau a haka zaka tafi, domin dama ai danni ake sakawa ko?" Yace haka ne amma ayi haƙuri a ɗan yarfamin ko ba yawa." Na ɗauki wanda hannu na yakai na feshe shi,sannan na ce mu tafi.
A falo Hajiya ce kaɗai take yin salla a gurin salarta,na shiga waige waige ina faɗin to ina ummana ta shiga kuma! Na kalleshi, cikin kukan shagaɓa nace kaga ka gani ko? Gashinan ta tafi ina ta cewa ka yi sauri amma ka ƙi gashi kuma ta tafi ko ɗakina fa bata shiga ba... Da leɓen shi ya nuna min bayana. Cikin sauri na waiwaya sai naga Umma ta fito daga ɗakin Hajiya tana faɗin Baby kukan me kuma ki ke yi haka kamar wata ƙaramar yarinya? Na saki dariya ga hawaye nace na zaci fa ko har kin tafi ne. Tace "Shi ne ki ke yin me?" Shamaki ya ce "Shi ne ta ke kuka dan shagwaɓa." Umma tace Shagaɓar gaske kuwa banda shiririta ina ke ina kukan na tafi tunda ba tare zamu tafi ba.Ta zauna agurin zamanta na aje jakar nace Umma bari in saka miki abincin ko? Tace "Kaɗan zaki sa min don banajin yunwa. Na sa mata kaɗan na loda mata nama, da da hali saina kwashe mata naman ta kaiwa su Jafar, amma gudun zargi ko maganar Hajiya dale dai na haƙura. Hajiya ta idar Shamaki dama ita ya ke jira, domin in ta fara salla sai mutum ya jira dan wani lokacin na kan tambayi kai na ko dai Hajiya sai an amshi sallar sannan take idarwa. Yace "Hajiya na gama shirin zan fita kasuwa. Ta dafa kanshi kamar yadda ta saba. Tace Allah ya yi maka albarka ya bada sa'a ya tsare gabanka da bayan ka."
Yace Ameen ya kalli Umma yace Umma a gaida su Jamila da Abba. Tace zan faɗa musu Allah ya bada sa'a da rabo mai amfani. Yace Ameen Umma na gode.
Na bishi da jaka ina jin takaicin banga ya ba Ummana komai ba har yana wani zai jira su gaisa, a zuciya ta nace sai na roƙe shi yau koda zai hana ni.
Sai da mukaje falon da nake tsayawa, na haɗe girar sama da ƙasa, ya sa hannu ya ɗago fuskanta yace "Me kuma aka ce ya faru Baby?" Nace ce ina son in bawa Ummana wani abu na tsaraba koda kuɗi ne ta saya wa ƙanne na ,amma na kasance bana maganin ko sisi. Cikin shagwaɓa na yi maganar. Ya kwaikwayi muryata yace, "Na ba Hajiya saƙo zata ba Umma shike nan?" Kai masa ɗan dukan wasa nayi ina faɗin na gode. Ya saki fuska ta ya amshi jakar na ɗaga hannu nayi masa bye bye.
Na dawo Umma ta aje abincin tana shan ruwa,na kalli naman kamar ma bata ci ba, nace Umma to ya baƙi ci naman ba kuma? Tace na ci Baby Allah ya amfana. Hajiya tace "Nima dai naga kamar bata ci ba, nan dai kamar gidan ki ne bakya yi fulako ba." Umma tace Alhamdulillahi ai na ci. Hajiya tace "To ko kuma dai a juye ta kaiwa yara dan kinga karnuka za'a baiwa?" Umma tace "Haba dai bazan ɗaukii abinci ba ga shi can a gidan, zuwa zanyi ma in tafi,ƙarfe biyu Abbansu y ace in dawo. Gashi naga ɗaya da rabi ta gota. Hajiya tace "To kuma baki shiga ɗakin nata ba, ga mamakina sai naga Hajiya ta miƙe tana faɗin "Muje in raka ki, nima ban taɓa shiga ɗanikinsu ba, me zakaje ka yi a ɗakin yaro." Umma tace gaskiya dai, bare ko yaushe suna dabdala a nan gurin ki. Tace haka kuwa.
Mamakin Hajiya ya hana ni magana ina biye da su ina tunanin. Hajiya dai ƙila dan kar mu tattauna wata maganar da Ummane ta yi wannan katan katan ɗin ta ƙi bamu fili ko kuwa kulawa ce da mutuntawa ta yi wa Umma.? Bani da amsa dan haka naci gaba da binsu.
Ta nuna wa Umma ko ina tun daga banɗaki har saura ɗakunan Umma dai tana ta addu'a da fatan alkhairi
Sannan suka zauna a kan kujera,na zauna a gaban su kamar mai nema gafara,Umma ta fara magana. "To Hajiya masan dai kuna ta haƙuri da ƙuruciya,yaran yanzu sai anyi haƙuri, a daure ana tsawata mata in tayi ba daidai ba a sata a hanya na hukunci kuma a yi mata ba sai an sanar da mu ba,. Allah ya sa mutu ka raba tsakanin su." Hajiya ta amsa da Ameen, ai ita Rabi'atu bata da matsala yarinya ce mai biyayya laifin ta da nii ɗaya ne. Na zaro ido cikin faɗuwar gaba domin inji laifin nawa. Taci gaba da fadin Duk yadda yarinyar nan zata so mijinta ba za ta yi ya ni Uwar da na haife shi ba Haka ne?" Umma tace "Ko alamar ƙafar ki bata kama ba." Hajiya tace madalla, to wai yarinyar nan nace ta shirya za'a kaita gidan wani malami wanda zai bata taimako Allah cikin ikon sa sai yadda ta yi da mijinta, kina kallo gata dai a cikin irin wannan gida amma bata maganin kwabo ɗaya,ko kina da shi?" Na girgiza kai tare da faɗin bani da shi. Tace yanzu dubi ke ba surukarsa bace, da fatar baki yace miki ki gaida gida,zancan gaskiya hakan ya kyautu?" Umma dai bata yi magana ba. Hajiya ta ci gaba da faɗin. Nasan har maƙota da wasu a dangi sai sun yi da ku,suce 'yar ku tana aure a gidan Alhaji Baita amma har yanzu kuna nan jiya i yau. Koma ace laifita ne ta yi aure gidan daula ta mance da ku, wasu ma cewa za suyi ana baku kun ƙi nunawa ne dan kar ku sammusu, maganar haka take?" Umma tace haka ne. Hajiya ta nuna ni da yatsa tace, "To kinganta nan fir taƙi zuwa gidan malamin har da ɗauke min ƙafa ina hankalce da ita,in ba mijin ta ne a gurina ba ta daina zuwa tunda ta san ba yadda za a yi in yi mata maganar a gaban sa. Ita bazata gurin Malami ba,ba kyau ba sai an mallake shi ba. Jifa sokonci. Kuma ita hakan zai wa amfani,nima kuma ta ɓangare na wani abin in zai min gaddama sai in bi ta hannunta kin san dai ɗan yau."
Mamakin Hajiya ya sa na kasa daina kallon ta, ko dai so take Shamaki ya fara yi mata sujjada. Mutumin da kara in ta aje ba zai taɓa tsallaka shi ba.
Muryar Umma ta katseni, tayi gyaran murya sannan ta ce, Wato Hajiya ni ma dai a nawa ganin sam bai kyautu Baby ta kai sunan mijinta gidan malami ba koda baya iya sauke hakkin da Allah ya ɗora masa nata na aure. Balle duk maganar nan ana yinta ne game da wata kyautatawa wadda in bai yi ba Allah ba zai kamashi da wani laifi ba. Babu shakka ban goyi bayan wannan abin ba. Kuma wai ma Hajiya dan mutane za su ce ko maƙota za su yi damu, Allah na tuba zaka hana bawa ya ɗauki zunubi ne, kace dole sai ya yi aikin lada? Kinga kuwa bamu isa mu hana a yi munafircinmu ba, kuma ko da me kuka bamu Hajiya wannan ba zai hana mai magana ya yi magar shiba. Dan haka don Allah Hajiya kar a nuna mata wannan hanyar, kinsan yaran zamani wataran sai ta tafi da kanta neman wata buƙatar da zata ɓatawa kowa rai. Munriga mun ɗora ta a hanyar sallar dare,in wata damuwa ce ta faɗawa Allah,kuma ta ke yi wa mijinta addu'a Allah ya tsare shi. Ta dubi Hajiya wadda ta zuba mata ido tace, ki yi hakuri in na faɗi ba dai dai ba. Amma shawara ta ƙarshe ku barshi ya ji da masu jiran shi na waje,kinsan 'yan kasuwa ba'a raba su da magauta, a gida sai a tsananta addu'a bare ta ku Hajiya, bakin Mahaifiya ya sha gaban bakin duk wani malami." Hajiya ta sauke ajiyar zuciya ta ce "To ai shikenan tunda kin goye mata baya, na kyale ku ,yanzu ita ko dan kishiyoyin da suka fita ko wasu da zasu shigo bakya bata ƙwarin gwiwa ta amshi taimako ba?"
Umma ta yi 'yar dariya tare da faɗin mijin mace huɗu kuma a tauye shi da mace ɗaya Allah ya rufa masa asiri. Ai Hajiya duk namiji da burin aure ya ke mutuwa saidai in Allah bai ƙaddara mishi ba. Dan Allah ina neman alfarma Hajiya a bar zancan gidan Malamin nan, Abbasu in yaji ba ita ba har ni zai saɓa min ƙwarai.
Juma ta ƙwanƙwasa ƙofa da sallama . Hajiya tace ta shigo , ta miƙo wayar Umma
da ta aje a inda ta zauna a falo, tace "Ana ta kiran wayar ne." Umma ta amsa da sauri tana faɗin Abban su ne.Daidai lokacin kiran ya sake shigowa. Ta ɗaga tana faɗin yi haƙuri wayar tana can sitirum ne mu kuma gamu a cikin ɗani. Muna jiyo murya Abba kasancewar wayar Umma ta samu matsala ko yaushe murya a buɗe ta ke. Yace "Kenan shantakewa ki ka yi a gidan yarinyar ke da na baki ƙarfe biyu yanzu saura mintina ko baro gidan nakiyi ba." Tace yanzu zan taho muna 'yar hira ne da surukarta kaga gata ma ku gaisa.
Ban an kara ba kawai sai ji nayi ya jani jikinsa, na fara mitar dan Allah a yi sauri kar Umma ta tafi yana faɗin "Haba Baby babu inda zataje." Nace bazan so ta gane me nayi ba fa kamar rashin kunya ne, ɗan Allah nikam kayi saur.... Bakinshi ya saka ya datse surutu na, wanda haka ya tilasta min yin tsit.
Bayan ya samu kanshi na uzzira mishi ya yi wanka ya shirya amma dole na zura mishi ido ya yi salla saboda an riga anyi a masallaci. Ni kuwa ko wakan banyi ba burina dai ya fita. Kafin ya kammala na ɗauki jakarsa na rataya a kafaɗa. Yace "Yau a haka zan tafi bazan saka turare ba?" Nace E yau a haka zaka tafi, domin dama ai danni ake sakawa ko?" Yace haka ne amma ayi haƙuri a ɗan yarfamin ko ba yawa." Na ɗauki wanda hannu na yakai na feshe shi,sannan na ce mu tafi.
A falo Hajiya ce kaɗai take yin salla a gurin salarta,na shiga waige waige ina faɗin to ina ummana ta shiga kuma! Na kalleshi, cikin kukan shagaɓa nace kaga ka gani ko? Gashinan ta tafi ina ta cewa ka yi sauri amma ka ƙi gashi kuma ta tafi ko ɗakina fa bata shiga ba... Da leɓen shi ya nuna min bayana. Cikin sauri na waiwaya sai naga Umma ta fito daga ɗakin Hajiya tana faɗin Baby kukan me kuma ki ke yi haka kamar wata ƙaramar yarinya? Na saki dariya ga hawaye nace na zaci fa ko har kin tafi ne. Tace "Shi ne ki ke yin me?" Shamaki ya ce "Shi ne ta ke kuka dan shagwaɓa." Umma tace Shagaɓar gaske kuwa banda shiririta ina ke ina kukan na tafi tunda ba tare zamu tafi ba.Ta zauna agurin zamanta na aje jakar nace Umma bari in saka miki abincin ko? Tace "Kaɗan zaki sa min don banajin yunwa. Na sa mata kaɗan na loda mata nama, da da hali saina kwashe mata naman ta kaiwa su Jafar, amma gudun zargi ko maganar Hajiya dale dai na haƙura. Hajiya ta idar Shamaki dama ita ya ke jira, domin in ta fara salla sai mutum ya jira dan wani lokacin na kan tambayi kai na ko dai Hajiya sai an amshi sallar sannan take idarwa. Yace "Hajiya na gama shirin zan fita kasuwa. Ta dafa kanshi kamar yadda ta saba. Tace Allah ya yi maka albarka ya bada sa'a ya tsare gabanka da bayan ka."
Yace Ameen ya kalli Umma yace Umma a gaida su Jamila da Abba. Tace zan faɗa musu Allah ya bada sa'a da rabo mai amfani. Yace Ameen Umma na gode.
Na bishi da jaka ina jin takaicin banga ya ba Ummana komai ba har yana wani zai jira su gaisa, a zuciya ta nace sai na roƙe shi yau koda zai hana ni.
Sai da mukaje falon da nake tsayawa, na haɗe girar sama da ƙasa, ya sa hannu ya ɗago fuskanta yace "Me kuma aka ce ya faru Baby?" Nace ce ina son in bawa Ummana wani abu na tsaraba koda kuɗi ne ta saya wa ƙanne na ,amma na kasance bana maganin ko sisi. Cikin shagwaɓa na yi maganar. Ya kwaikwayi muryata yace, "Na ba Hajiya saƙo zata ba Umma shike nan?" Kai masa ɗan dukan wasa nayi ina faɗin na gode. Ya saki fuska ta ya amshi jakar na ɗaga hannu nayi masa bye bye.
Na dawo Umma ta aje abincin tana shan ruwa,na kalli naman kamar ma bata ci ba, nace Umma to ya baƙi ci naman ba kuma? Tace na ci Baby Allah ya amfana. Hajiya tace "Nima dai naga kamar bata ci ba, nan dai kamar gidan ki ne bakya yi fulako ba." Umma tace Alhamdulillahi ai na ci. Hajiya tace "To ko kuma dai a juye ta kaiwa yara dan kinga karnuka za'a baiwa?" Umma tace "Haba dai bazan ɗaukii abinci ba ga shi can a gidan, zuwa zanyi ma in tafi,ƙarfe biyu Abbansu y ace in dawo. Gashi naga ɗaya da rabi ta gota. Hajiya tace "To kuma baki shiga ɗakin nata ba, ga mamakina sai naga Hajiya ta miƙe tana faɗin "Muje in raka ki, nima ban taɓa shiga ɗanikinsu ba, me zakaje ka yi a ɗakin yaro." Umma tace gaskiya dai, bare ko yaushe suna dabdala a nan gurin ki. Tace haka kuwa.
Mamakin Hajiya ya hana ni magana ina biye da su ina tunanin. Hajiya dai ƙila dan kar mu tattauna wata maganar da Ummane ta yi wannan katan katan ɗin ta ƙi bamu fili ko kuwa kulawa ce da mutuntawa ta yi wa Umma.? Bani da amsa dan haka naci gaba da binsu.
Ta nuna wa Umma ko ina tun daga banɗaki har saura ɗakunan Umma dai tana ta addu'a da fatan alkhairi
Sannan suka zauna a kan kujera,na zauna a gaban su kamar mai nema gafara,Umma ta fara magana. "To Hajiya masan dai kuna ta haƙuri da ƙuruciya,yaran yanzu sai anyi haƙuri, a daure ana tsawata mata in tayi ba daidai ba a sata a hanya na hukunci kuma a yi mata ba sai an sanar da mu ba,. Allah ya sa mutu ka raba tsakanin su." Hajiya ta amsa da Ameen, ai ita Rabi'atu bata da matsala yarinya ce mai biyayya laifin ta da nii ɗaya ne. Na zaro ido cikin faɗuwar gaba domin inji laifin nawa. Taci gaba da fadin Duk yadda yarinyar nan zata so mijinta ba za ta yi ya ni Uwar da na haife shi ba Haka ne?" Umma tace "Ko alamar ƙafar ki bata kama ba." Hajiya tace madalla, to wai yarinyar nan nace ta shirya za'a kaita gidan wani malami wanda zai bata taimako Allah cikin ikon sa sai yadda ta yi da mijinta, kina kallo gata dai a cikin irin wannan gida amma bata maganin kwabo ɗaya,ko kina da shi?" Na girgiza kai tare da faɗin bani da shi. Tace yanzu dubi ke ba surukarsa bace, da fatar baki yace miki ki gaida gida,zancan gaskiya hakan ya kyautu?" Umma dai bata yi magana ba. Hajiya ta ci gaba da faɗin. Nasan har maƙota da wasu a dangi sai sun yi da ku,suce 'yar ku tana aure a gidan Alhaji Baita amma har yanzu kuna nan jiya i yau. Koma ace laifita ne ta yi aure gidan daula ta mance da ku, wasu ma cewa za suyi ana baku kun ƙi nunawa ne dan kar ku sammusu, maganar haka take?" Umma tace haka ne. Hajiya ta nuna ni da yatsa tace, "To kinganta nan fir taƙi zuwa gidan malamin har da ɗauke min ƙafa ina hankalce da ita,in ba mijin ta ne a gurina ba ta daina zuwa tunda ta san ba yadda za a yi in yi mata maganar a gaban sa. Ita bazata gurin Malami ba,ba kyau ba sai an mallake shi ba. Jifa sokonci. Kuma ita hakan zai wa amfani,nima kuma ta ɓangare na wani abin in zai min gaddama sai in bi ta hannunta kin san dai ɗan yau."
Mamakin Hajiya ya sa na kasa daina kallon ta, ko dai so take Shamaki ya fara yi mata sujjada. Mutumin da kara in ta aje ba zai taɓa tsallaka shi ba.
Muryar Umma ta katseni, tayi gyaran murya sannan ta ce, Wato Hajiya ni ma dai a nawa ganin sam bai kyautu Baby ta kai sunan mijinta gidan malami ba koda baya iya sauke hakkin da Allah ya ɗora masa nata na aure. Balle duk maganar nan ana yinta ne game da wata kyautatawa wadda in bai yi ba Allah ba zai kamashi da wani laifi ba. Babu shakka ban goyi bayan wannan abin ba. Kuma wai ma Hajiya dan mutane za su ce ko maƙota za su yi damu, Allah na tuba zaka hana bawa ya ɗauki zunubi ne, kace dole sai ya yi aikin lada? Kinga kuwa bamu isa mu hana a yi munafircinmu ba, kuma ko da me kuka bamu Hajiya wannan ba zai hana mai magana ya yi magar shiba. Dan haka don Allah Hajiya kar a nuna mata wannan hanyar, kinsan yaran zamani wataran sai ta tafi da kanta neman wata buƙatar da zata ɓatawa kowa rai. Munriga mun ɗora ta a hanyar sallar dare,in wata damuwa ce ta faɗawa Allah,kuma ta ke yi wa mijinta addu'a Allah ya tsare shi. Ta dubi Hajiya wadda ta zuba mata ido tace, ki yi hakuri in na faɗi ba dai dai ba. Amma shawara ta ƙarshe ku barshi ya ji da masu jiran shi na waje,kinsan 'yan kasuwa ba'a raba su da magauta, a gida sai a tsananta addu'a bare ta ku Hajiya, bakin Mahaifiya ya sha gaban bakin duk wani malami." Hajiya ta sauke ajiyar zuciya ta ce "To ai shikenan tunda kin goye mata baya, na kyale ku ,yanzu ita ko dan kishiyoyin da suka fita ko wasu da zasu shigo bakya bata ƙwarin gwiwa ta amshi taimako ba?"
Umma ta yi 'yar dariya tare da faɗin mijin mace huɗu kuma a tauye shi da mace ɗaya Allah ya rufa masa asiri. Ai Hajiya duk namiji da burin aure ya ke mutuwa saidai in Allah bai ƙaddara mishi ba. Dan Allah ina neman alfarma Hajiya a bar zancan gidan Malamin nan, Abbasu in yaji ba ita ba har ni zai saɓa min ƙwarai.
Juma ta ƙwanƙwasa ƙofa da sallama . Hajiya tace ta shigo , ta miƙo wayar Umma
da ta aje a inda ta zauna a falo, tace "Ana ta kiran wayar ne." Umma ta amsa da sauri tana faɗin Abban su ne.Daidai lokacin kiran ya sake shigowa. Ta ɗaga tana faɗin yi haƙuri wayar tana can sitirum ne mu kuma gamu a cikin ɗani. Muna jiyo murya Abba kasancewar wayar Umma ta samu matsala ko yaushe murya a buɗe ta ke. Yace "Kenan shantakewa ki ka yi a gidan yarinyar ke da na baki ƙarfe biyu yanzu saura mintina ko baro gidan nakiyi ba." Tace yanzu zan taho muna 'yar hira ne da surukarta kaga gata ma ku gaisa.