Sashe 29
Hamshaƙiya Uwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mun fara tafiya ba wanda yace kala, sai ya tsaida mota a gefen titi ya Juyo ya kalle ni. Baby naji kunya yau nayi..... Nasa hannu na rufe masa baki,sannan nace tawuce wannan maganar fatana ka kara kiyayewa kuma idan ka ga wata mace wadda ranka ke sonta ka zo ka fada min zaka aureta akwai gurbin mata biyu a gidanka. Yace haba Baby Allah ya bani ke me zanyi da wasu matan kinsan Allah ko Azima darajar Hajiya ne amma wani lokacin ko kallon ta bana son yi." Na ce amma na jima da hanaka fadin haka taci gaba da cin albarkacin Hajiya Ka dinga sakar mata fuska. Yace jiya da kika sani gaba dole na kwanta da ita sai naga duk ta bani tausayi kinga yadda ta ke yin rawar jiki kuwa? Nace ka gani sai ka dauki alhakinta. Yace shikenan duk na bari zan yi yadda ki kace. Na kama hancin shi nace to mijin tace muje gida....
....
Sannu a hankali rayuwa ta canza girma ya hau kaina da kananan shekaru. Ina kokori sosai ganin cewa na kula da kowa yadda ya kamata. Bangaren su Maman Umar ina mu 'a mala da su kamar 'yan uwana na jini kuma sai dai munfi shiri da Maman Iman. Duk da cewa wani lokacin suna dan nuna min wai na mallake musu kani, sai dai na barshi a wasa suke sai dai inyi dariya ince dan Amana ne shi ko dana mallake shi bazan cutar da shiba.
Ko zaman minti biyar ka yi da mu ni da Shamaki sai ka fahimci akwai kauna mai yawa kuma mai karfi tsakanin mu. Ance zomu zauna zo mu saba amma muna kiyaye wa domin ban tuna wani rikici da muka yi ba a tsakaninmu. Sannan ga fahimtar juna.
Bayan hannu na ya fada da tukin mota wata asabar nace yau zan kwashi yarana muje ziyarar dangi. Yace "Ina ne? Nace gidanmu mana. Yace "Karfe nawa za atafi a kuma dawo karfe nawa? " Nace haba Gaye kai dakana kasuwa ma. Yace ni bana son a kai magariba ne Baby wallahi in na dawo bakyanan wani irin kunci nake ji a zuciya ta. " Nace to insha Allahu ana yin la asar zamu dawo. Nace tun jiya nake jin marmarin tuwon Ummanmu. Yace "Allah ya bada sa'a in kuma ba tuwon suka yi ba fa?"
Nace dama izni nake jira in kira Jamlla in ce amin tuwona sukuma yaran nan zan tafi musu da abinci kasan basa kaunar tuwo kuma bana son in saka Umma girki kashi biyu. Kafin ya yi magana Azima ta yi sallama ta shigo da yake muna zaune a falonsa ne.
Ta zauna sannan ta gaishe damu. Muka amsa tayi shiru alamun zatayi magana da shi. Zan tashi ya kamo kunnena yace ina zakije?" Nace zamuje mu yi shiri ne. Yace "Ban sallame ki ba,ki jira." Na kalli Azima wadda ba hakan ta so ba. Nace Ina Safna yau ba a kawo taba. " Tace tana bacci. Nace ta zo ta rakamu cikin gari.
Na fada da tsokana. Azima tace "Cikin gari zaku ke nan yau?" Na ce I. Tace "A gaishe su. Ta kalli Shamaki tace "Yaya Dama zantuna maka maganar wayar ne ina son ina kiran su Maman mu muna gaisawa don Allah." Yace in siyo waya ki ci gaba da Tiktok kenan. nace miki sai dai mai botira kin ce ke bakya son mai botura ba sai ki sha zamanki ba. Na zuba mishi ido ina kallon shi, Ya ki kallona domin ya san na fada mishi ya sai mata wayar tunda ya zo ya fada min yadda suka yi. Ta ta mike zata tafi. Nace Azima wace iri ki ke so? Ta ce Ipone ita na saba rikewa. Ya yi karaf yace "Wallai baza a sai Ipone ba." Na ce ka yi hakuri ka sai mata duk wadda ka ga dama amma banda mai botura.
Ya rike min hanci dakarfi tare da fadin "Ya zanyi tunda kin ce ayi. Na saki yar kara nace Azima knga Yayanki zai ciran hanci ko? Tace "Ummm sai anjima sai kun dawo ku gaishe su." Nace za su ji. Tana fita nace yanzu kai dama baka sai mata wayar ba. Yace to Allah ya baki hakuri yau zan siyo. Yanzu muje ciki dan Allah ki dan yi min tausa ko da minti goma ne. Nace Amma dai iya tausa zanyi maka dai domin na san hali yanzu sai ka canza labarin. Yace banyi alkawarin iyatausa ba sai abinda hali yayi.Na kira wayar cikin gida na fadawa Rahin cewa ta shirya min yaran nan zamu fita. Na dube shi Nace to goyani muje in yi maka. Ya duka na haye bayansa ina dariya, yana fadin sai in goya irinki goma.
Tare muka fito dashi wai shima muje ya gaida su Umma sannan mu aje shi a kasuwa nace dawo wa fab? Yace zan kira Malam Bala. Har mukaje layin mu ba wani gyara da ya yi min atuki. Muna fakin yace "Kin san Allah Baby zaman su Umma a lugun nan ya ishe ni,da zasu yarda sai a sai musu wani gidan koda awata unguwar ne." Nace za su yarda mana kuma kaga wannan gidan na nuna masa wani gida, a bakin titi. Nace masa maigidan ya rasu kwanaki an saka gidan a kasuwa za a saida saidai bansani ba ko an siyar domin Abba naji wani abokin shi ya taya ba a sallama ba,nazo gida lokacin naji suna maganar. Yace ai bashi da girma. Nace kuma ba laifi dan ya yi biyun na su Umman. Yacc "Inda wannan za su sai da (ya nuna na kusa da gidan.)ai da sai a hada ayi musu harda karamin masallaci Allah ya kai ladan a Hajiyarmu. Nace wallahi kuwa, amma bari zan tambaya. Muka shiga layin muna dan gaisawa da wadanda muka sani har muka shiga gida. Jamila ta shimfida tabarma yazauna sukagaisa da Umma ya tambayi Abba tace ya fita. Su Jafar suka gaida shi. Ya mike yace to shi kam zai wuce kasuwa kar in manta duk yadda akayi sai in fada masa. Nace ka manta ne ni zan kai ka yace to ko dai in amshi makullin . Nace ba girman ka bane. Ni zan kaika, Kuma ina son in zaga in nuna wa "yan uwa motata. Nace da Jamila ga sunan ki kai su gidan kitso kafin in kai Dadyn su kasuwa. Tace "To".
Muka fita muka hau mota. Muna tafe muna hira. Nace sai na bishi naga office din sa. Yace "Bana son a kalle min ke. Nace ai ba a sanni ba. Muka taka zuwa gurin Kantin na su yana ta gaisawa da mutane har muka shiga ciki. Nayi murmushi na tuna lokacin da muka zo siyayya da bikinmu. Su Hassan da Dahiru suka taso suka gaishe mu,sannan muka nufi sama inda office dinsa ya ke. Ofishin kato ga kujeru ga bandaki, ga Dininig ga talbijin ga Firji. Nace in tambaye ka wani abu baza kaji haushi ba? Yace "Tambayi." Nace ka taba amfani da wata mace a nan? Yace Haba Baby ai duk abinda mutum zai yi a rayuwa ya tsare kimar shi a gurin sana'ar shi da kuma unguwar da yake, saboda su za su fara bada shedar sa in ya mutu. Ko na Azima wata kaddara ce ko ishara Allah ya nuna mana. Ya zuro hannayen shi a kuguna yace kuma fadin haka da kika yi har kinsa naji ina shi a war yi a nan din." Na ce haba dai Yalabai da zu fa a gida daga tausa ka zarce a ringa daga kafa mana yau ma dai girkin Azima ne.Yace ai sai dare, kuma kinsan irin wannan abin da kwakwalwa ta amsa abinda tunani ya bata sai ya taso ba maganar anyi dazu bane. Mu maza muna samun karin lafiya. Haka dai yaje ya rufe kofa Hassan ya kira yawar Ofishin wai yana da baki, yace su jira akwai wata bakuwar a ciki. Abin mamaki Shamaki ya kusance ni a ofishinsa cikin wani irin doki kamar ranar ya fara gani na. Sai da muka nutsu nashiga na yi wanka tsaf harda ruwan zafi a bandakin. Nace abin mamaki yanda naga kayi kamar ba dazu a gida sai da ka samu natsuwa muka fito ba.Yace "Yace Baby akwai abinda mata basa ganewa. Wato kinsan ita shi'awa da ki ka ganta wata abace da bata da madakata, sannan ba komai ke motsa ta ba, haka karamin abu kan iya motsata.Mu maza muna son abubuwa irin wani abu da ba a saba yi ba. Misali kamar wannan, in ba dama irin haka ta samu ba ai bazaka dakko matar ka daga gida ka yi auratayya da ita a Office ba. Watarana a mota wata rana kaje da matar ka Hotel kamar yadda na taba yi kina ta yi min shirme." Mukasa dariya. Nace Na gane yanzu kawai duk inda ka ke so a shirye na ke. Yace na gode da wannan damar da ki ka bani, domin ina son ire iren haka. Wannan shine yake sa mazan da dama neman mata, saboda suna son irin wannan kalolin amma mata basa ganewa wata sai tace mijinta dan iskane, ko tace yara ita ta girma.
Nace Allah ya kare mana ku da daga sharrin matan waje da duk musulmi yace "Amine."
Nace muje karaka ni ance kana da baki. Muka fito yana fada min cewa "Da yawa matan da muke nema awaje ba su kai matanmu na gida komai ba, wata sai ka gama bukatar ka kana kallonta sai kaji duk ranka ya baci." Nace ga zunubi kuna yawo da shi. Daidai lokacin mun sakko kasa bakin da ke jiran shi har kashi biyu, nace masa kawai ka koma bari in tafi. Yace "A a, ya dube su suka gaisa, yace barin raka Madam Ya kalli Hassan yace wanda suka fara zuwa ka kai su sama. Su Hassan suka ce Anty sai anjima. Nace to sai anjima.
Muka fito yace kina cewa in barki ta yaya zan barki a kasuwar nan ba sai wani ya nemi ya miki magana ba, a haka ma ina jin kar wani ya kalle ki.
....
Sannu a hankali rayuwa ta canza girma ya hau kaina da kananan shekaru. Ina kokori sosai ganin cewa na kula da kowa yadda ya kamata. Bangaren su Maman Umar ina mu 'a mala da su kamar 'yan uwana na jini kuma sai dai munfi shiri da Maman Iman. Duk da cewa wani lokacin suna dan nuna min wai na mallake musu kani, sai dai na barshi a wasa suke sai dai inyi dariya ince dan Amana ne shi ko dana mallake shi bazan cutar da shiba.
Ko zaman minti biyar ka yi da mu ni da Shamaki sai ka fahimci akwai kauna mai yawa kuma mai karfi tsakanin mu. Ance zomu zauna zo mu saba amma muna kiyaye wa domin ban tuna wani rikici da muka yi ba a tsakaninmu. Sannan ga fahimtar juna.
Bayan hannu na ya fada da tukin mota wata asabar nace yau zan kwashi yarana muje ziyarar dangi. Yace "Ina ne? Nace gidanmu mana. Yace "Karfe nawa za atafi a kuma dawo karfe nawa? " Nace haba Gaye kai dakana kasuwa ma. Yace ni bana son a kai magariba ne Baby wallahi in na dawo bakyanan wani irin kunci nake ji a zuciya ta. " Nace to insha Allahu ana yin la asar zamu dawo. Nace tun jiya nake jin marmarin tuwon Ummanmu. Yace "Allah ya bada sa'a in kuma ba tuwon suka yi ba fa?"
Nace dama izni nake jira in kira Jamlla in ce amin tuwona sukuma yaran nan zan tafi musu da abinci kasan basa kaunar tuwo kuma bana son in saka Umma girki kashi biyu. Kafin ya yi magana Azima ta yi sallama ta shigo da yake muna zaune a falonsa ne.
Ta zauna sannan ta gaishe damu. Muka amsa tayi shiru alamun zatayi magana da shi. Zan tashi ya kamo kunnena yace ina zakije?" Nace zamuje mu yi shiri ne. Yace "Ban sallame ki ba,ki jira." Na kalli Azima wadda ba hakan ta so ba. Nace Ina Safna yau ba a kawo taba. " Tace tana bacci. Nace ta zo ta rakamu cikin gari.
Na fada da tsokana. Azima tace "Cikin gari zaku ke nan yau?" Na ce I. Tace "A gaishe su. Ta kalli Shamaki tace "Yaya Dama zantuna maka maganar wayar ne ina son ina kiran su Maman mu muna gaisawa don Allah." Yace in siyo waya ki ci gaba da Tiktok kenan. nace miki sai dai mai botira kin ce ke bakya son mai botura ba sai ki sha zamanki ba. Na zuba mishi ido ina kallon shi, Ya ki kallona domin ya san na fada mishi ya sai mata wayar tunda ya zo ya fada min yadda suka yi. Ta ta mike zata tafi. Nace Azima wace iri ki ke so? Ta ce Ipone ita na saba rikewa. Ya yi karaf yace "Wallai baza a sai Ipone ba." Na ce ka yi hakuri ka sai mata duk wadda ka ga dama amma banda mai botura.
Ya rike min hanci dakarfi tare da fadin "Ya zanyi tunda kin ce ayi. Na saki yar kara nace Azima knga Yayanki zai ciran hanci ko? Tace "Ummm sai anjima sai kun dawo ku gaishe su." Nace za su ji. Tana fita nace yanzu kai dama baka sai mata wayar ba. Yace to Allah ya baki hakuri yau zan siyo. Yanzu muje ciki dan Allah ki dan yi min tausa ko da minti goma ne. Nace Amma dai iya tausa zanyi maka dai domin na san hali yanzu sai ka canza labarin. Yace banyi alkawarin iyatausa ba sai abinda hali yayi.Na kira wayar cikin gida na fadawa Rahin cewa ta shirya min yaran nan zamu fita. Na dube shi Nace to goyani muje in yi maka. Ya duka na haye bayansa ina dariya, yana fadin sai in goya irinki goma.
Tare muka fito dashi wai shima muje ya gaida su Umma sannan mu aje shi a kasuwa nace dawo wa fab? Yace zan kira Malam Bala. Har mukaje layin mu ba wani gyara da ya yi min atuki. Muna fakin yace "Kin san Allah Baby zaman su Umma a lugun nan ya ishe ni,da zasu yarda sai a sai musu wani gidan koda awata unguwar ne." Nace za su yarda mana kuma kaga wannan gidan na nuna masa wani gida, a bakin titi. Nace masa maigidan ya rasu kwanaki an saka gidan a kasuwa za a saida saidai bansani ba ko an siyar domin Abba naji wani abokin shi ya taya ba a sallama ba,nazo gida lokacin naji suna maganar. Yace ai bashi da girma. Nace kuma ba laifi dan ya yi biyun na su Umman. Yacc "Inda wannan za su sai da (ya nuna na kusa da gidan.)ai da sai a hada ayi musu harda karamin masallaci Allah ya kai ladan a Hajiyarmu. Nace wallahi kuwa, amma bari zan tambaya. Muka shiga layin muna dan gaisawa da wadanda muka sani har muka shiga gida. Jamila ta shimfida tabarma yazauna sukagaisa da Umma ya tambayi Abba tace ya fita. Su Jafar suka gaida shi. Ya mike yace to shi kam zai wuce kasuwa kar in manta duk yadda akayi sai in fada masa. Nace ka manta ne ni zan kai ka yace to ko dai in amshi makullin . Nace ba girman ka bane. Ni zan kaika, Kuma ina son in zaga in nuna wa "yan uwa motata. Nace da Jamila ga sunan ki kai su gidan kitso kafin in kai Dadyn su kasuwa. Tace "To".
Muka fita muka hau mota. Muna tafe muna hira. Nace sai na bishi naga office din sa. Yace "Bana son a kalle min ke. Nace ai ba a sanni ba. Muka taka zuwa gurin Kantin na su yana ta gaisawa da mutane har muka shiga ciki. Nayi murmushi na tuna lokacin da muka zo siyayya da bikinmu. Su Hassan da Dahiru suka taso suka gaishe mu,sannan muka nufi sama inda office dinsa ya ke. Ofishin kato ga kujeru ga bandaki, ga Dininig ga talbijin ga Firji. Nace in tambaye ka wani abu baza kaji haushi ba? Yace "Tambayi." Nace ka taba amfani da wata mace a nan? Yace Haba Baby ai duk abinda mutum zai yi a rayuwa ya tsare kimar shi a gurin sana'ar shi da kuma unguwar da yake, saboda su za su fara bada shedar sa in ya mutu. Ko na Azima wata kaddara ce ko ishara Allah ya nuna mana. Ya zuro hannayen shi a kuguna yace kuma fadin haka da kika yi har kinsa naji ina shi a war yi a nan din." Na ce haba dai Yalabai da zu fa a gida daga tausa ka zarce a ringa daga kafa mana yau ma dai girkin Azima ne.Yace ai sai dare, kuma kinsan irin wannan abin da kwakwalwa ta amsa abinda tunani ya bata sai ya taso ba maganar anyi dazu bane. Mu maza muna samun karin lafiya. Haka dai yaje ya rufe kofa Hassan ya kira yawar Ofishin wai yana da baki, yace su jira akwai wata bakuwar a ciki. Abin mamaki Shamaki ya kusance ni a ofishinsa cikin wani irin doki kamar ranar ya fara gani na. Sai da muka nutsu nashiga na yi wanka tsaf harda ruwan zafi a bandakin. Nace abin mamaki yanda naga kayi kamar ba dazu a gida sai da ka samu natsuwa muka fito ba.Yace "Yace Baby akwai abinda mata basa ganewa. Wato kinsan ita shi'awa da ki ka ganta wata abace da bata da madakata, sannan ba komai ke motsa ta ba, haka karamin abu kan iya motsata.Mu maza muna son abubuwa irin wani abu da ba a saba yi ba. Misali kamar wannan, in ba dama irin haka ta samu ba ai bazaka dakko matar ka daga gida ka yi auratayya da ita a Office ba. Watarana a mota wata rana kaje da matar ka Hotel kamar yadda na taba yi kina ta yi min shirme." Mukasa dariya. Nace Na gane yanzu kawai duk inda ka ke so a shirye na ke. Yace na gode da wannan damar da ki ka bani, domin ina son ire iren haka. Wannan shine yake sa mazan da dama neman mata, saboda suna son irin wannan kalolin amma mata basa ganewa wata sai tace mijinta dan iskane, ko tace yara ita ta girma.
Nace Allah ya kare mana ku da daga sharrin matan waje da duk musulmi yace "Amine."
Nace muje karaka ni ance kana da baki. Muka fito yana fada min cewa "Da yawa matan da muke nema awaje ba su kai matanmu na gida komai ba, wata sai ka gama bukatar ka kana kallonta sai kaji duk ranka ya baci." Nace ga zunubi kuna yawo da shi. Daidai lokacin mun sakko kasa bakin da ke jiran shi har kashi biyu, nace masa kawai ka koma bari in tafi. Yace "A a, ya dube su suka gaisa, yace barin raka Madam Ya kalli Hassan yace wanda suka fara zuwa ka kai su sama. Su Hassan suka ce Anty sai anjima. Nace to sai anjima.
Muka fito yace kina cewa in barki ta yaya zan barki a kasuwar nan ba sai wani ya nemi ya miki magana ba, a haka ma ina jin kar wani ya kalle ki.