Sashe 16
Hamshaƙiya Uwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na kwanta kan sallayar ina furta hasbunallahu wa ni'imal wakil. Sannu a hankali sai wani sanyi ya ke sauka a zuciyata.
Ina jin taku tafiyar shi da kamshin turaren shi, ban dago ba har ya yi zaman dirshan a gabana.
Yace "Baby. " Yanzu kam na shiraya yin magana da shi, na dago a hankali na kalle shi. Yace kiyi hakuri ni ma banso haka ba. " Sai lokacin wasu hawaye suka soma zirya a kumatuna. Cikin rawar murya nace tambaya daya zan yi maka, ina son ka daure ka fada min gaskiya. Dasauri yace "Insha Allahu. " Na ce nasha karantawa a littattafan hikaya kuma na yi imani haka ne, so daya ne tak ya ke, kuma mutum daya ake yi wa. Mu kuma a gurin ka Allah kadai ya san adadinmu sai kuma kai, ina son in san wakafi so ina nufin wannan son kwaya daya tak.
Ya mike da Sauri tare da fadin "point of correction! Baby,! ke da Azima zaki ce ba wai baki san adadi ba. Ina da wasu kenan ko ya ki ke nufi? "
Na tashi na koma baki gado na zauna.
Ya zo ya zauna shima, dole ne in latsa masa basira domin in fahimci wasu abubuwa. Nace Duk da na kasance karamar yarinya ba haka yana nufin bani da wayo ko basira ba, sannan duk da kasancewar iyayena talakawa ba haka shima yana nufin baza su binciki wa za su baiwa 'yarsu ba. Sa a daya akayi a lokacin sakamakon ya biyo ta hannu na, sai dai wutar sonka da ta ruru a zuciyata ta sa na boye sakamakon ko nice na canza gurin mummanan shima ya koma kyakykyawa. Ina tunanin wai ko zan iya zama silar canza warka, amma Sai gashi na kusa cinye rabin shekara ban iya wani katabus ba. Na lura Ya firgita, amma da yake namijin duniya ne, sai naga ya dake, yace "To me aka fada a kaina wancan lokacin? Kuma me ya baki tabbaci game da zargin har
kuma ki ka gaskata? "
Na yi murmushin takaici, ka san abinda nake nufi Shamaki, ina jin nauyinka har yanzu bazan so muna tattauna wannan maganar gatsal ba. Ka sani magace ta neman matan ka. Kuma na samu tabbaci ne daga cikin da ka yi wa Azima. Sannan auran ku da aka daura a shekaran jiya, ya samo asaline daga fitar da ku ka yi kai da ita kuka fake da zuwa gidan Maman Nana. Ya yi shiru ya sunkuyar da kai. Na ci gaba, har yanzu ina son ka, ina jin ka a zuciyata, ina son ka bani amsata kafin muci gaba da tattaunawa game da wannan matsalar.
Ya juyo ya kama hannuwana biyu, " Me ki ka sani game da ni? "
Na daga ido na kalle shi. Abubuwa da dama. "Fada min wani abu guda daya." Na juya masa baya Cikin bakin ciki nace, A tafiyar da ka yi zuwa kasar waje ka tafi da wata yarinya. Ya sa hannu ya juyo da ni, muka kalli juna cikin ido hawaye suka soma zubowa daga cikin gida nuna. Nace me ya sa haka Shamaki? Me yasa bazaka aure su ba.? Kai babban mutum ne, kai uba ne na yara mata, ka kare musu mutucin su mana. Ya dora yatsa a kan laben na, ki yi shiru ki taya ni da addu'a Kuma, zanyi iya kokari na inga cewa na daina. Sannan maganar Azima ita ce ta yi ta shige min tana kawo kanta dakina da sunan tambayar wani abu, zuciya bata da kashi Baby amma dai komai ya wuce Insha Allahu. " Na sauke ajiyar zuciya.
Sannan na rungume shi na ce don Allah in ka ga wata a waje ta birge ka to ka zo gida ina nan ina jiranka.
Sannan ga Azima, in kana da bukatar karin aure kar ka damu da ni.
Gam ya katse ni a jikinsa, yace na gode da ki ka
Fahimce ni, dan kuma nasan zaki rufa min asiri ko su Umma baza su ji ba. Nace karma damu.
A cikin satin aka yi gyaran gida ranar lahadi aka kaita, ba kowa sai wasu 'tan uwan su sai yayun Shamaki. Ni kuwa na fito falo gurin su aka gaggaisa ko a jiki na. Maman Iman tace wai meyasa ban yi kunshi ba. Nace mata na ga ba taro za ayi ba shine kawai ban damu kaina ba. Ta taba baki tare da fadin aifa. Wata matsala sai da ya zo wai in hada mishi kaya a karamin akwatin sa, na zuba masa harda jallabiyu da yakan sa da safe, komai da na san yana amfani da shi, na rako shi Hajiya suna zaune da wata kakar Azima. Ya yi musu sallama ya tafi.
Na dan zauna gurin su Jim kadan na tafi daki na na kwanta.
Bacci fa sai ya gagara zuciyata sai hasko min su take yi, gaskiya kishi bala'i ne. Yadda na ga rana haka na ga dare, ina yin salla na fito na shiga kicin Hajiya tana lazimi lokacin. Na gama na zo na gaida Hajiya, tace ya kadaici. " Nace haba ai ba wata damuwa ai yana tafiya kuma in zauna ni daya. Tace haka ne ayi ta hakuri dai. Na yi dan murmushi. Na yi ta zuba ido inga ya zo da safe shiru, ba ango sai wajen azahar sannan ya shigo lokacini ina hadawa Hajiya fura.
A ciki muka amsa masa gaisuwa daga ni har Hajiya. Ya zauna ta kalle shi, me ya hana ka fita kasuwa? Yace hadari ne aka yi dazu sai na kwanta Kuma bacci ya dauke ni. Na mike na nufi sasana, yau sai naji gaba daya haushin sa nake ji. Bansan ya suka kare da Hajiya ba, na garkame dakina. Ina jin kwankwasawar shi na share shi. Domin na zaci cewa zai zo da safe, ko dan Hajiya. Ya kira waya ta ina kallo, sai da ya yi kira biyar a jere sannan ya hakura ya tafi.
Sai da na tabbatar ya tafi sanna na fito. Haka na yi ta masa har kwana uku muna wasan buya. Ranar ya ritsani a kicin muna girkin dare, yacc wa Baba Juma da Tabawa su dan fita. Ya dube ni, "Saboda ke na dawo daga kasuwa yau da wuri. " Na dubw shi kamar wani abu bai faru ba. Nace lafiya zaka dawo saboda ni? Ya zaki fada min memene abinda na yi miki wanda ya sa kake guduna? Nacc ban gane gudu ba. Yace Kinga nifa bazaki yi min wannan azabtar war ba. In wani laifi na yi miki don Allah ki fada min in baki hakuri. " Na yi 'yar dariya . Nace baka min komai ba. Juma ta shigo tana fadin gafaradan ku dai, naji girki na yana kauri.
🖊️🖊️🖊
️Na kalli Juma wadda ta je tana kashe gas ta dan tsaya ko zata tsinci wata Magyar a raina nace kai Juma akwai ta da son jin zance. Yace Juma kin kashe gas din? " Tace na kashe Dannan Ta fice ba don ranta ya so ba. Ya dube ni. "Yi magana ina jinki." Nace Dan Allah ka tafi sabgogin ka, ni ba wani laifi da ka min, haka kuma banga abinda na yi maka ba. Yace
"Ke da Hajiya duk kun canza min ko kinsan wani abu game da haka ki kara min haske? "
Wani sabon haushin sa ya kamani, wato shi bai san ma ya yi wa Hajiya laifi ba, tunda ya yi auran nan bance sun yi zaman minti talatin da shiba wanda na san hakan yana cin ran Hajiyar. Kuma babu tabbacin cewa yana zuwa kasuwar a kan lokaci. Na tabbata Hajiya tana cike da datasanin auren nan. "Ki min magana kin yi shiru. " Ya katse min tunani
Nace kaje ka tambaye ta mana ba mahaifiyar ka ba ce? Dan Allah ka rabu da ni, bana son ka sa raina ya kai ga baci. Na kai karshen maganar cikin daure fuska da fusata. Yace "Wata magana zamu yi ki zo muje daki. " Nayi masa wani irin kallo, Nace a yi ta anan koma wace magana ce. Ya dan yi shiru ya zura min ido, ya ce 'Sai ina ganin kamar ba ke ba, wai munata gaddamar magana zamu yi akan kwana nawa ya kamata in ke yi muku, sai mu yi shawara. " Na yi murmushin takaici, sannan nace yau kuma za ayi shawara da ni, tun da na zo gidanan waya taba jin koda ra'ayi na akan komai ma, da Hajiya ka ke shawara hatta akan abinda ya shafe ni, sai yau ne kuma za ayi shawara da ni saboda za a kwana da ni? Menene a cikin kwanan ne, ka kwana da ni ne fa kawai. Na yi 'yar dariyar takaici, dan Allah kaje in domin kwana ne Shamaki na bar mata kai, kuje ku yi ta kwana. Zaka iya tafiya yanzu ko dai ni in bar maka kicin di?
Ya kasa magana na san yana mamaki na wai kuwa ni ce nake yi masa magana haka. Ganin ba zai fita ba, sai na fice fuu na nufi dakina ko gurin da Hajiya ta ke ban kalla ba.
Ko minti biyar ban yi ba, sai wayar cikin gida ta yi kara, na daga Hajiya tace inzo falonta. Nace a zuciyata yanzu zabga son kai. Suna zaune ita da shi, a nasan yanzu zata goye masa baya.
Ina jin taku tafiyar shi da kamshin turaren shi, ban dago ba har ya yi zaman dirshan a gabana.
Yace "Baby. " Yanzu kam na shiraya yin magana da shi, na dago a hankali na kalle shi. Yace kiyi hakuri ni ma banso haka ba. " Sai lokacin wasu hawaye suka soma zirya a kumatuna. Cikin rawar murya nace tambaya daya zan yi maka, ina son ka daure ka fada min gaskiya. Dasauri yace "Insha Allahu. " Na ce nasha karantawa a littattafan hikaya kuma na yi imani haka ne, so daya ne tak ya ke, kuma mutum daya ake yi wa. Mu kuma a gurin ka Allah kadai ya san adadinmu sai kuma kai, ina son in san wakafi so ina nufin wannan son kwaya daya tak.
Ya mike da Sauri tare da fadin "point of correction! Baby,! ke da Azima zaki ce ba wai baki san adadi ba. Ina da wasu kenan ko ya ki ke nufi? "
Na tashi na koma baki gado na zauna.
Ya zo ya zauna shima, dole ne in latsa masa basira domin in fahimci wasu abubuwa. Nace Duk da na kasance karamar yarinya ba haka yana nufin bani da wayo ko basira ba, sannan duk da kasancewar iyayena talakawa ba haka shima yana nufin baza su binciki wa za su baiwa 'yarsu ba. Sa a daya akayi a lokacin sakamakon ya biyo ta hannu na, sai dai wutar sonka da ta ruru a zuciyata ta sa na boye sakamakon ko nice na canza gurin mummanan shima ya koma kyakykyawa. Ina tunanin wai ko zan iya zama silar canza warka, amma Sai gashi na kusa cinye rabin shekara ban iya wani katabus ba. Na lura Ya firgita, amma da yake namijin duniya ne, sai naga ya dake, yace "To me aka fada a kaina wancan lokacin? Kuma me ya baki tabbaci game da zargin har
kuma ki ka gaskata? "
Na yi murmushin takaici, ka san abinda nake nufi Shamaki, ina jin nauyinka har yanzu bazan so muna tattauna wannan maganar gatsal ba. Ka sani magace ta neman matan ka. Kuma na samu tabbaci ne daga cikin da ka yi wa Azima. Sannan auran ku da aka daura a shekaran jiya, ya samo asaline daga fitar da ku ka yi kai da ita kuka fake da zuwa gidan Maman Nana. Ya yi shiru ya sunkuyar da kai. Na ci gaba, har yanzu ina son ka, ina jin ka a zuciyata, ina son ka bani amsata kafin muci gaba da tattaunawa game da wannan matsalar.
Ya juyo ya kama hannuwana biyu, " Me ki ka sani game da ni? "
Na daga ido na kalle shi. Abubuwa da dama. "Fada min wani abu guda daya." Na juya masa baya Cikin bakin ciki nace, A tafiyar da ka yi zuwa kasar waje ka tafi da wata yarinya. Ya sa hannu ya juyo da ni, muka kalli juna cikin ido hawaye suka soma zubowa daga cikin gida nuna. Nace me ya sa haka Shamaki? Me yasa bazaka aure su ba.? Kai babban mutum ne, kai uba ne na yara mata, ka kare musu mutucin su mana. Ya dora yatsa a kan laben na, ki yi shiru ki taya ni da addu'a Kuma, zanyi iya kokari na inga cewa na daina. Sannan maganar Azima ita ce ta yi ta shige min tana kawo kanta dakina da sunan tambayar wani abu, zuciya bata da kashi Baby amma dai komai ya wuce Insha Allahu. " Na sauke ajiyar zuciya.
Sannan na rungume shi na ce don Allah in ka ga wata a waje ta birge ka to ka zo gida ina nan ina jiranka.
Sannan ga Azima, in kana da bukatar karin aure kar ka damu da ni.
Gam ya katse ni a jikinsa, yace na gode da ki ka
Fahimce ni, dan kuma nasan zaki rufa min asiri ko su Umma baza su ji ba. Nace karma damu.
A cikin satin aka yi gyaran gida ranar lahadi aka kaita, ba kowa sai wasu 'tan uwan su sai yayun Shamaki. Ni kuwa na fito falo gurin su aka gaggaisa ko a jiki na. Maman Iman tace wai meyasa ban yi kunshi ba. Nace mata na ga ba taro za ayi ba shine kawai ban damu kaina ba. Ta taba baki tare da fadin aifa. Wata matsala sai da ya zo wai in hada mishi kaya a karamin akwatin sa, na zuba masa harda jallabiyu da yakan sa da safe, komai da na san yana amfani da shi, na rako shi Hajiya suna zaune da wata kakar Azima. Ya yi musu sallama ya tafi.
Na dan zauna gurin su Jim kadan na tafi daki na na kwanta.
Bacci fa sai ya gagara zuciyata sai hasko min su take yi, gaskiya kishi bala'i ne. Yadda na ga rana haka na ga dare, ina yin salla na fito na shiga kicin Hajiya tana lazimi lokacin. Na gama na zo na gaida Hajiya, tace ya kadaici. " Nace haba ai ba wata damuwa ai yana tafiya kuma in zauna ni daya. Tace haka ne ayi ta hakuri dai. Na yi dan murmushi. Na yi ta zuba ido inga ya zo da safe shiru, ba ango sai wajen azahar sannan ya shigo lokacini ina hadawa Hajiya fura.
A ciki muka amsa masa gaisuwa daga ni har Hajiya. Ya zauna ta kalle shi, me ya hana ka fita kasuwa? Yace hadari ne aka yi dazu sai na kwanta Kuma bacci ya dauke ni. Na mike na nufi sasana, yau sai naji gaba daya haushin sa nake ji. Bansan ya suka kare da Hajiya ba, na garkame dakina. Ina jin kwankwasawar shi na share shi. Domin na zaci cewa zai zo da safe, ko dan Hajiya. Ya kira waya ta ina kallo, sai da ya yi kira biyar a jere sannan ya hakura ya tafi.
Sai da na tabbatar ya tafi sanna na fito. Haka na yi ta masa har kwana uku muna wasan buya. Ranar ya ritsani a kicin muna girkin dare, yacc wa Baba Juma da Tabawa su dan fita. Ya dube ni, "Saboda ke na dawo daga kasuwa yau da wuri. " Na dubw shi kamar wani abu bai faru ba. Nace lafiya zaka dawo saboda ni? Ya zaki fada min memene abinda na yi miki wanda ya sa kake guduna? Nacc ban gane gudu ba. Yace Kinga nifa bazaki yi min wannan azabtar war ba. In wani laifi na yi miki don Allah ki fada min in baki hakuri. " Na yi 'yar dariya . Nace baka min komai ba. Juma ta shigo tana fadin gafaradan ku dai, naji girki na yana kauri.
🖊️🖊️🖊
️Na kalli Juma wadda ta je tana kashe gas ta dan tsaya ko zata tsinci wata Magyar a raina nace kai Juma akwai ta da son jin zance. Yace Juma kin kashe gas din? " Tace na kashe Dannan Ta fice ba don ranta ya so ba. Ya dube ni. "Yi magana ina jinki." Nace Dan Allah ka tafi sabgogin ka, ni ba wani laifi da ka min, haka kuma banga abinda na yi maka ba. Yace
"Ke da Hajiya duk kun canza min ko kinsan wani abu game da haka ki kara min haske? "
Wani sabon haushin sa ya kamani, wato shi bai san ma ya yi wa Hajiya laifi ba, tunda ya yi auran nan bance sun yi zaman minti talatin da shiba wanda na san hakan yana cin ran Hajiyar. Kuma babu tabbacin cewa yana zuwa kasuwar a kan lokaci. Na tabbata Hajiya tana cike da datasanin auren nan. "Ki min magana kin yi shiru. " Ya katse min tunani
Nace kaje ka tambaye ta mana ba mahaifiyar ka ba ce? Dan Allah ka rabu da ni, bana son ka sa raina ya kai ga baci. Na kai karshen maganar cikin daure fuska da fusata. Yace "Wata magana zamu yi ki zo muje daki. " Nayi masa wani irin kallo, Nace a yi ta anan koma wace magana ce. Ya dan yi shiru ya zura min ido, ya ce 'Sai ina ganin kamar ba ke ba, wai munata gaddamar magana zamu yi akan kwana nawa ya kamata in ke yi muku, sai mu yi shawara. " Na yi murmushin takaici, sannan nace yau kuma za ayi shawara da ni, tun da na zo gidanan waya taba jin koda ra'ayi na akan komai ma, da Hajiya ka ke shawara hatta akan abinda ya shafe ni, sai yau ne kuma za ayi shawara da ni saboda za a kwana da ni? Menene a cikin kwanan ne, ka kwana da ni ne fa kawai. Na yi 'yar dariyar takaici, dan Allah kaje in domin kwana ne Shamaki na bar mata kai, kuje ku yi ta kwana. Zaka iya tafiya yanzu ko dai ni in bar maka kicin di?
Ya kasa magana na san yana mamaki na wai kuwa ni ce nake yi masa magana haka. Ganin ba zai fita ba, sai na fice fuu na nufi dakina ko gurin da Hajiya ta ke ban kalla ba.
Ko minti biyar ban yi ba, sai wayar cikin gida ta yi kara, na daga Hajiya tace inzo falonta. Nace a zuciyata yanzu zabga son kai. Suna zaune ita da shi, a nasan yanzu zata goye masa baya.