Sashe 25
Hamshaƙiya Uwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Tun daga ranar da ya kawo min labarinki na fahimci yana matukar son ki, to ina ta tsoro kar a kuma ga lokaci yana ta kure min. Na saka ayi min bincike, naji dadin yadda aka kawo min sakamakon talauci ne kurum abinda suke ganin zai zama aibun ki, na nuna musu talauci ba aibu bane, dan haka ban dakatar da shi ba.
Ba dabi a ta bace in saka malamai wani aiki bayan saukar karatun kur, 'ani wanda ake yi mana duk litinin da Juma a, domin neman kariyar Allah da falalarsa, amma sai gashi na saka ayimin bincike a kanki, bayanin Malamin ya yi min dadi ko da ba gaskiya ya fada min ba. Matsalar daya ce bana son yafi sonki ina tsoro kar kiyi amfani da haka ki cutar min da shi, sai nasa aka hado wani sihiri wanda zaki so shi, da Allah ya ta shi nuna min ban isaba, sai gashi kunci dabinon tare ke dashi. In zaki tuna shine dabinon da na baki wanda kika ci a ranar farko da ki ka kawo ziyarar gaishe ni ke da kanwarki. Ki yafe min wannan cutarwar da na yi miki. Ta sauke a jiyar zuciya. Ta saka hannunta ta sake share min hawayen kan fuskata hannuwan ta sanyi kalau. Tace "Kafin kasa ta rufe idona, kuna zargina da son kaina game da 'ya'yana, ba haka bane ina kokari ne in nuna musu dukkan soyayyata a cikin kwanakin da suka rage min a duniya.
Zuwanki na yarda Allah ya amshi addu'a ta, ya kawo wa Shamaki wadda zai dora kai a kan cinyarta ya yi kuka ta lallashe shi. Kowata uku baki rufa ba ki ka cinye duk wata jarabawa tun kafin in miki ita. Abu daya ne kinyi karama da jan ragamar amma kamar yadda nace Allah ne zai taya ki.
Tun a farkon shekarar nan jikina ya motsa likitana muka yi waya, ya turo min likitocinsu na nan suka dubani, ya sanar da ni cewa ba shakka in har ina da wani abu da zan gabatar in gabatar kafin watannin farko na sabuwar shekarar nan da muka shiga. Abinda Azima da Shamaki suka aikata na dauke shi a matsayin fada Allah ya ke min, in gane wayona da dabarata baza su kaini ba. Ciwona ya tashi saboda damuwar da suka jefani a ciki, wanda tun daga ranar jikina ya motsa gaba daya. Maganin da nake amfani da shi ya daina min aiki.
Likitana yace in taho amma in tabbatar cewa na yi duk wata wasiyya kafin in taho domin ba lallai in koma da raiba.
Muka fashe da kuka a tare sannan ta dora kanta a cinyata, munyi kuka mai tsuma zuciya tsawon minti biyu, sannan ta dago tana lallashi. Kiyi hakuri Rabi'atu, ki dauki girman da Allah ya baki. Cikin dashasshiyar murya da makyarkyata nace bazan iyaba Hajiya abubuwan suna da yawa. Tace zaki iya kinyi na gani, har abinda ya shafi kasuwar Shamaki zaki shigo ciki domin taimaka masa. Na rubuta na aje masa a cikin wasiyyar da na rubuta musu kowa da tasa. Abinda ya shafi sadaka ko zakka kinyi na gani, sannan za a samu karin wasu duk Allah zai haska miki tunda shi ya kawo ki.
Ranar da na kiraki cikin dare jikina ya matsa na zaci ranar zan mutu gashi ina son in tabbatar ko kinsan waye Shamaki. Duk abinda Juma ta ke fada miki da tattunawar da ki ke yi da ita nice na tsara domin in kara tabbatar da wacece ke, haka kuma tura Juma gidan Azima shima nayi ne domin in gano ko za su baki wata matsala bayan bana nan.
Dan haka ki rike Juma sosai tana da Amana zata taimaka miki. Na hanaki zuwa aikin Hajji da Ummara domin in auna hakurinki, na tafi da kishiyar ki domin in jaraba kishinki sai na samu Allah ya miki baiwa ta hakuri kawaici da kuma tsaida zuciya daya tare da dayanta Allah. Ba bukatar sai na fada miki tsakanin Shamaki da "yan"uwansa, domin kin binciko duk ina da bayanin yadda kuka fara, ni ce nasa Juma ta fada miki cewa zan tambaye ki waye Shamaki saboda ina son ki saka hankali ki gano waye shi din. Ni ce na aje littafin da kika karanta. Kuma ina sane da zuwanki gurin tsohuwa a Face. Ta nuna akwatin ta, dakko min waccan akwatin. " Na mike jiki babu karfi na tafi dakko akwatin Hajiya wadda na jasu zuwa hanyar fita danzun nan.
A kasan muka bude dan tashin hankali ya sa bani da karfin da zan iya daga ta in dora saman gado.
Muka zauna kasa muka sa akwatin a tsakiya. Ta ciro littafin tarihin Alhaji Ali Baita. Tace ga mai kyan duk da kinji komai, amma komai yana cikin nan. wancan wanda kika karanta wanda aka yi kuskure ne aka kawo na duba, shine aka rufe gurin kar wani ya karanta.
Ta ciro wata folda ta miko min wannan ki adana masa su, duk wata sheda ta dukiyar Shamaki tana cikin nan. Lauyoyinsa amintattune mutanan Lagos, sune suka je na gabatar musu da ke a matsayin matar Shamaki wadda zata saka ido akan dukiyarsa."
Na zabura, bazan iya ba, banajin yaren turanci bansan Hajiya ta dafa kafadata, ki kwantar da hankalinki, sannu zaki gane komai, abin duk mai sauki ne, kuma su sunajin Hausa. Taci gaba. Zuwa yanzu dai Allah ya sa zan mutu cikin natsuwar cewa zan bar Shamaki a gurin ki. Kar ki manta kuma karki shagala, amana ce. Kin riga kinsan waye Shamaki ma ana, kinsan dabi'unsa masu kyau da marasa kyau, kinsan halayen shi, kin san me yafi so da kuma abinda baya so, kinsan me zai iya da kuma abinda ba zai iya ba. To dan haka kin san ya zaki zauna da shi. Ta dube ni cikin ido, haka ne?" Na daga kai, alamun eh. Tace kinsan Shamaki Allah ya baki hakurin jure duk wasu matsalolin da zaki fuskata.
Ta ce ciro likkafani da ganyen magarya ki saka a waccan durowar domin kar ya yi nisa. Ta ciro wani makullin karami ta bani, tace "Wannan ki saka a jakarki, makullin wannan durowar ce ta daki na, akwai gwalagwalan da nake amfani da su wanda yanzu zai zama gadon yarana, bana son makullin ya fada hannu da ba daya daga cikinsu ba, amana ce ki ba Maman Umar. Ta saka hannu ta ciro dan kunen kunnenta ta ce ki saka wannan a kunnen ki ta ciro zobe daga karamin yatsanta ta ce saka wannan shima, duk lokacin da ki ka kalla sai ki tuna cewa nice na baki, kuma ki yi min addu'a.
Wani irin kunci naji zuciya da idanuna suka kafe da hawayen sai radadin yaji. Nace Hajiya to wai yaushe suka ce miki abin zai faru? Ta lumshe ido cikin fargaba wadda nake gani a idanunta. Tace "Su kansu baza su iya sani ba, bare ni. " Nace ni nafi zargin cewa ba gaskiya bane kuma in Allah ya yarda ba zai faruba, ga ki lafiyar ki lau. Hajiya tace "Ba
ki san abinda nake ji ba da kuma wanda nake gani a mafarki na. Ina tabbatar miki abin zai faru, ki tayani addu'a in hadu da Allah lafiya. In amsa tambayin kabari. " Na sake rike kai. Mutuwa fa, kuma kasan cewa zaka mutu har ma da wa'adi, gaskiya Hajiya jaruma ce wadda ta cancanci a bada labarinta. Na dago kai nace kuma nace Hajiya me yasa ki ka zo dani domin inga wannan tashin hankali?
Tace saboda kar ki shagala da Duniya, kuma hakan zai baki dama ki rike amanar da na bar miki.
Ta ciro turaruka guda biyu, ki aje su kusa da ke za a yi amfani dasu gurin wanka gawata da kuma likkafanina.
Shamaki ya kira direban su Malam Bala lokacin da zasu taso daga filin jirgin Abuja. Sakna wadda take fushi tun da suka taso ta dauki jakarta tana yi masa kallon sama da kasa "Zan iya tafiya yanzu ko?" Domin nan ba Dubai bane ina da masu daukar nauyin na.
Shamaki ya kalleta. "Ko a can ban rike ki ba kece baki ga damar zama ba, Sakna zan fi son haka kije abinki.
Haka ka fada ko, zaka nemeni babu shiri. Ta wuce. Ko kallo bai bita da ba, ya maida kanshi ga abinda ke damunshi, har a Abuja ya kasa samu su Hajiya. Ya danna kiran Maman Umar ta shiga, a ringing na biyu ta daga. Ina ka shige ne mun nemeka mun gaji? Yace farko dai "Hajiya fa wayoyinta basa shiga. " Tace Hajiya suna India suda Baby, muna sa ran ta kaita ne a duba ko akwai matsala ne game da rashin rashin haihuwar ta...
.....
Shamaki ya ji wani dadi ya rufe shi, yace "Alhamdulillah! Ba shakka Hajiya ta gamsu da Baby, Maman Umar Hajiya zata yi min bazata ne. Allah na gode, "
Maman Umar ko dai in bisu ne? " Cikin dariya ta ce dan autan Hajiya, to in kace zaka bisu kwana nawa ne kafin ka samu visa? Kilama har sun dawo. Yace akwai yadda zanyi sai dai ina son in bar Hajiya ta ida muradinta." Fari ciki fal zuciyarsa ya sauka a filin jirgi tun yana mota ya fara waya yana neman visa ta India gaskiya gara ya bi su shima ya yi musu bazata. Domin ya kasa fasssra yanayin da yake ciki.
Ba dabi a ta bace in saka malamai wani aiki bayan saukar karatun kur, 'ani wanda ake yi mana duk litinin da Juma a, domin neman kariyar Allah da falalarsa, amma sai gashi na saka ayimin bincike a kanki, bayanin Malamin ya yi min dadi ko da ba gaskiya ya fada min ba. Matsalar daya ce bana son yafi sonki ina tsoro kar kiyi amfani da haka ki cutar min da shi, sai nasa aka hado wani sihiri wanda zaki so shi, da Allah ya ta shi nuna min ban isaba, sai gashi kunci dabinon tare ke dashi. In zaki tuna shine dabinon da na baki wanda kika ci a ranar farko da ki ka kawo ziyarar gaishe ni ke da kanwarki. Ki yafe min wannan cutarwar da na yi miki. Ta sauke a jiyar zuciya. Ta saka hannunta ta sake share min hawayen kan fuskata hannuwan ta sanyi kalau. Tace "Kafin kasa ta rufe idona, kuna zargina da son kaina game da 'ya'yana, ba haka bane ina kokari ne in nuna musu dukkan soyayyata a cikin kwanakin da suka rage min a duniya.
Zuwanki na yarda Allah ya amshi addu'a ta, ya kawo wa Shamaki wadda zai dora kai a kan cinyarta ya yi kuka ta lallashe shi. Kowata uku baki rufa ba ki ka cinye duk wata jarabawa tun kafin in miki ita. Abu daya ne kinyi karama da jan ragamar amma kamar yadda nace Allah ne zai taya ki.
Tun a farkon shekarar nan jikina ya motsa likitana muka yi waya, ya turo min likitocinsu na nan suka dubani, ya sanar da ni cewa ba shakka in har ina da wani abu da zan gabatar in gabatar kafin watannin farko na sabuwar shekarar nan da muka shiga. Abinda Azima da Shamaki suka aikata na dauke shi a matsayin fada Allah ya ke min, in gane wayona da dabarata baza su kaini ba. Ciwona ya tashi saboda damuwar da suka jefani a ciki, wanda tun daga ranar jikina ya motsa gaba daya. Maganin da nake amfani da shi ya daina min aiki.
Likitana yace in taho amma in tabbatar cewa na yi duk wata wasiyya kafin in taho domin ba lallai in koma da raiba.
Muka fashe da kuka a tare sannan ta dora kanta a cinyata, munyi kuka mai tsuma zuciya tsawon minti biyu, sannan ta dago tana lallashi. Kiyi hakuri Rabi'atu, ki dauki girman da Allah ya baki. Cikin dashasshiyar murya da makyarkyata nace bazan iyaba Hajiya abubuwan suna da yawa. Tace zaki iya kinyi na gani, har abinda ya shafi kasuwar Shamaki zaki shigo ciki domin taimaka masa. Na rubuta na aje masa a cikin wasiyyar da na rubuta musu kowa da tasa. Abinda ya shafi sadaka ko zakka kinyi na gani, sannan za a samu karin wasu duk Allah zai haska miki tunda shi ya kawo ki.
Ranar da na kiraki cikin dare jikina ya matsa na zaci ranar zan mutu gashi ina son in tabbatar ko kinsan waye Shamaki. Duk abinda Juma ta ke fada miki da tattunawar da ki ke yi da ita nice na tsara domin in kara tabbatar da wacece ke, haka kuma tura Juma gidan Azima shima nayi ne domin in gano ko za su baki wata matsala bayan bana nan.
Dan haka ki rike Juma sosai tana da Amana zata taimaka miki. Na hanaki zuwa aikin Hajji da Ummara domin in auna hakurinki, na tafi da kishiyar ki domin in jaraba kishinki sai na samu Allah ya miki baiwa ta hakuri kawaici da kuma tsaida zuciya daya tare da dayanta Allah. Ba bukatar sai na fada miki tsakanin Shamaki da "yan"uwansa, domin kin binciko duk ina da bayanin yadda kuka fara, ni ce nasa Juma ta fada miki cewa zan tambaye ki waye Shamaki saboda ina son ki saka hankali ki gano waye shi din. Ni ce na aje littafin da kika karanta. Kuma ina sane da zuwanki gurin tsohuwa a Face. Ta nuna akwatin ta, dakko min waccan akwatin. " Na mike jiki babu karfi na tafi dakko akwatin Hajiya wadda na jasu zuwa hanyar fita danzun nan.
A kasan muka bude dan tashin hankali ya sa bani da karfin da zan iya daga ta in dora saman gado.
Muka zauna kasa muka sa akwatin a tsakiya. Ta ciro littafin tarihin Alhaji Ali Baita. Tace ga mai kyan duk da kinji komai, amma komai yana cikin nan. wancan wanda kika karanta wanda aka yi kuskure ne aka kawo na duba, shine aka rufe gurin kar wani ya karanta.
Ta ciro wata folda ta miko min wannan ki adana masa su, duk wata sheda ta dukiyar Shamaki tana cikin nan. Lauyoyinsa amintattune mutanan Lagos, sune suka je na gabatar musu da ke a matsayin matar Shamaki wadda zata saka ido akan dukiyarsa."
Na zabura, bazan iya ba, banajin yaren turanci bansan Hajiya ta dafa kafadata, ki kwantar da hankalinki, sannu zaki gane komai, abin duk mai sauki ne, kuma su sunajin Hausa. Taci gaba. Zuwa yanzu dai Allah ya sa zan mutu cikin natsuwar cewa zan bar Shamaki a gurin ki. Kar ki manta kuma karki shagala, amana ce. Kin riga kinsan waye Shamaki ma ana, kinsan dabi'unsa masu kyau da marasa kyau, kinsan halayen shi, kin san me yafi so da kuma abinda baya so, kinsan me zai iya da kuma abinda ba zai iya ba. To dan haka kin san ya zaki zauna da shi. Ta dube ni cikin ido, haka ne?" Na daga kai, alamun eh. Tace kinsan Shamaki Allah ya baki hakurin jure duk wasu matsalolin da zaki fuskata.
Ta ce ciro likkafani da ganyen magarya ki saka a waccan durowar domin kar ya yi nisa. Ta ciro wani makullin karami ta bani, tace "Wannan ki saka a jakarki, makullin wannan durowar ce ta daki na, akwai gwalagwalan da nake amfani da su wanda yanzu zai zama gadon yarana, bana son makullin ya fada hannu da ba daya daga cikinsu ba, amana ce ki ba Maman Umar. Ta saka hannu ta ciro dan kunen kunnenta ta ce ki saka wannan a kunnen ki ta ciro zobe daga karamin yatsanta ta ce saka wannan shima, duk lokacin da ki ka kalla sai ki tuna cewa nice na baki, kuma ki yi min addu'a.
Wani irin kunci naji zuciya da idanuna suka kafe da hawayen sai radadin yaji. Nace Hajiya to wai yaushe suka ce miki abin zai faru? Ta lumshe ido cikin fargaba wadda nake gani a idanunta. Tace "Su kansu baza su iya sani ba, bare ni. " Nace ni nafi zargin cewa ba gaskiya bane kuma in Allah ya yarda ba zai faruba, ga ki lafiyar ki lau. Hajiya tace "Ba
ki san abinda nake ji ba da kuma wanda nake gani a mafarki na. Ina tabbatar miki abin zai faru, ki tayani addu'a in hadu da Allah lafiya. In amsa tambayin kabari. " Na sake rike kai. Mutuwa fa, kuma kasan cewa zaka mutu har ma da wa'adi, gaskiya Hajiya jaruma ce wadda ta cancanci a bada labarinta. Na dago kai nace kuma nace Hajiya me yasa ki ka zo dani domin inga wannan tashin hankali?
Tace saboda kar ki shagala da Duniya, kuma hakan zai baki dama ki rike amanar da na bar miki.
Ta ciro turaruka guda biyu, ki aje su kusa da ke za a yi amfani dasu gurin wanka gawata da kuma likkafanina.
Shamaki ya kira direban su Malam Bala lokacin da zasu taso daga filin jirgin Abuja. Sakna wadda take fushi tun da suka taso ta dauki jakarta tana yi masa kallon sama da kasa "Zan iya tafiya yanzu ko?" Domin nan ba Dubai bane ina da masu daukar nauyin na.
Shamaki ya kalleta. "Ko a can ban rike ki ba kece baki ga damar zama ba, Sakna zan fi son haka kije abinki.
Haka ka fada ko, zaka nemeni babu shiri. Ta wuce. Ko kallo bai bita da ba, ya maida kanshi ga abinda ke damunshi, har a Abuja ya kasa samu su Hajiya. Ya danna kiran Maman Umar ta shiga, a ringing na biyu ta daga. Ina ka shige ne mun nemeka mun gaji? Yace farko dai "Hajiya fa wayoyinta basa shiga. " Tace Hajiya suna India suda Baby, muna sa ran ta kaita ne a duba ko akwai matsala ne game da rashin rashin haihuwar ta...
.....
Shamaki ya ji wani dadi ya rufe shi, yace "Alhamdulillah! Ba shakka Hajiya ta gamsu da Baby, Maman Umar Hajiya zata yi min bazata ne. Allah na gode, "
Maman Umar ko dai in bisu ne? " Cikin dariya ta ce dan autan Hajiya, to in kace zaka bisu kwana nawa ne kafin ka samu visa? Kilama har sun dawo. Yace akwai yadda zanyi sai dai ina son in bar Hajiya ta ida muradinta." Fari ciki fal zuciyarsa ya sauka a filin jirgi tun yana mota ya fara waya yana neman visa ta India gaskiya gara ya bi su shima ya yi musu bazata. Domin ya kasa fasssra yanayin da yake ciki.