Sashe 23
Hamshaƙiya Uwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na baki amanar zumunci Shamaki da ''yan uwanshi, duk yadda za ayi kar ki bari zumuncin su ya samu tangarda! Na baki amanar dangina da dangin Shamaki."
Jikina ya hau bari na soma tunanin ko jirgin ne zai fadi. Nace Hajiya in jirgi ya fadi ai har ni ne baza mu rayu ba. Tayi murmushi, sannan tace ba jirgine zai fadi ba, ina son ki kwantar da hankali ki amshi duk wannan amanar da nake baki, domin zaki iya. Dan Allah kar duk wani me aiki ko wani wanda muke dangantaka da shi ya ce, wayyo yau ina ma Hajiya tana nan. " Nace to Hajiya duk da kince kar in tambaye ki, a can zaki zauna in munje?
Tace za kiji komai. Ta sakar min hannu. Na zura mata ido ina tunanin abinda Hajiya take magana kamar me wasiyya kuma gata dai lafiyar ta lau. Ko kuma dai in mun koma ne zata koma gefe ta sakar min komai? Na sauke ajiyar Allah ya sa ma haka ne zai fi sauki aka ace Duniyar ta ke maganar bari.
Haka dai muka isa Kasar wata mota ta zo ta dauke mu da kayanmu zuwa wani katafaren gida. Mun samu wasu hadimai kamar dai irin wadannan da muke gani a fina finan India. Sune suka amshi kayanmu zuwa wani daki da ke sama. Muka shiga dakin kato ne sosai gadon da kujerun duk a ciki suke. Muka yi salloli sannan muka kwanta duk da cewa garin ma yariga ya waye. Na farka naga Hajiya zaune kan kujera tana shan shayi suna tattaunawa da wani mutum Baindiye wanda nake zaton likita ne, saboda rigar likitoci dake jikin shi. Nabi mamakin yadda mutumin ke yin magana da Hausa duk da cewar Hausar bata goge ba.
.....
Yace "Hajiya ciwo ya zo matakin karshe kamar yadda muka fada miki a wancan lokacin.
Abinda Gwajin mu ya nuna shine kin shiga matakin karshe na ciwon Allah zai iya ganin dama ya barki. Sannan a ka ida bai kamata muna fada miki halin da kike ciki ba, yaranki sune ya kamata su sani ke kuma a boye miki amma kin ce a a. Banda kina da karfin hali da yanzu kin mutu saboda fargaba. " Tace Dr ni musulma ce tun daga lokacin da ku ka fada min ciwona zuwa matakin da nake kai yanzu ban taba jin cewa bazan mutu ba. Kuma fasa yin bautar Allah ba, kuma nasan cewa dole zan mutu watarana ko babu wannan ciwon. Ina da dalilaina da bana son yara na su samu labarin wannan ciwo tsawon shekaru biyar da kuka ce zan iya kaiwa na rayu, da su cikin farin ciki, in da sun sani ni da su zamu rayu cikin damuwa da tashin hankali. Nakasan ce ina boye musu, kuma ina neman mafita ba wadda zata hana mai aukuwa ta auku ba, ina neman mafita ne kawai wadda zata zama madadi a gare su. Nasan babu madadin mahaifiya tabbas, amma ana samu mai share hawaye.
Cikin jimami yake ce mata "Kin samu? " Tace Ina fatan cewa na samu. Ka ga waccan ta nuno inda nake da yatsa tare da waiwayo ta kalli Inda nake kwance, sai muka hada ido fuskarta sharkaf da hawaye ina yin wata irin ajiyar zuciya mai hade da kunshe kuka irin na tashin hankali. Da sauri Hajiya ta mike ta nufo ni.
Maman Umar ta shigo da sallama Falon shiru. Ta nufi ciki, Juma ce take hada miya yayin da Tabawa ke firar doya. Tace "Juma kina ciki?" Juma tace Sannu da zuwa Maman Umar yanzu ki ke tace? "Wallahi nice, ina Mamanmu take ban ganta a cikin ba. " Juma ta bi Maman Umar da kallo, domin bata taba jin ta kira Hajiya da Maman su ba. Maman Umar ta yi yar dariya tace "Juma mamaki ki ke ji ne?" Juma ta ce Ato ai dole inji mamaki na ga wata sabuwar Shagwaba. Ta kawaikwayi muryar Maman Umar wai Mamanmu.
Maman Umar ta yi dariya tace kin san Allah ina zaune naji kawai ina son ganin Hajiya na kira wayar ta sai naji bata shiga, shine na ca bari dai inzo." Juma ta saka dariya tace wannan karon Hajiya ta yi wa kowa bazata, nifa kawai kira na tayi tace tanason za su yi tafiya da matar Shamaki Uwargidan. Tace mudawo nan gidan har Azima, a kula da gida da kuma yara. Nace ina za suje tace kasar waje. Cikin tsananin mamaki Maman Umar ta ce, Hajiya ce kuma yau tayi tafiya ba tare da saninmu ba?"
Juma tace ina zaton Uban dakina shine kadai zai iya sanin tafiyar nan. Maman Umar tace to ina taje kuma wai harda matar Shamaki? " Juma tace ni dai bansan kasar ba, ta dai cemin kasar waje.
Maman Umar ta danno lambar Baby tana fadin ba lallai a samu Baby a waya ba saboda layinta in ba anyi masa aiki ba to fa ba zai yi amfani tana wata kasar ba.
Layin kuwa bai shiga ba. Ta kira layin Maman Nana wadda tasan ko Hajiya ta boye ma wani wata magana sai ta fadawa mata. Suka gaisa, tace "Wai kuwa Maman Nana Hajiya ta fada miki zata yi tafiya? Maman Nana tace a a gaskiya bata fada min ba, ina taje? Ban sani ba, ji nayi ina son ganinta na zo sai kuma wai ashe sun fita waje da matar Shamaki. "Wace kasa?" Maman Nana ta tambaya cikin mamaki. Maman Umar tace bansani ba nima, ga wayoyin ta duk basa shiga. Maman Nana ta yi shiru, can tace "Tofa! To kuma Shamaki ai ya sani ko? " Maman Nana ta ce Shamaki yana da masaniya ki kira lambarsa ta Dubai ko ta Chaina Nima zan kira.
Har Maman Umar ta tafi bata samu layin Shamaki ba, kuma duk su Maman Afra da Maman Iman babu wadda bata kira ba amma basu san komai game da tafiyar Hajiya ba. Gashi wayar Shamaki ta kasa samuwa.
Maman Umar ta kira su gaba daya zuwa gidan ta, tace itafa tana ji a jikinta akwai wani abu, tana zargin Shamaki ya gudune domin kar Hajiya ta sa shi ya saki Baby. " Maman Iman tace ni kuma na kula Hajiya tana son Baby, kila dai ta fita da ita ne a dubata ko zata samu haihuwa domin kusan so biyu tana yi min magana akan rashin haihuwar Baby.? "
Maman Nana tace "Hakan ma zai iya yiwuwa. " . Maman Afra tace in har batun Haihuwa ne nasan Hajiya
India zata nufa a duba mata lafiyar Baby, dan haka sai mu bincika mu gani ko can ta tafi idan canne sai mu daina daga hankalinmu.
Take Maman Umar ta kira wani a office din masu yin bizar wanda tasan shine Hajiya ke yin Hulda da shi. Ta tambaye shi ko bizar wace kasa ya yi wa Hajiya? Yace ta India ce, maman Umar ta tambaye shi tsawo lokacin da bizar zata dauka. Yace "sati biyu ne ta yi masa godiya suka yi sallama.
Daga nan suka ce bari su jira har su dawo, sai dai cikin su kowa na mamakin abinda yasa Hajiya ta ki tayi musu sallama. Domin koda Hajiya take boye musu wani abu na sirrin gidan ta, bata taba boye musu cewa zata yi tafiya. Tana yin sallama da su koda a wayane kuma ta nemi gafarar su ta kuma ce ta yafe musu, tun suna jin babu dadi game da sallamar ta ta harma suka saba bama sa jin komai game da hakan.
Shamaki wanda shima ya kashe wayoyin shi domin kar Hajiya ta kira shi ta ce ya turo mata sakin Baby tun da yaje Dubai ya kasa tafiya China domin rayuwar bata yi masa dadi, tsawon wane lokacin zai dauka yana gujewa Mahaifiyar shi, yasan yana son Baby amma ko kusa bazai hada sonta da na Hajiya ba. Yanzu gashi tun da ya zo tunanin ya gujewa Hajiyar ke damun shi. Baby sai dai kewa da tunani rabuwarsu ke samun shi. Ranar da ya cika kwana biyar a kasar, ya yanke shawara cewa ya kunna waya ya san zuwa yanzu Hajiya ta kira shi sau babu adadi. Sai dai har aka yi kwana biyu Hajiya bata kira shi ba. Tabbas Hajiya tayi fushi da shine domin da yanzu ta kira shi. Yace bari ya kira ta. Wayoyin Hajiya basa shiga. Ya kira wayar Baby ita ma bata shiga. Dan haka ya soma shiri tafiya gida domin ya gyara kuskure da ya bata.
Sakna wata yarinya ce 'yar Niger wadda suke soyayya da Shamaki, yana sonta sosai amma fa bada batun aure ba, yana ji da ita a matan da ya ke nema. Duk lokacin da zai fita zuwa wata kasa, to da ita yake fita, Ko wannan tafiyar ma da ita suke tare, sai dai tana ta yi masa korafin cewa wannan zuwan bata san meyasa ba, kamar ya fara gajiya da ita, domin tun da suka zo, babu wata shakatawa da suka fita kamar yadda suka saba, sannan bashi da labari sai na Baby da Hajiya har ta gaji da jinsa. Gashi yanzu yana maganar zasu koma.
Shamaki yana hada kaya tana tambayarsa cikin rashin jin dadi, "Wai Sweetheart mun fasa zuwa kasar China din ne? "E " ya amsa kawai ba tare da ya kalle ta ba.
Jikina ya hau bari na soma tunanin ko jirgin ne zai fadi. Nace Hajiya in jirgi ya fadi ai har ni ne baza mu rayu ba. Tayi murmushi, sannan tace ba jirgine zai fadi ba, ina son ki kwantar da hankali ki amshi duk wannan amanar da nake baki, domin zaki iya. Dan Allah kar duk wani me aiki ko wani wanda muke dangantaka da shi ya ce, wayyo yau ina ma Hajiya tana nan. " Nace to Hajiya duk da kince kar in tambaye ki, a can zaki zauna in munje?
Tace za kiji komai. Ta sakar min hannu. Na zura mata ido ina tunanin abinda Hajiya take magana kamar me wasiyya kuma gata dai lafiyar ta lau. Ko kuma dai in mun koma ne zata koma gefe ta sakar min komai? Na sauke ajiyar Allah ya sa ma haka ne zai fi sauki aka ace Duniyar ta ke maganar bari.
Haka dai muka isa Kasar wata mota ta zo ta dauke mu da kayanmu zuwa wani katafaren gida. Mun samu wasu hadimai kamar dai irin wadannan da muke gani a fina finan India. Sune suka amshi kayanmu zuwa wani daki da ke sama. Muka shiga dakin kato ne sosai gadon da kujerun duk a ciki suke. Muka yi salloli sannan muka kwanta duk da cewa garin ma yariga ya waye. Na farka naga Hajiya zaune kan kujera tana shan shayi suna tattaunawa da wani mutum Baindiye wanda nake zaton likita ne, saboda rigar likitoci dake jikin shi. Nabi mamakin yadda mutumin ke yin magana da Hausa duk da cewar Hausar bata goge ba.
.....
Yace "Hajiya ciwo ya zo matakin karshe kamar yadda muka fada miki a wancan lokacin.
Abinda Gwajin mu ya nuna shine kin shiga matakin karshe na ciwon Allah zai iya ganin dama ya barki. Sannan a ka ida bai kamata muna fada miki halin da kike ciki ba, yaranki sune ya kamata su sani ke kuma a boye miki amma kin ce a a. Banda kina da karfin hali da yanzu kin mutu saboda fargaba. " Tace Dr ni musulma ce tun daga lokacin da ku ka fada min ciwona zuwa matakin da nake kai yanzu ban taba jin cewa bazan mutu ba. Kuma fasa yin bautar Allah ba, kuma nasan cewa dole zan mutu watarana ko babu wannan ciwon. Ina da dalilaina da bana son yara na su samu labarin wannan ciwo tsawon shekaru biyar da kuka ce zan iya kaiwa na rayu, da su cikin farin ciki, in da sun sani ni da su zamu rayu cikin damuwa da tashin hankali. Nakasan ce ina boye musu, kuma ina neman mafita ba wadda zata hana mai aukuwa ta auku ba, ina neman mafita ne kawai wadda zata zama madadi a gare su. Nasan babu madadin mahaifiya tabbas, amma ana samu mai share hawaye.
Cikin jimami yake ce mata "Kin samu? " Tace Ina fatan cewa na samu. Ka ga waccan ta nuno inda nake da yatsa tare da waiwayo ta kalli Inda nake kwance, sai muka hada ido fuskarta sharkaf da hawaye ina yin wata irin ajiyar zuciya mai hade da kunshe kuka irin na tashin hankali. Da sauri Hajiya ta mike ta nufo ni.
Maman Umar ta shigo da sallama Falon shiru. Ta nufi ciki, Juma ce take hada miya yayin da Tabawa ke firar doya. Tace "Juma kina ciki?" Juma tace Sannu da zuwa Maman Umar yanzu ki ke tace? "Wallahi nice, ina Mamanmu take ban ganta a cikin ba. " Juma ta bi Maman Umar da kallo, domin bata taba jin ta kira Hajiya da Maman su ba. Maman Umar ta yi yar dariya tace "Juma mamaki ki ke ji ne?" Juma ta ce Ato ai dole inji mamaki na ga wata sabuwar Shagwaba. Ta kawaikwayi muryar Maman Umar wai Mamanmu.
Maman Umar ta yi dariya tace kin san Allah ina zaune naji kawai ina son ganin Hajiya na kira wayar ta sai naji bata shiga, shine na ca bari dai inzo." Juma ta saka dariya tace wannan karon Hajiya ta yi wa kowa bazata, nifa kawai kira na tayi tace tanason za su yi tafiya da matar Shamaki Uwargidan. Tace mudawo nan gidan har Azima, a kula da gida da kuma yara. Nace ina za suje tace kasar waje. Cikin tsananin mamaki Maman Umar ta ce, Hajiya ce kuma yau tayi tafiya ba tare da saninmu ba?"
Juma tace ina zaton Uban dakina shine kadai zai iya sanin tafiyar nan. Maman Umar tace to ina taje kuma wai harda matar Shamaki? " Juma tace ni dai bansan kasar ba, ta dai cemin kasar waje.
Maman Umar ta danno lambar Baby tana fadin ba lallai a samu Baby a waya ba saboda layinta in ba anyi masa aiki ba to fa ba zai yi amfani tana wata kasar ba.
Layin kuwa bai shiga ba. Ta kira layin Maman Nana wadda tasan ko Hajiya ta boye ma wani wata magana sai ta fadawa mata. Suka gaisa, tace "Wai kuwa Maman Nana Hajiya ta fada miki zata yi tafiya? Maman Nana tace a a gaskiya bata fada min ba, ina taje? Ban sani ba, ji nayi ina son ganinta na zo sai kuma wai ashe sun fita waje da matar Shamaki. "Wace kasa?" Maman Nana ta tambaya cikin mamaki. Maman Umar tace bansani ba nima, ga wayoyin ta duk basa shiga. Maman Nana ta yi shiru, can tace "Tofa! To kuma Shamaki ai ya sani ko? " Maman Nana ta ce Shamaki yana da masaniya ki kira lambarsa ta Dubai ko ta Chaina Nima zan kira.
Har Maman Umar ta tafi bata samu layin Shamaki ba, kuma duk su Maman Afra da Maman Iman babu wadda bata kira ba amma basu san komai game da tafiyar Hajiya ba. Gashi wayar Shamaki ta kasa samuwa.
Maman Umar ta kira su gaba daya zuwa gidan ta, tace itafa tana ji a jikinta akwai wani abu, tana zargin Shamaki ya gudune domin kar Hajiya ta sa shi ya saki Baby. " Maman Iman tace ni kuma na kula Hajiya tana son Baby, kila dai ta fita da ita ne a dubata ko zata samu haihuwa domin kusan so biyu tana yi min magana akan rashin haihuwar Baby.? "
Maman Nana tace "Hakan ma zai iya yiwuwa. " . Maman Afra tace in har batun Haihuwa ne nasan Hajiya
India zata nufa a duba mata lafiyar Baby, dan haka sai mu bincika mu gani ko can ta tafi idan canne sai mu daina daga hankalinmu.
Take Maman Umar ta kira wani a office din masu yin bizar wanda tasan shine Hajiya ke yin Hulda da shi. Ta tambaye shi ko bizar wace kasa ya yi wa Hajiya? Yace ta India ce, maman Umar ta tambaye shi tsawo lokacin da bizar zata dauka. Yace "sati biyu ne ta yi masa godiya suka yi sallama.
Daga nan suka ce bari su jira har su dawo, sai dai cikin su kowa na mamakin abinda yasa Hajiya ta ki tayi musu sallama. Domin koda Hajiya take boye musu wani abu na sirrin gidan ta, bata taba boye musu cewa zata yi tafiya. Tana yin sallama da su koda a wayane kuma ta nemi gafarar su ta kuma ce ta yafe musu, tun suna jin babu dadi game da sallamar ta ta harma suka saba bama sa jin komai game da hakan.
Shamaki wanda shima ya kashe wayoyin shi domin kar Hajiya ta kira shi ta ce ya turo mata sakin Baby tun da yaje Dubai ya kasa tafiya China domin rayuwar bata yi masa dadi, tsawon wane lokacin zai dauka yana gujewa Mahaifiyar shi, yasan yana son Baby amma ko kusa bazai hada sonta da na Hajiya ba. Yanzu gashi tun da ya zo tunanin ya gujewa Hajiyar ke damun shi. Baby sai dai kewa da tunani rabuwarsu ke samun shi. Ranar da ya cika kwana biyar a kasar, ya yanke shawara cewa ya kunna waya ya san zuwa yanzu Hajiya ta kira shi sau babu adadi. Sai dai har aka yi kwana biyu Hajiya bata kira shi ba. Tabbas Hajiya tayi fushi da shine domin da yanzu ta kira shi. Yace bari ya kira ta. Wayoyin Hajiya basa shiga. Ya kira wayar Baby ita ma bata shiga. Dan haka ya soma shiri tafiya gida domin ya gyara kuskure da ya bata.
Sakna wata yarinya ce 'yar Niger wadda suke soyayya da Shamaki, yana sonta sosai amma fa bada batun aure ba, yana ji da ita a matan da ya ke nema. Duk lokacin da zai fita zuwa wata kasa, to da ita yake fita, Ko wannan tafiyar ma da ita suke tare, sai dai tana ta yi masa korafin cewa wannan zuwan bata san meyasa ba, kamar ya fara gajiya da ita, domin tun da suka zo, babu wata shakatawa da suka fita kamar yadda suka saba, sannan bashi da labari sai na Baby da Hajiya har ta gaji da jinsa. Gashi yanzu yana maganar zasu koma.
Shamaki yana hada kaya tana tambayarsa cikin rashin jin dadi, "Wai Sweetheart mun fasa zuwa kasar China din ne? "E " ya amsa kawai ba tare da ya kalle ta ba.