Sashe 3
Gurbin Ido Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"jam" ta amsa tana juyawa da dan hanzarinta tabar wajen zuwa nasu dakin.
"Kiji tsoron Allah fulera,kiji tsoron randa Allah zai kamaki da haqqin marainiya" daga haka ya dauka ledarsa ya rab'eta ya wuce ciki,ta bishi da harara,sannan ta sauke idanunta tabi hanyar maimunatun ta wuce da hararar itama har zuwa qofar dakin nasu,sannan taja qwafa tana sakin labulen
"Tsoronka da zanji,rashin godiyar Allah ne yasa baka ganin qoqarina ai,banda ni ma waye zai riqeta?" Taci gaba da mita abinta,saidai ko daga kai bappa jauro baiyi ba bare ya kalleta,idan da sabo ya riga ya saba da halayyarta.
Saman shimfidarta ta koma ta zauna sannan ta bude ledar biredin,a hankali ta dinga yaga tana turawa,cikin ranta tana godewa Allah da ya turo bappa jauro,da haka zata kwana da tsohuwar yunwarta.
Yadda biredin ya fara mata go slow a wuya ya sanyaya bisa dole ta miqe cikin raunin da jikinta ya fara yi ta lalubi wani tsohon kofi nata ta tsiyaya ruwa a jallonsu dake dakin,ta sake komawa ta zauna,tana ci tana korawa da ruwan,kafin sannan tuni bacci yayi gaba da gaje,wadda maimunatu bata da tabbacin tayi sallar magariba bare isha'i.
Jahilci ya sanya gaje da wata ire irensu sam basu baiwa ibadarsu muhimmanci,duk da cewa akwai makarantar islamiyya guda daya tal,wadda anan ake koyarwa da kowa da kowa cikin rugar tasu,maza da mata yara da manya,cikin hobbansa da malaman ahlussunnah sukayi suka kawo musu malami bafulatani irinsu yake zaune dasu.yana koyar dasu,saidai ba kowa bane ya fahimci alfanun hakan ba bare har yace zaije,da yawa wani kallo sukewa makarantar,dai daikunsu ke zuwa.
Tana da.matuqar buri da kuma sha'awar kasancewarta daliba a makarantar,saidai inama taga lokacin da zai zama rara(saura) a gareta tsahon wuni guda,wanda bata bautar komai,da gar zatayi.amfani dashi ta ziyarci makarantar da sunan daukan karatu,kullum aiki take,babu dare ba rana,ba asabar babu lahadi,kamar yadda babu alhamis babu kuma juma'a,koda makara tar bokonsu dake da dan karen nisa,koda yuashe maimunatu mafarkin zuwanta take,bare wannan dake kurkusa dasu,gaje nada dama mai yawa da zata iya zuwa makarantar,saidai sam ita ba wannan bane a gabanta ba,bata taba ma kwatanta zuwa din ba.
Dai dai lokacin da gari ya sake daukan shuru bayan daukewar mamakon ruwan saman.....dai dai lokacin da wata iska me sanyi ke kadawa,a wannan lokacin zazzabi ya fara saukar mata,yana murqushe duk wata gaba dake da sauram qwari a jikinta,takurewa tayi sosai waje guda,tana jin yadda zazzabin ke ratsawa ta qashi da tsokar jikinta,a hankali yana saukar mata da sanyi da wani irin radadi,saita cure waje daya,numfashinta na fita da qyar tana kokawa dashi.
Duk da cewa wannan din ba baqon yanayi bane tare da ita,amma shi ciwo ba'a taba sabo dashi,ta jima cikin wannan yanayin tana kokawa da numfashinta,tana hangen kanta tsakanin rayuwa da mutuwa kafin ubangiji cikin tausayinsa rahamarsa da kuma jin qansa ta fara samun sassauci,numfashinta ya fara komawa dai dai,saidai qirjinta dake riqe da kuma ciwon dake ratsawa cikin jikinta yana sandarta a hankali,har wani wahalallen bacci yayi awon gaba da ita.
***********
"Maimunatu!.....maimunatu....." Can tsakiyar baccinta....sannan cikin tsakiyar kwanyarta taji ana ambatar sunanta,shurin da aka kaima gefan cikinta shi ya qarasa tabbatar mata da cewa ba cikin duniyar mafarki take ba,abinda ya sanyata zumbur ta miqe daga kwanciyarta,sai kuma ta sanya hannayenta guda biyu ta dafe kanta tana furta
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" saboda wani nauyi da taji kan nata yayi mata,baya ga dan karen ciwon da yake mata
"Ke yafi kamata a jawa innalillahi,akalluɗo(muguwa)" inna dake tsaye bisa kanta ta fada cikin fushi,bata ko motsa ba bare tace wani abu,kanta na qas tana jin yadda zuciyarta ke suya,jikinta ke tsami da kuma ciwo saboda ciwon dake jikinta
"Ananata haala maimunatu?(bakyajin magana maimunatu ko)da kika zo kika kwanta kina barshi,waye zai miki tatsar nonon,waye zai fita da dabbobin?,ko uwarki ce zatazo tayimin?" Idanunta ta runtse,tana jin xafi cikin zuciyarta fiye da kowanne irin zafi,koda wasa bata qaunar inna ta dinga sanyo mahaifiyarta cikin kowanne irin sha'ani ko laifi da zata aikata mata,ta kuma tabbatar ci gaba da shurunta xai bawa innar dama taci gaba da zagin nata ne,don haka cikin murya mai cike da rauni tace
"Minyauɗo inna(bani da lafiya inna)" idanu innar ta qanqance tana dubanta
"Wannan keta shafa,yahudillo durgul,wurtawa(zo ki tafi kiwo,fito)" ta fada a tsawace kamar zata finciko maimunatun.
Bata da sauran zabin da ya wuce ta miqe din kamar yadda inna fa buqata,duk kuwa da yadda takejin jikinta,ta dafa a hankali ta miqe tsaye,a sanda innar ke mata wani kallo
"Nikam kin zamemin alaqaqai masifa" saita juya ta fita zuwa waje tana zazzaga masifarta,idan lokacin ka shigo gidan zaka tsammaci wani mummunan abu maimuntun ta aikatawa innar.
Kayanta data saqale.jiya ta miqa hannu cikin juriya ta cirosu,hawaye me dumi ya subuce mata,ta zame zanin jikinta,ta fara shirya kanta a cikinsu,babu batun wanka bare akai ga abinci,dama bata lafiyarta take ba
"Wurtawa fa maimaunatu" ta tsinkayo muryar innar tana fada cikin salo na azalzala
"Mihosh shawai filkul(dan kwali zan dauko)" maimunatun ta fada tana duqawa a hankali ta dauki dan yalolon dan kwalinta ta dora kan sassalkan gashinta dake cure waje daya cikin kitson doka(bijaɗe a fulatance),sannan ta matsa zuwa bakin kofa tana laluben wuffajen ta(asalin rufaffen takalmin da fulani ke amfani dashi wajen kiwo.
Ba zata iya duqawa ta sakasu yadda ta saba ba,dole sai datakai qasa ta zauna dirshan sannan ta samu damar sanyasu ga qafafuwanta,ta miqe tana riqe da sandarta tana takowa zuwa tsakar gidan nasu iska na kadata.
Kamar kullum babu kowa a tsakar gidan,daga inna dake can rumfar da suke girki,sai gaje dake zaune tana cin tuwo,tuwon da take da tabbacin da safen akayishi,amma bata da darajar da za'a bata ta sanyawa cikinta,ko don darajar bautar da zata fita yi musu.
Ganin tuwon ya tuna mata da guntun biredinta na jiya,ta sanya hannu ta dafe qaramar jakar da take daureta a qugunta taji tudunsa tabbacin yana nan,sanna ya fara takawa zuwa ma'adanar dabbobin,muggan kalaman inna sunayi mata rakiya,har zuwa sanda ta kammala kunce na kuncewa,ta kuma fara kadasu suka dauki hanya.
❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥
*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*
*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*
*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*
😄😄😄😄😄😄😄
*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*
*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*
INAYA(riba biyu)___mamughee
SANADIN LABARINA___Rano
BABU SO___Billynabdul
FARHATUL K'ALB___Miss xoxo
GURBIN IDO____Huguma
*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*
*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*
Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300
*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank
*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902
*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107
*_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: *_GURBIN IDO_*
*Huguma*
*Free page 03*
Duk wani taku da takeyi tana yinsa ne da taimakon sandar dake riqe a hannunta,a yau madadin sandar ta zame mata ta saita dabbobin da take jan ragamarsu,sai ta zame mata mataimakiya wajen sanya diga diganta zuwa qasa.
A yau din da baki ta.dinga saitasu tana basu umarni,duk da yadda magana ke mata wuya ainun,duk kalma daya idan xata fitar sai taji kamar kanta zai tsage,sun dan dauki lokaci kafin su isa inda suke qyale dabbobin,kowacce ta ni'imtu ta kums amfana daga rahamar ubangijinmu.
Tana isa kamar koda yaushe,mabanbantan makiyaya dake wajen kowa ya fara qoqarin tattare dabbobinsa don gudun afkawa ko cakuduwa da nata dabbobin,ba yaune farau ba,nan da anjima kadan ma tana iya ganin wajen babu kowa sai ita daya da nata dabbobin,abune data saba da ganinsa,canfi ne da suka riga suka dasawa ransu,wanda batasan ranar da zai goge ba,hakanan babu me cire musu shi sai mahaliccinmu.
A yau dinma bata damu ba kamar kowanne lokaci,bayan ta tabbatar da sun iso inda ya dace,saita fara zame jikinta daga cikinsu,tana wara manya kuma fararen idanunta da kalarsu ta jirkita saboda zafin ciwo dana zazzabi,tana neman inuwar da zata dace da ita.
Babbar bishiyar mangwaro ce,mai yawam sanyi da kuma inuwa,wadda bata da wani tsaho.mai.yawa amma sai yawan 'ya'ya,daga nan inda bishiyar take basu da nisa da inda zata hangi dabbobinta,hakanan ba nisa da inda zata gangara dasu susha ruwa da zarar lokacin hakan yayi.
A hankali ta zame malafare(hular kaba da suke amfani da ita" ta ajjiye a wajen,duk da hular ba nauyi gareta ba,amma sai takejin kamar ta dora wani dutse saman kanta,ta zare jakar dake qugunta itama ta ajjiyeta,da zata iya kwanciya zatayi,amma tana jin nauyin sallar da batayi ba takai mata ko ina,don haka ta juya zuwa sashen da ruwa ke gudana,ta daura alwala ta dawo ta tada salla saman dankwalin kanta data cire ga yane kanta da mayafin da akoda yaushe bata rabo da yafashi,duk kuwa da cewa baqon abune cikin al'adarsu,zata iya cewa ma kaf fadin rugar ita daya ce cikin matasan yara masu shakaru irin nata dake amfani dashi.
"Maimunatu!.....maimunatu" da sauri ta daga kanta daga durquson da tayi masa,tana ware idanunta cikin matuqar kaduwa da razana,murya mafi muni da razanarwa a wajenta.....muryar da mamallakin muryar abubuwane da tunda take a rayuwarta bata taba jin abinda ta tsana cikin duniyarta sama dasu ba
"Yaushe ya dawo?" Ta jefawa kanta tambayar tana wurga idanunta don tantance daga wanne bangare yake dosota.
Daga can nesa ta hangeshi,tsabar kauri da qarfin muryarne ya sanya ta dinga jinta kusa da ita kamar yana gab da ya cimmata,qasa tayi sosai don kada ya hangota,sannan ta miqe a hankali,ta tattare dankwali hula da jakarta waje daya ga wurga saman bishiyar da take zaune qasanta,karo na farko da tayi ala wadai da rashin iya koyan hawa bishiya irin nata,saita saita mayafinta ta lullube jikinta da kyau,sannan ta zagaya ta bayan bishiyar ta lafe sosai a jikinta,ta yadda zata iya hangoshi,zuciyarta na wani buguwa ɗik ɗik,tana cike da fata da kuma addu'ar rashin samun sa'ar ganinta.
"Kiji tsoron Allah fulera,kiji tsoron randa Allah zai kamaki da haqqin marainiya" daga haka ya dauka ledarsa ya rab'eta ya wuce ciki,ta bishi da harara,sannan ta sauke idanunta tabi hanyar maimunatun ta wuce da hararar itama har zuwa qofar dakin nasu,sannan taja qwafa tana sakin labulen
"Tsoronka da zanji,rashin godiyar Allah ne yasa baka ganin qoqarina ai,banda ni ma waye zai riqeta?" Taci gaba da mita abinta,saidai ko daga kai bappa jauro baiyi ba bare ya kalleta,idan da sabo ya riga ya saba da halayyarta.
Saman shimfidarta ta koma ta zauna sannan ta bude ledar biredin,a hankali ta dinga yaga tana turawa,cikin ranta tana godewa Allah da ya turo bappa jauro,da haka zata kwana da tsohuwar yunwarta.
Yadda biredin ya fara mata go slow a wuya ya sanyaya bisa dole ta miqe cikin raunin da jikinta ya fara yi ta lalubi wani tsohon kofi nata ta tsiyaya ruwa a jallonsu dake dakin,ta sake komawa ta zauna,tana ci tana korawa da ruwan,kafin sannan tuni bacci yayi gaba da gaje,wadda maimunatu bata da tabbacin tayi sallar magariba bare isha'i.
Jahilci ya sanya gaje da wata ire irensu sam basu baiwa ibadarsu muhimmanci,duk da cewa akwai makarantar islamiyya guda daya tal,wadda anan ake koyarwa da kowa da kowa cikin rugar tasu,maza da mata yara da manya,cikin hobbansa da malaman ahlussunnah sukayi suka kawo musu malami bafulatani irinsu yake zaune dasu.yana koyar dasu,saidai ba kowa bane ya fahimci alfanun hakan ba bare har yace zaije,da yawa wani kallo sukewa makarantar,dai daikunsu ke zuwa.
Tana da.matuqar buri da kuma sha'awar kasancewarta daliba a makarantar,saidai inama taga lokacin da zai zama rara(saura) a gareta tsahon wuni guda,wanda bata bautar komai,da gar zatayi.amfani dashi ta ziyarci makarantar da sunan daukan karatu,kullum aiki take,babu dare ba rana,ba asabar babu lahadi,kamar yadda babu alhamis babu kuma juma'a,koda makara tar bokonsu dake da dan karen nisa,koda yuashe maimunatu mafarkin zuwanta take,bare wannan dake kurkusa dasu,gaje nada dama mai yawa da zata iya zuwa makarantar,saidai sam ita ba wannan bane a gabanta ba,bata taba ma kwatanta zuwa din ba.
Dai dai lokacin da gari ya sake daukan shuru bayan daukewar mamakon ruwan saman.....dai dai lokacin da wata iska me sanyi ke kadawa,a wannan lokacin zazzabi ya fara saukar mata,yana murqushe duk wata gaba dake da sauram qwari a jikinta,takurewa tayi sosai waje guda,tana jin yadda zazzabin ke ratsawa ta qashi da tsokar jikinta,a hankali yana saukar mata da sanyi da wani irin radadi,saita cure waje daya,numfashinta na fita da qyar tana kokawa dashi.
Duk da cewa wannan din ba baqon yanayi bane tare da ita,amma shi ciwo ba'a taba sabo dashi,ta jima cikin wannan yanayin tana kokawa da numfashinta,tana hangen kanta tsakanin rayuwa da mutuwa kafin ubangiji cikin tausayinsa rahamarsa da kuma jin qansa ta fara samun sassauci,numfashinta ya fara komawa dai dai,saidai qirjinta dake riqe da kuma ciwon dake ratsawa cikin jikinta yana sandarta a hankali,har wani wahalallen bacci yayi awon gaba da ita.
***********
"Maimunatu!.....maimunatu....." Can tsakiyar baccinta....sannan cikin tsakiyar kwanyarta taji ana ambatar sunanta,shurin da aka kaima gefan cikinta shi ya qarasa tabbatar mata da cewa ba cikin duniyar mafarki take ba,abinda ya sanyata zumbur ta miqe daga kwanciyarta,sai kuma ta sanya hannayenta guda biyu ta dafe kanta tana furta
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" saboda wani nauyi da taji kan nata yayi mata,baya ga dan karen ciwon da yake mata
"Ke yafi kamata a jawa innalillahi,akalluɗo(muguwa)" inna dake tsaye bisa kanta ta fada cikin fushi,bata ko motsa ba bare tace wani abu,kanta na qas tana jin yadda zuciyarta ke suya,jikinta ke tsami da kuma ciwo saboda ciwon dake jikinta
"Ananata haala maimunatu?(bakyajin magana maimunatu ko)da kika zo kika kwanta kina barshi,waye zai miki tatsar nonon,waye zai fita da dabbobin?,ko uwarki ce zatazo tayimin?" Idanunta ta runtse,tana jin xafi cikin zuciyarta fiye da kowanne irin zafi,koda wasa bata qaunar inna ta dinga sanyo mahaifiyarta cikin kowanne irin sha'ani ko laifi da zata aikata mata,ta kuma tabbatar ci gaba da shurunta xai bawa innar dama taci gaba da zagin nata ne,don haka cikin murya mai cike da rauni tace
"Minyauɗo inna(bani da lafiya inna)" idanu innar ta qanqance tana dubanta
"Wannan keta shafa,yahudillo durgul,wurtawa(zo ki tafi kiwo,fito)" ta fada a tsawace kamar zata finciko maimunatun.
Bata da sauran zabin da ya wuce ta miqe din kamar yadda inna fa buqata,duk kuwa da yadda takejin jikinta,ta dafa a hankali ta miqe tsaye,a sanda innar ke mata wani kallo
"Nikam kin zamemin alaqaqai masifa" saita juya ta fita zuwa waje tana zazzaga masifarta,idan lokacin ka shigo gidan zaka tsammaci wani mummunan abu maimuntun ta aikatawa innar.
Kayanta data saqale.jiya ta miqa hannu cikin juriya ta cirosu,hawaye me dumi ya subuce mata,ta zame zanin jikinta,ta fara shirya kanta a cikinsu,babu batun wanka bare akai ga abinci,dama bata lafiyarta take ba
"Wurtawa fa maimaunatu" ta tsinkayo muryar innar tana fada cikin salo na azalzala
"Mihosh shawai filkul(dan kwali zan dauko)" maimunatun ta fada tana duqawa a hankali ta dauki dan yalolon dan kwalinta ta dora kan sassalkan gashinta dake cure waje daya cikin kitson doka(bijaɗe a fulatance),sannan ta matsa zuwa bakin kofa tana laluben wuffajen ta(asalin rufaffen takalmin da fulani ke amfani dashi wajen kiwo.
Ba zata iya duqawa ta sakasu yadda ta saba ba,dole sai datakai qasa ta zauna dirshan sannan ta samu damar sanyasu ga qafafuwanta,ta miqe tana riqe da sandarta tana takowa zuwa tsakar gidan nasu iska na kadata.
Kamar kullum babu kowa a tsakar gidan,daga inna dake can rumfar da suke girki,sai gaje dake zaune tana cin tuwo,tuwon da take da tabbacin da safen akayishi,amma bata da darajar da za'a bata ta sanyawa cikinta,ko don darajar bautar da zata fita yi musu.
Ganin tuwon ya tuna mata da guntun biredinta na jiya,ta sanya hannu ta dafe qaramar jakar da take daureta a qugunta taji tudunsa tabbacin yana nan,sanna ya fara takawa zuwa ma'adanar dabbobin,muggan kalaman inna sunayi mata rakiya,har zuwa sanda ta kammala kunce na kuncewa,ta kuma fara kadasu suka dauki hanya.
❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥
*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*
*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*
*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*
😄😄😄😄😄😄😄
*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*
*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*
INAYA(riba biyu)___mamughee
SANADIN LABARINA___Rano
BABU SO___Billynabdul
FARHATUL K'ALB___Miss xoxo
GURBIN IDO____Huguma
*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*
*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*
Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300
*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank
*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902
*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107
*_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: *_GURBIN IDO_*
*Huguma*
*Free page 03*
Duk wani taku da takeyi tana yinsa ne da taimakon sandar dake riqe a hannunta,a yau madadin sandar ta zame mata ta saita dabbobin da take jan ragamarsu,sai ta zame mata mataimakiya wajen sanya diga diganta zuwa qasa.
A yau din da baki ta.dinga saitasu tana basu umarni,duk da yadda magana ke mata wuya ainun,duk kalma daya idan xata fitar sai taji kamar kanta zai tsage,sun dan dauki lokaci kafin su isa inda suke qyale dabbobin,kowacce ta ni'imtu ta kums amfana daga rahamar ubangijinmu.
Tana isa kamar koda yaushe,mabanbantan makiyaya dake wajen kowa ya fara qoqarin tattare dabbobinsa don gudun afkawa ko cakuduwa da nata dabbobin,ba yaune farau ba,nan da anjima kadan ma tana iya ganin wajen babu kowa sai ita daya da nata dabbobin,abune data saba da ganinsa,canfi ne da suka riga suka dasawa ransu,wanda batasan ranar da zai goge ba,hakanan babu me cire musu shi sai mahaliccinmu.
A yau dinma bata damu ba kamar kowanne lokaci,bayan ta tabbatar da sun iso inda ya dace,saita fara zame jikinta daga cikinsu,tana wara manya kuma fararen idanunta da kalarsu ta jirkita saboda zafin ciwo dana zazzabi,tana neman inuwar da zata dace da ita.
Babbar bishiyar mangwaro ce,mai yawam sanyi da kuma inuwa,wadda bata da wani tsaho.mai.yawa amma sai yawan 'ya'ya,daga nan inda bishiyar take basu da nisa da inda zata hangi dabbobinta,hakanan ba nisa da inda zata gangara dasu susha ruwa da zarar lokacin hakan yayi.
A hankali ta zame malafare(hular kaba da suke amfani da ita" ta ajjiye a wajen,duk da hular ba nauyi gareta ba,amma sai takejin kamar ta dora wani dutse saman kanta,ta zare jakar dake qugunta itama ta ajjiyeta,da zata iya kwanciya zatayi,amma tana jin nauyin sallar da batayi ba takai mata ko ina,don haka ta juya zuwa sashen da ruwa ke gudana,ta daura alwala ta dawo ta tada salla saman dankwalin kanta data cire ga yane kanta da mayafin da akoda yaushe bata rabo da yafashi,duk kuwa da cewa baqon abune cikin al'adarsu,zata iya cewa ma kaf fadin rugar ita daya ce cikin matasan yara masu shakaru irin nata dake amfani dashi.
"Maimunatu!.....maimunatu" da sauri ta daga kanta daga durquson da tayi masa,tana ware idanunta cikin matuqar kaduwa da razana,murya mafi muni da razanarwa a wajenta.....muryar da mamallakin muryar abubuwane da tunda take a rayuwarta bata taba jin abinda ta tsana cikin duniyarta sama dasu ba
"Yaushe ya dawo?" Ta jefawa kanta tambayar tana wurga idanunta don tantance daga wanne bangare yake dosota.
Daga can nesa ta hangeshi,tsabar kauri da qarfin muryarne ya sanya ta dinga jinta kusa da ita kamar yana gab da ya cimmata,qasa tayi sosai don kada ya hangota,sannan ta miqe a hankali,ta tattare dankwali hula da jakarta waje daya ga wurga saman bishiyar da take zaune qasanta,karo na farko da tayi ala wadai da rashin iya koyan hawa bishiya irin nata,saita saita mayafinta ta lullube jikinta da kyau,sannan ta zagaya ta bayan bishiyar ta lafe sosai a jikinta,ta yadda zata iya hangoshi,zuciyarta na wani buguwa ɗik ɗik,tana cike da fata da kuma addu'ar rashin samun sa'ar ganinta.