Sashe 108
Gurbin Ido Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Anni ammi anty maama,hajja su laila gaba dayansu harda matan kawun nan maimunatu guda hudu,a hannuwan laila da salma fararen shawula ne dake dauke da wasu kyawawan baby boys a ciki,wadanda dukka wanda ya kallesu bazaya so dauke idanuwansa daga kansu ba,wani irin kyau suka dauko daga uwa da uba suka cakude,duka duka basu haura awa guda da zuwansu duniya ba,saidai soyayyar dake kewaye dasu mai tarin yawa ce.
A hankali qofar toilet din ta bude, maimunatu ce tare da umma sa'adah,gefe kuma afrah ce,suna riqe da ita a hannu tana takawa a hankali,sai kuma duka hankula sukayi kansu,kowa yana zabga mata sannu
"Anya maimunatu ba zaki bar kukan nan haka ba?,ko babies dinne bakiso?" Hajja ta fada tana kama baki,dubanta umma sa'adah tayi
"Daadarta take tunawa,wai dama haka tasha wahala ta haifeta?,ta sake shan wahala.bata haifa abinda ke cikinta ba ta rasu?" Kowa saida jikinsa yayi sanyi,suka fara bata baki cikin nuna kulawa.
A mugun sukwane motocin guda biyu suka dira farfajiyar asibitin,motar farko bata ko kai ga kammala tsaiwa ba aka bude murfinta aka sauko da wani irin kuzari hanzari da kuma sassarfa.
Captain ja'afar ne,sanye da wani farin kaftan da aka qawata shi da dimki na musamman,tamkar yana da masaniyar yau din rana ce ta musamman a rayuwarsa,biye dashi kuwa manyan ma'aikatansa ne,don ya baro company ne babu shiri.
Dukka baya suka rufa masa,jabir ya qara hanzari ya cimmasa
"Relax mana captain,ance lafiya qalau fa ta sauka"
"I know dude,na qagu na ganta ne" ya fada yana sake qara hanzarinsa harda sassarfa.
Daga baya dukka suka tsaya,banda jabir da yaci gaba da binsa har suka isa bakin qofar, ja'afar dinne a gaba,don haka yana bude qofar hankalin kowa yayi kanshi,yayin da shi kuma idanunsa gaba daya suke kan maimunatunshi dake zaune saman gado,umma sa'adah na qoqarin bata tea tasha ko za'a samu ruwan nono ya samu,don yaran sun fara qananun rigingimu.
Suna hada idanu sabbin qwalla suka cika mata idanu,abubuwa ne mabanbanta cikin zuciyarta,farinciki takeji mara misaltuwa da a yau ta bawa ja'afar din muradin ransa wato 'ya'ya,tunda cikinta ya girma baya cikakken bacci,don ta fishi samun barci me kyau ma,kullum cikin addu'a yake ba dare ba rana,hidima yake mata da jikinsa da aljihunsa,ya qwallafa rai matuqa akan cikin,har ta dinga jin anya ba mutuwa zasuyi ita da yaran ba?,anya itama ba wucewa zatayi yadda daadarta ta rasu ba?,sai gashi komai yazo ya wuce kamar ba'ayi ba.
Abu na biyu zallar shagwaba ne da kuma tuna irin wahalar data sha,yazo yanzu zaa sauke masa nasa rabon da bai samu ba a dazun d tana labor.
Dukka gaidashi suke,yayin da manyan ke masa barka,yana amsa musu amma hankalinsa ya karkata gaba daya a kanta,miqewa sukayi suka fara basu waje,afra da laila suka isa gefan gadon suka ajjiye yaran suma sukabi bayansu.
Shuru dakin ya dauka bayan ficewarsu, hannayensa saye a aljihun rigarsa yana qare musu kallo daga nesa,yana jin komai tamkar a mafarki,idan ya kalleta sai ya maida dubansa ga yaran,duk da baya iya ganin fuskarsu sosai
"Angel" ya kirayi sunanta a tausashe,yana jin wata sabuwar soyayyarta tana ratsa qashi bargo da kuma jijiyar jikinsa,kasa daga kai tayi ta kalleshi,sai ya haqura da kiran saboda yadda yakeji kamar ana fusgarshi zuwa gareta ya soma takawa a hankali,har ya isa bakin gadon,jikinta na gogar gwiwoyinta data zubo qafafunta qasa ta jingina da bangon.
Hannayensa ya sanya ya daga fuskarta da kyau yana kallonta,sai itama ta zube masa idanuwanta da sukayi wani tarwai, tausayinta ya kamashi,yaso ace dukka gwagwarmayar naqudar data sha yana tare da ita,sai gashi ya qunsa mata ciki ya barta da wahala ita kadai
[11/25, 12:59 PM] Safiyyatulkiram: 83
Murmushin nasara likitan ya saki,yau da alama ranar sa'arsa ce
"Babu damuwa hajiya,zamu baki daki ki kwanciyarki kita baccinki,basai kin koma gida ba bare ki gayawa kowa,ana gama diba zaasa miki kudinki a jaka a baki ki tafi dashi a sirrance saboda gudun barayi da 'yan sane,aidai kinsan miliyan talatin ba qananun kudi bane ko?" Kai ta jinjina
"Qwarai kuwa likkita,ai sai na samo.masu tayin irga inajin"
"Yauwa to" hankalinta kwance aka bata daki lafiyayye tayi kwanciyarta tana sheqa baccin,tasan gidanta babu kowa sai laulo,gaje kuwa batace ga inda taje ba,jauro kuwa tuni ya sawwaqe mata dama saki guda,saboda yadda tayi silar yawace yawacen gajee,gashi taqi saituwa,hidimar aurensa yake kawai yana fatan zuwan sabuwar amaryarsa ta daidata gidan da yaran,don yasanta tsayayya ce sosai akan tarbiyya.
Daga wannan baccin dai inna furera sai tashi tayi ta tsinci kanta ajeji cikin matsanancin ciwo,da qyar cikin masu wucewa cikin dare suka ganota suka daukota zuwa cikin gari,ciwo yayi ciwo har 'yan uwanta daga gembu sukazo,qarshe aka.kaita babban asibiti.
Sakamakon bincike ya nuna qodarta guda daya aka cire,dayar kuma ba cikakkiyar lafiya ne da ita ba,haka taci gaba da rayuwa cikin ciwo,idan ka kallo cikinta kamar zai fashe.
Duka wannan labarin sai da yuuma tazo take gayawa umma sa'adah,yuman tace
"Azabar cin dukiyar marainiyar nan kadai bazai barta ba,hala wutar data ciwa cikinta na dukiyar maraya Allah ya fara azabtar da ita tun gidan duniya"
"Haka Allah yake lamarinsa,shi hakki ai yanzu tun a duniya Allah yake sakayyarsa basai anje kiyama ba" umma sa'ada tana fada,sosai maimunatu taji tausayinsu daga ita har gajee,amma data fara maganar ma umma sa'adah cewa tayi
"Akul na sake jin maganar wadan nan mutanen daga bakinki,ki fuskanci rayuwarki,banda Allah ya qwaceki da tuni har yanzu kina hannunta,baasan ma a wanne hali zaki kasance ba".
°°°°°°°°°°A hankali ta soma bude idanunta,tana jin yadda yake shafar gefan fuskarta a hankali cikin taushi,kafin ta gama.bude idanuwan nata murmushi ya mamaye fuskarta,ta san mutum daya ne ke da wannan aikin,wanda salon tashin da zai mata daga bacci ya banbanta dana kowa.
Tarrr ta bude idanuwanta akan fuskar sa dake faman kallonta kamar zai cinyeta
"Yaushe ka shigo?" Sai daya langabar dakai gefe sannan ya amsa
"Kina can duniyar baccin,baby na ya daukemin ke,na zama abun tausayi,baccin nan ya fara yawa angel" ya fada yana sake shafar fuskarta data yi masa kyau sosai,a tausashe ta riqe hannunsa,a yanzun burinta shine ta samu lafiya ta shiga hidimta masa,tana tuna dramer dinsu da anni shekaran jiya da tayi maganar wai ya maidata makaranta,baima iya amsawa annin ba
"Ke maimunatu namiji baida tabbas,idan kika zauna zakiga zaunau,ya maidaki makarnatar daya zaba miki ki qarasa karatunki,koba komai kin tsira da kwalinki" anni ta fada saidai can qasan ranta bata nufin abinda ta fada din
"ki qyaleshi don Allah anni,na haqura da makarantar Allah" baki ta kama kamar gaske ta zabga salati
"Iyeee,ja'afaru?,yaushe ka iskantamin 'ya?"
"Yo ai gaskiya ce,banda abinki hajiya anni,ta yaya matar aure da ciki ruqu qui ruqu qui zata wani dinga tafiya boko?,ta zauna tayi bautar aure shine gaba"
"To ai shikenan,duk qoqarin da nake kun watsan qasa a ido?,ya maisheki mara ta ido ko?" Anni ta fada tana tafa hannu,sai a sannan kunya ta kama maimunatu,ta miqe da sauri tana boye dariya tana ficewa a dakin
"Bi a hankali!" Suka hada baki wajen fada kowa yana zabura saboda yadda ta kusan yin tuntube wajen fitar.
Ashe ja'afar din na labe yana jiranta,tana qarasa fitowa kuwa ya dauketa cak yana dariya
"Well done,yau kin biyani,gwara da anni yau tayi ta kanta" dariya maimunatu ta shiga qyalqyalawa
"Wato yau itace tayi ta kanta din kenan?,to babu ruwana"
"Da gaske nake data sake tada maganar zan fito mata kaina tsaye,ko kuma na daukeki mu bace cikin duniya,kinga babu me takuramu" rungumeshi tayi tana dariya
"Ba inda zamu,zamu rayu cikin aminci da yardar Allah cikin ahalinmu".
"Me kike tunani?"ya fada yana shafar gashinta, murmushi ta sake
"Anni"
"The great rigimammiyar kaka" dariya maimunatu ta sake
"Maza ta jika" hannu ya bata yana murmushi
"Taso muje,abbi ne yazo dubaki" ido ta fidda
"Abbi kuma?,ta yaya zan iya kallonsa don Allah hubby"
"Am here for you,ba komai,ai shima.uba ne" tanata doddojewa da jin kunyar abbin haka ya rakata ta kuskure bakinta ya zura mata hijab suka fito.
Cikin kunya ta sulale gabansa tana gaidashi,mutum ne mai cikakken sanin addini dana zamani,don haka bashi da wata damuwa,ya amsa mata a sake yana tambayar jikin nata,daga bisani ta fita ta basu waje shida ja'afar din
"Tunda kacemin zaka samu lokaci banji kace komai ba,ni na samar maka lokacin,na shaidama minister zuwanka,yau basai gobe ba kaje ku sasanta ka dawo da ita,itama ta zauna a dakinta kamar 'yar uwarta" kansa a qasa,gaba daya abbi ya yanke masa hanzarinsa,to amma bazai iya musa masa ba,ya amsa masa da to,yana mamakin dattako irin na abbin,bayan duka tarin aibun daya gani a kanta amma bai bashi qofar rabuwa da ita ba.
Sanda ya koma dakin bayan ya raka abbi ya wuce yayi qoqarin danne dukka damuwarsa don kada hankalin maimunatu ya tashi,saidai wayam ya rasata a dakin,ya dinga lalubenta bai sameta a ko ina ba sai a kitchen, tayi zaune tana lodar abinci baba tabawa tana qara mata,sai yayi tsaye rungume da hannuwansa yana kallonta yana murmushi,baba tabawan ce ta fara ganinsa,sai tayi murmushi
"Sannu da zuwa manya,qaraso ciki mana"
"Baba ke kike sake shagwaba diyar nan taki, abincin nan da take ci dole ta qara nauyi" murmushi tayi
"Ba dole ba,ai haka mukeso,alamun samun lafiya kenan"
"Gaskiya ne" ya amsa yana sakin qaramin murmushi yana takowa zuwa inda take zaunen,baba tabawa kuma ta ajjiye serving spoon din hannunta tana bar musu kitchen din,don yanzu haka take musu.
Yadda take taunar abinda ke cikin plate din ya burgeshi,saboda yadda dan qaramin bakinta yake juyawa,tsigar jikinsa ta zuba,ya matsa kadan sannan a hankali ya riqe fuskarta ya hade bakinsu waje daya.
Sai daya tsotse dukka labban nata da sauran maiqon dake kai,tuni plate din hannunta ya yafi yayi nasa waje,abinda yake ciki ya watse,dauke kansa yayi a hankali yana maida numfashi,shi da ita suna kallon farantin dake watse a qasa,tabe baki tayi kamar zata saki kuka tana duban yadda dan waken yayi d'ai d'ai,dubansa ya maida kanta
"Meye wannan?"
"Dan wake nane fa?,kaga abinda kayimin" ta fadi a mugun narke,da alama qiris take jira ta saki kuka,murmushi ya saki yana dan take yatsunta da nashi
"Yanzu tsakani da Allah ni na zubar miki?,ba ke kika zubar da kayanki ba?, mene abun dadi a nan ma fulawa ne ko da menen?,kaman bama" baisan hakan daya fada tunzurata yayi ba,kawai saita sake masa kuka
A hankali qofar toilet din ta bude, maimunatu ce tare da umma sa'adah,gefe kuma afrah ce,suna riqe da ita a hannu tana takawa a hankali,sai kuma duka hankula sukayi kansu,kowa yana zabga mata sannu
"Anya maimunatu ba zaki bar kukan nan haka ba?,ko babies dinne bakiso?" Hajja ta fada tana kama baki,dubanta umma sa'adah tayi
"Daadarta take tunawa,wai dama haka tasha wahala ta haifeta?,ta sake shan wahala.bata haifa abinda ke cikinta ba ta rasu?" Kowa saida jikinsa yayi sanyi,suka fara bata baki cikin nuna kulawa.
A mugun sukwane motocin guda biyu suka dira farfajiyar asibitin,motar farko bata ko kai ga kammala tsaiwa ba aka bude murfinta aka sauko da wani irin kuzari hanzari da kuma sassarfa.
Captain ja'afar ne,sanye da wani farin kaftan da aka qawata shi da dimki na musamman,tamkar yana da masaniyar yau din rana ce ta musamman a rayuwarsa,biye dashi kuwa manyan ma'aikatansa ne,don ya baro company ne babu shiri.
Dukka baya suka rufa masa,jabir ya qara hanzari ya cimmasa
"Relax mana captain,ance lafiya qalau fa ta sauka"
"I know dude,na qagu na ganta ne" ya fada yana sake qara hanzarinsa harda sassarfa.
Daga baya dukka suka tsaya,banda jabir da yaci gaba da binsa har suka isa bakin qofar, ja'afar dinne a gaba,don haka yana bude qofar hankalin kowa yayi kanshi,yayin da shi kuma idanunsa gaba daya suke kan maimunatunshi dake zaune saman gado,umma sa'adah na qoqarin bata tea tasha ko za'a samu ruwan nono ya samu,don yaran sun fara qananun rigingimu.
Suna hada idanu sabbin qwalla suka cika mata idanu,abubuwa ne mabanbanta cikin zuciyarta,farinciki takeji mara misaltuwa da a yau ta bawa ja'afar din muradin ransa wato 'ya'ya,tunda cikinta ya girma baya cikakken bacci,don ta fishi samun barci me kyau ma,kullum cikin addu'a yake ba dare ba rana,hidima yake mata da jikinsa da aljihunsa,ya qwallafa rai matuqa akan cikin,har ta dinga jin anya ba mutuwa zasuyi ita da yaran ba?,anya itama ba wucewa zatayi yadda daadarta ta rasu ba?,sai gashi komai yazo ya wuce kamar ba'ayi ba.
Abu na biyu zallar shagwaba ne da kuma tuna irin wahalar data sha,yazo yanzu zaa sauke masa nasa rabon da bai samu ba a dazun d tana labor.
Dukka gaidashi suke,yayin da manyan ke masa barka,yana amsa musu amma hankalinsa ya karkata gaba daya a kanta,miqewa sukayi suka fara basu waje,afra da laila suka isa gefan gadon suka ajjiye yaran suma sukabi bayansu.
Shuru dakin ya dauka bayan ficewarsu, hannayensa saye a aljihun rigarsa yana qare musu kallo daga nesa,yana jin komai tamkar a mafarki,idan ya kalleta sai ya maida dubansa ga yaran,duk da baya iya ganin fuskarsu sosai
"Angel" ya kirayi sunanta a tausashe,yana jin wata sabuwar soyayyarta tana ratsa qashi bargo da kuma jijiyar jikinsa,kasa daga kai tayi ta kalleshi,sai ya haqura da kiran saboda yadda yakeji kamar ana fusgarshi zuwa gareta ya soma takawa a hankali,har ya isa bakin gadon,jikinta na gogar gwiwoyinta data zubo qafafunta qasa ta jingina da bangon.
Hannayensa ya sanya ya daga fuskarta da kyau yana kallonta,sai itama ta zube masa idanuwanta da sukayi wani tarwai, tausayinta ya kamashi,yaso ace dukka gwagwarmayar naqudar data sha yana tare da ita,sai gashi ya qunsa mata ciki ya barta da wahala ita kadai
[11/25, 12:59 PM] Safiyyatulkiram: 83
Murmushin nasara likitan ya saki,yau da alama ranar sa'arsa ce
"Babu damuwa hajiya,zamu baki daki ki kwanciyarki kita baccinki,basai kin koma gida ba bare ki gayawa kowa,ana gama diba zaasa miki kudinki a jaka a baki ki tafi dashi a sirrance saboda gudun barayi da 'yan sane,aidai kinsan miliyan talatin ba qananun kudi bane ko?" Kai ta jinjina
"Qwarai kuwa likkita,ai sai na samo.masu tayin irga inajin"
"Yauwa to" hankalinta kwance aka bata daki lafiyayye tayi kwanciyarta tana sheqa baccin,tasan gidanta babu kowa sai laulo,gaje kuwa batace ga inda taje ba,jauro kuwa tuni ya sawwaqe mata dama saki guda,saboda yadda tayi silar yawace yawacen gajee,gashi taqi saituwa,hidimar aurensa yake kawai yana fatan zuwan sabuwar amaryarsa ta daidata gidan da yaran,don yasanta tsayayya ce sosai akan tarbiyya.
Daga wannan baccin dai inna furera sai tashi tayi ta tsinci kanta ajeji cikin matsanancin ciwo,da qyar cikin masu wucewa cikin dare suka ganota suka daukota zuwa cikin gari,ciwo yayi ciwo har 'yan uwanta daga gembu sukazo,qarshe aka.kaita babban asibiti.
Sakamakon bincike ya nuna qodarta guda daya aka cire,dayar kuma ba cikakkiyar lafiya ne da ita ba,haka taci gaba da rayuwa cikin ciwo,idan ka kallo cikinta kamar zai fashe.
Duka wannan labarin sai da yuuma tazo take gayawa umma sa'adah,yuman tace
"Azabar cin dukiyar marainiyar nan kadai bazai barta ba,hala wutar data ciwa cikinta na dukiyar maraya Allah ya fara azabtar da ita tun gidan duniya"
"Haka Allah yake lamarinsa,shi hakki ai yanzu tun a duniya Allah yake sakayyarsa basai anje kiyama ba" umma sa'ada tana fada,sosai maimunatu taji tausayinsu daga ita har gajee,amma data fara maganar ma umma sa'adah cewa tayi
"Akul na sake jin maganar wadan nan mutanen daga bakinki,ki fuskanci rayuwarki,banda Allah ya qwaceki da tuni har yanzu kina hannunta,baasan ma a wanne hali zaki kasance ba".
°°°°°°°°°°A hankali ta soma bude idanunta,tana jin yadda yake shafar gefan fuskarta a hankali cikin taushi,kafin ta gama.bude idanuwan nata murmushi ya mamaye fuskarta,ta san mutum daya ne ke da wannan aikin,wanda salon tashin da zai mata daga bacci ya banbanta dana kowa.
Tarrr ta bude idanuwanta akan fuskar sa dake faman kallonta kamar zai cinyeta
"Yaushe ka shigo?" Sai daya langabar dakai gefe sannan ya amsa
"Kina can duniyar baccin,baby na ya daukemin ke,na zama abun tausayi,baccin nan ya fara yawa angel" ya fada yana sake shafar fuskarta data yi masa kyau sosai,a tausashe ta riqe hannunsa,a yanzun burinta shine ta samu lafiya ta shiga hidimta masa,tana tuna dramer dinsu da anni shekaran jiya da tayi maganar wai ya maidata makaranta,baima iya amsawa annin ba
"Ke maimunatu namiji baida tabbas,idan kika zauna zakiga zaunau,ya maidaki makarnatar daya zaba miki ki qarasa karatunki,koba komai kin tsira da kwalinki" anni ta fada saidai can qasan ranta bata nufin abinda ta fada din
"ki qyaleshi don Allah anni,na haqura da makarantar Allah" baki ta kama kamar gaske ta zabga salati
"Iyeee,ja'afaru?,yaushe ka iskantamin 'ya?"
"Yo ai gaskiya ce,banda abinki hajiya anni,ta yaya matar aure da ciki ruqu qui ruqu qui zata wani dinga tafiya boko?,ta zauna tayi bautar aure shine gaba"
"To ai shikenan,duk qoqarin da nake kun watsan qasa a ido?,ya maisheki mara ta ido ko?" Anni ta fada tana tafa hannu,sai a sannan kunya ta kama maimunatu,ta miqe da sauri tana boye dariya tana ficewa a dakin
"Bi a hankali!" Suka hada baki wajen fada kowa yana zabura saboda yadda ta kusan yin tuntube wajen fitar.
Ashe ja'afar din na labe yana jiranta,tana qarasa fitowa kuwa ya dauketa cak yana dariya
"Well done,yau kin biyani,gwara da anni yau tayi ta kanta" dariya maimunatu ta shiga qyalqyalawa
"Wato yau itace tayi ta kanta din kenan?,to babu ruwana"
"Da gaske nake data sake tada maganar zan fito mata kaina tsaye,ko kuma na daukeki mu bace cikin duniya,kinga babu me takuramu" rungumeshi tayi tana dariya
"Ba inda zamu,zamu rayu cikin aminci da yardar Allah cikin ahalinmu".
"Me kike tunani?"ya fada yana shafar gashinta, murmushi ta sake
"Anni"
"The great rigimammiyar kaka" dariya maimunatu ta sake
"Maza ta jika" hannu ya bata yana murmushi
"Taso muje,abbi ne yazo dubaki" ido ta fidda
"Abbi kuma?,ta yaya zan iya kallonsa don Allah hubby"
"Am here for you,ba komai,ai shima.uba ne" tanata doddojewa da jin kunyar abbin haka ya rakata ta kuskure bakinta ya zura mata hijab suka fito.
Cikin kunya ta sulale gabansa tana gaidashi,mutum ne mai cikakken sanin addini dana zamani,don haka bashi da wata damuwa,ya amsa mata a sake yana tambayar jikin nata,daga bisani ta fita ta basu waje shida ja'afar din
"Tunda kacemin zaka samu lokaci banji kace komai ba,ni na samar maka lokacin,na shaidama minister zuwanka,yau basai gobe ba kaje ku sasanta ka dawo da ita,itama ta zauna a dakinta kamar 'yar uwarta" kansa a qasa,gaba daya abbi ya yanke masa hanzarinsa,to amma bazai iya musa masa ba,ya amsa masa da to,yana mamakin dattako irin na abbin,bayan duka tarin aibun daya gani a kanta amma bai bashi qofar rabuwa da ita ba.
Sanda ya koma dakin bayan ya raka abbi ya wuce yayi qoqarin danne dukka damuwarsa don kada hankalin maimunatu ya tashi,saidai wayam ya rasata a dakin,ya dinga lalubenta bai sameta a ko ina ba sai a kitchen, tayi zaune tana lodar abinci baba tabawa tana qara mata,sai yayi tsaye rungume da hannuwansa yana kallonta yana murmushi,baba tabawan ce ta fara ganinsa,sai tayi murmushi
"Sannu da zuwa manya,qaraso ciki mana"
"Baba ke kike sake shagwaba diyar nan taki, abincin nan da take ci dole ta qara nauyi" murmushi tayi
"Ba dole ba,ai haka mukeso,alamun samun lafiya kenan"
"Gaskiya ne" ya amsa yana sakin qaramin murmushi yana takowa zuwa inda take zaunen,baba tabawa kuma ta ajjiye serving spoon din hannunta tana bar musu kitchen din,don yanzu haka take musu.
Yadda take taunar abinda ke cikin plate din ya burgeshi,saboda yadda dan qaramin bakinta yake juyawa,tsigar jikinsa ta zuba,ya matsa kadan sannan a hankali ya riqe fuskarta ya hade bakinsu waje daya.
Sai daya tsotse dukka labban nata da sauran maiqon dake kai,tuni plate din hannunta ya yafi yayi nasa waje,abinda yake ciki ya watse,dauke kansa yayi a hankali yana maida numfashi,shi da ita suna kallon farantin dake watse a qasa,tabe baki tayi kamar zata saki kuka tana duban yadda dan waken yayi d'ai d'ai,dubansa ya maida kanta
"Meye wannan?"
"Dan wake nane fa?,kaga abinda kayimin" ta fadi a mugun narke,da alama qiris take jira ta saki kuka,murmushi ya saki yana dan take yatsunta da nashi
"Yanzu tsakani da Allah ni na zubar miki?,ba ke kika zubar da kayanki ba?, mene abun dadi a nan ma fulawa ne ko da menen?,kaman bama" baisan hakan daya fada tunzurata yayi ba,kawai saita sake masa kuka